check your best novels here

Sunday 26 February 2017

NAWAFF!!! 23 to 26

[17/12/2016 14:56] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆







NA BILKISA IBRAHIM




page 23 & 24

......WASHE GARI...su papa sukazo shida 'kaninsa dayazo daga katsina, dakuma Abban mas'ud, bayan angama gaishe2 suka shiga tattauna abinda yakawosu.
   An 'kar'kare magana za'ayi shagalin biki nanda sati hud'u masu zuwa, (1monch )sananan su Nawaf sun gama wasan kofin africa kenan, kafin yakoma Spain sai asha shagalin biki kawai.
   kai zamu shabiki, kowaya yashirya masu karatu.
    Bayan an 'kar'kare magana yasmeen tashigo ta gaidasu, 'kanin papa ya yaba kam da tarbiyyar yasmeen , yanada tabbacin Nawaf yayi dace!!!!!!!.

-------------------------------------
   Yau dai gaba d'aya family d'in suna falon papa, Nawaf yana kwance a kujera mai zaman mutum biyu, Anwar yana saitin kansa ri'ke da littafin larabci, Nawaf yana koya masa, Abdallah kam hankalinsa yana kan tv dan shi dama d'an a hutane.
   Papa da momcy suna gefe zaune papa yana nazarin wasu manya2 littatafai shida momcy, da alama bincike yakeyi akan wata shari'ar, momcy tana tayashi, tunda itama mai ilimince.
   Nawaf ya ce, "Abdallah tashi kakawo mini lifton.
   Abdallah yad'an turo baki gaba, yaya dan ALLAH bari ad'an wuce nan.
   Harararsa Nawaf yayi, ya ce, "to uncle Abdallah bari najiraka, da sauri Abdallah yatashi dan yasan gatse yay masa, yana kuskurewa saiyasha mari abanza, dan Nawaf akwai saurin hawa kamar filawa lol.
   Momcy ta ce, "ya ALLAH kashirya mini Abdallah.
   Sukace amin.
Papa ya ce, "aii Abdallah shike bama kowa ciwon kai agidannan.
  Abdallah yashigo d'auke da butar shayi mai 'kalli da 'karamin kofi da cokali, agaban Nawaf ya dire batare da yayai maganaba.
   Girgiza kai kawai Nawaf yayi yad'auka yazuba yana sha, ya ce, "yaro nafika zafin kai.
   Papa ya ce, "yau modebbo yaushane zaka koma abuja??.
   Papa gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma.
   Okey ALLAH yakaimu, aii momcy tamaka bayani akan tarewar matarka ko??, Nawaf yad'an rage fara'a, eh tagayamin, amma papa dan ALLAH abari saina koma Spain idan mun gama (KAKAR WASANNI), nadawo tunda muna samun hutu awanan lokacin saita tare!!.
   Kagafa ko inda za'a ajiyeta babu, amma zuwa sanan an kammala ginina!!. 
   Agidan Nawaf yake gini tacan baya, saboda papa yanada burin zama da iyalin guru ďaya yasa yasayi filin dake haďe da nasa yazagayeshi kowa ya girma cikin 'ya'yan saiya gina 6angarensa.
   Toshi Nawaf yaďan fara ginin ya watsar, gashi koma aure yaro yanzu. 
   Girgiza kai papa yayi, ban yardaba Modebbo, kafin katafi za'ta tare, 6angarenka za'a gyara muku yanzu saiku fara zama anan, anjima ka cire dukkan abinda kakeso daga 6angarenka kadawo dasu ďakin kusada nawa, dan za'a gyara 6angarenka asake komai naciki insha ALLAH.
     idan kazo wanan hutun saika tafi da matarka kawai, munriga mun gama yanke magana, yanzu hakama 'yan katsina sunsan komai, kuma yau dasafe nakira 'yan saudia na sanar musu, nextweek ma (MAHER da ZAID) zasuzo, 'kannanen momcy ne.
   Shiru Nawaf yayi dan zucuyarsa sai tafarfasa take, yanzu sai kawai abokansa suzo suga wanan 'yar yarinyar ya aura, gata mara kunya, kuma 6angarensa bedroom ďayane, kenan papa yana nufin a bedroom ďaya zasu zauna kenan???......
    Momcy ta katse masa tunani da fad'in yakamata ka sanar da abokanka, tunda yazu zamanine mai sau'ki komai zaka iya yi ta hanyar SOCIAL MEDIA.
   Nawaf ya ce, "to momcy zanyi 'ko'kari nida mas'ud, amma sainake ganin abun kamar babu shiri??.
   Miye rashin shiri anan modebbo, acikin wata d'aya mu zamu shirya komai, shiyyasa na ce, "su maher suzo!.
    Su Alhaji buba ba muta nen kirki bane, zasu iya aikata duk abinda tu naninsu yabasu.
  Momcy ta ce, "gsky ne Alhaji.
    Su Anwar suka shiga tsallen murna, za'ayi biki agidansu, shi dama Anwar bai ta6a ganin anyi taro agindansuba tunda shine auta, gara Abdallah yaga taron sunan Anwar d'in.

_________________________
    Ita madai yasmeen wanan labarin ya iso mata, saidai suna hanya d'aya da ango itama batayi murnaba, saima kuka data zauna tanayi, umma ta ce, "hawayen gareki dayawa yarinya, ke komai akayi sai kuka saikace hanyar ruwa, haka zakije gidan mijin dayayi miki abu ki hau kuka??, AĹLAH yabaki sa'a.
   Abba shidai lallashinta yakeyi, yayinda yaseer keta kwasar dariya danshi farinciki fal cikinsa.
    Da yamma Nawaf da mas'ud sukazo, fuskar ango da amarya babu walwala, bayan ta gaishesu mas'ud kawai ya amsa mata, ya ce, "Amarya ina 'kyauta ta??.
   Yasmeen tayi d'an murmushi, ta ce, "bari nakira maka ita, tana son tashi tana tsoron Nawaf ita kuma bazata tambayeshiba wlhy, kamar daga sama sai sukaji sallamar Ameena, yasmeen ta ce, " 'yar halak.
   Ameena ta zauna tana faďin to miya faru??.
   Tunda tashigo mas'ud ya yaba, kuma insha ALLAH yasamu matar aure kenan, Ameena ta gaishesu, amamakin yasmeen saitaga Nawaf ya amsa harda murmushi, ya ce, "Ameena zaki auri tuzurin abokina kuwa???.
   Harararsa mas'ud yayi ya ce, "kai malam waye tuzurun???.
    Cikin dariya Nawaf ya ce, "kai mana, aii itama tasan kai tuzurune 27years babu aure fa.
   Mas'ud ya ce, "ashe kaima tuzurinne??, yasmeen kinji tuzuru kika aura!!. 
    Haka sukayita tsokanar juna, kuma anan aka kulla 'kya'ky'kyawar ala'ka tsakanin amina da mas'ud.
   Ficewa sukayi suka bar Nawaf da yasmeen a falon, suma suka tafi domin yin tasu hirar.
   Nawaf ya mirtike fuska, ya ce, "k kice su papa su tsaida maganar bikinnan dasuke shirin yi!!.
   Yasmeen ta yaysine fuska, "kai miya hanaka ka fad'a musu naga kaine Namiji.
   Harara Nawaf ya sakar mata, sai akace miki ni mara kunya ne irinki!!!.
   Baki yasmeen ta ta6e tace ashe....
    Yay saurin cewa ashe mi???.
 ta murguďa baki tana faďin sainaji zafin ma'kara.
   twoow tsaki Nawaf yayi yana fad'in yarinya ki ajiye rashin kunyarki a gefe dan wlhy yanzu wahala zakisha bata wasaba.
  Yau ba shirmenki ya kawoniba dan inada abinyi, gobe zan koma abuja, duk abinda kike bu'kata ki sanarma mas'ud.
    Hummm kaidai kasha cizo malam, yasmeen tafaďa a zuciyarta.
   Saida ya'kara mirtike fuska sanan ya ce, "ki koma makarantarki idan kina ra'ayi.
   Cikin murna yasmeen ta ce, "dgsk??, harararta yayi ya ce, "k bana son shirme kinji.
   Baki ta murguďa masa, ya ce, "dawa kike???, ta ri'ke 'kugu da wanda ya tsargu mana.
    Nawaf yay murmushi danshi dariya ma tabashi, yakula ta rainashi da yawa, amma zai koya mata hankali kwanan nan,     ya ce, "habawa yarinya wataran ko ance kiyi mini rashin kunya bazakiyi ba wlhy.
   Kud'i ya ajiye mata 'yan dubu2 ďauri biyu, ya mi'ke, karki ďauka dan bananan ko dannance ki koma makaranta ki ďauka kinsamu hanyar yawo, nasaka masu kulamin da shigarki da fitarki, idan naji wani abu sa6anin dokar dana kafa, tofa kiyi kuka da kanki, yana gama faďa ya fice.
   Harara yasmeen tarakashi da ita tana faďin sai an karya dokar taka, tunda ba dokar ALLAH ba ce, "mutun ya rin'ka abu saikace wani ubana.
   Tashiga kwaykwayon maganarsa yanda yakeyi aģadarence.

__________ABUJA________
 Bayan kammala (colfine second round) da akayi, Najeria ta tashi da maki 7.
   To ayau kuma zasu buga da Egypt, (colfine cotter pineal) wasan daf da 'karshe ke nan.
   Wasa yayima 9ja daďi, dan antashi 1-0, 
    9ja 1 & Egypt 0
 Karkuga murna wajen 'yan 9ja.

2days later.
   (Seme pineal) wasan kusada 'karshe, 9ja da South Afirica, wanan kuma ankai ruwa rana, dan sai ana saura minti2 atashi, cosee!, wani ďan wasan 9ja yay wani fasin da Nawaf yasamu damar antayawa 9ja kwallon cikin ragar south Africa, guri yaruďe da ihu Najeria sai murna mukeyi.
   Dukkanin wasanan yasmeen ta kalla, dukda bawani burgeta yakeyiba, amma takanji tana sha'awar kalla, da antashi zakaga yaseer yakirashi yana masa murna, takan ta6e baki ta ce, "ma yaseer uban 'yan shishshigi kawai, ďan san asani.
   Oho dai yaseer yafaďa, kema san asani ďin yasa kike kallon kwallon yanzu tunda da ba'ka kallo da.
   Duka ta kaimasa ya kauce, cikin shagwa6a ta ce, "umma kinga yaseer ko yana tsokanata.
   Umma ta ce, "kunfi kusa, kubar sakani ashirmenku kunji.
   Yaseer yatashi yafice yana mata gwallo.
    Kwafa tayi ta ce, "zaka dawo ka sameni yaro.

Yaune za'a buga wasan 'karshe, yaukam stadium d'in abuja babu masaya tsinke, dan yau harda shugaban 'kasar NAJERIA shima yazo.
   Bayan gama addu'a da abinda yadace,Najeria da Algeria suka fara buga wasa, kowa iya 'ko'karinsa yake a wasanan, dan haka har aka tashi hutun rabin lokaci babu wanda ya zira kwallo.
    Bayan andawoma gwagwar maya aka cigaba dayi, amma ina komai bai canjaba, tun ana saran wani zai ci har aka fitar da rai, lokaci yacika aka'ara, shima ya shuďe babu wanda yaci, dole saidai ayi (peneritty).

 *Algeria tafara zirama 9ja
 *Najeria sai 9ja itama ta zira
 *Algeria 
 *Najeria 
 *Algeria 
 *Najeria 
 *Algeria 9ja tazubar
 *Najeria 
 *Algeria 
 *Najeria Nawaf ya zira mana ta 'karshe.
    Dukkan filin da sassan gidajen kwallo dake Najeria suka d'au ihu na murn, bakin kowa abuďe, shugaban 'kasa yayi murna sosai.

  Duk da kwallo bata burge yasmeen to yau tayi murna sosai, sai murmushi takeyi dan daďi.
   Na ce, "humm yasmeen kodai???????.
   Bayan shugaban 'kasa ya karramasu kowa yanufi inda yafi wayo, (club club nasu kenan)
 Shidai Nawaf kano yataho..................




©2016



Bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
          luv u oll my fan's
[17/12/2016 20:21] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page 25 & 26

....To shima dai mas'ud a6angarensa komai ya dai2ta, har ankawo kuďi dan anaso ayi bikin tareda na Nawaf, yasmeen tayi farinciki sosai da faruwar haka, bare ameena amarya, ai tafi kowa farinci, dan tana son mas'ud sosai.
      Yau kuma aka kawo lefensu su duka akwatuna bakwai2, komai iri ďaya, wanan aikin papa ne, dan shida momcy suka haďo lefen.
     Wannan shi ake Kiran lefen 'yan gata, mutanen anguwa da dangi duk sun yaba.   
        Filin jirgin na kano cike yake da matasa domin tarbar NAWAF!!.
   jirgi yafara shawagi neman muhallin sauka, bayan tsayawarsa fasinjoji suka fara fitowa, Nawaf shine na 6, ahankali yake sakkowa kamar bayaso,  jikinsa sanye da 'kananun kaya, ya ďora 'katuwar rigar sanyi fara, ya saki hular a baya, sai tashin 'kamshi yakeyi, yagoyo jar jakka abayansa wadda aka rubuta (Adidas)na ce, "kai gay ďinnan handsome ne gsky.
    Da gudu anwar yaje ya rungumesa, shima cikin farinciki ya rungume shi, yana faďin i missing u autan momcy.
   Missing u too yayana.
   Gaba ďaya 'yan uwa da abokan arzi'ki suka taso gareshi, 'yan jarida kuwa sai 'kutsa kai sukeyi domin samo bayanai.
   Da'kyar suka barshi yashiga mota mas'ud yaja suka nufi gida, anata ďaga masa hannu shima yana ďagawa.
   Abdallah ya ce, "yaya dabamu samu mun gudoba dasai yamma zamu baro filin jirginnan.
   Nawaf ya ce, "gsky ne brother shiyyasa naso na sauka da daddare.
   Mas'ud yay dariya ai koda daddaren ne sai mutane sun jiraka tunda anuna a labarai zaka sauka kano yau, aii ko randa kazo daga Spain mutane basu taru hakaba??.
   Abdallah ya ce, "to ba sunga ya cimusu kwalloba yau, suka tuntsure da dariya su duka.
   Anwar ya ce, "nifa wani tsareni yayi saina bashi number yaya, na ce, "masa banida waya kuma ban ri'ke number ba.
   Mas'ud ya ce, "hummm autan momcy sarkin wayo.
   A babban tsakar gidan sukai Parking, Nawaf yasha mamaki dan ganin dangi cike da gida, 'yan katsina da saudia, duk sunzo, dangi sai rungumeshi ake ana murna, musamman 'yan saudia dansu dama al'adarsuce.
   Family falo suka nifa inda sauran dangi suke harda kakarsu Nawaf ta wajen uwa tanan darai hajja humaira kenan.
   Hajja humaira ta ringume Nawaf tana farin cikin ganinsa, ta ce Masha ALLAH mai gida ka 'kara 'kyau da girma, kodai an canja mini kaine??, Nawaf yay dariya A'a hajjana ba a canja miki niba ninedai maigidanki na 'karfen!!!.
    Gaba ďaya akasaka dariya, ta ce, "kamanta damu ko Nawaf!!?, da sauri ya 'kara rungume hajja ya ce, "ni na isa na manta daku, uwargida sarautar mata, hajja nayi missing ďinki sosai.
   Hajja ta ce, "ďan nema kai dai bazaki hausarba bare larabcin?, turawa sun 6ata mana ka!!.
   Nawaf yay murmushi yabi dukkan iyaye da kakannin yana gaishesu, har 'yan katsina.
   Ya ce, "ni banga sauran sisters ďina ba??, kobasu zoba??.
   Tab wazai 'kizuwa bikin ka (Abi)yaya kenan, kowa yazo, sauran suna gidan amaryarka, muma yanzu za'a kaimu, wai a al'adar hausawa yaune ('kunshi)to zamuje mu ganine!!.
   Nawaf yay murmushi, lallai kam idan kun gani saiku koya koh??, dariya ameera tayi ta ce, "to Abi!!.
    Duk da larabci suke maganar, ina fassara mukune yanda zaku gane lol.
    D'akin kusada papa ya shiga inda ya maida kayansa kafin yatafi, yay wanka, yaci abinci, kwanciya yayi domin yaďan huta.
   Sai wayarsa ta hau wringing, mas'ud ne yake kiransa, ya ce, "ďan uwa ya akayine??, ya ce, "tambayata ma kakeyi?? To kafito muje wajen kamu.
   Nawaf ya yatsine fuska, miye kuma kamu??, dariya mas'ud yayi ya ce, "idan munje zaka gani, kai malam nidai hajja haka ta ce, "mini sai gobe.
   Dariya mas'ud yayi ya ce, "nima wasa nake maka, bari nabarka kayi barci ka huta, sai mun haďu anjima.
   Okey bye Nawaf yafaďa yana ďaga masa hannu kamar yana ganinsa.
____________________________
    A 6angaren yasmeen kuwa suna gidan su ameena anan ake zaman 'kunshi, gidan cike yake da 'kawayensu da dangin Nawaf larabawa da 'yan katsina, muta nen saudia dai basa jin hausa saidai turanci, dan haka gurin yazama dandalin turanci, tunda duk sunaji.
   Wata mai 'kunshi aka ďakko tanama amare yasmeen da Ameena ta iya sosai, saikuma wasu su biyu sunayima 'kawayen amre suma kam gwanayene, yasmeen bata cikin walwala, amma bataso dangin Nawaf su gane dan haka ta saki jiki anata hira, Ameena ce kawai take gane damuwarta.
   suma sai jida ita sukeyi, wata budurwace dai yasmeen takula batada walwala, tunda sukazoma tanemi guri ďaya ta zauna ita kaďai, (ummu habeeba ce) tana mutuwar son Nawaf, ita ce Nawaf ya ce, "ta cika 'kyau, kuma gsky ya faďa dan tafi sauran 'yammatan 'kyau gsky.
   Sai dare aka maidasu gidansu Nawaf,, Nawaf yana zaune a harabar gidan tareda sauran samarin 'yan uwansa na katsina dana saudia, anata hira da raha.
   Moto ci suka fara sauke 'yammatan, wajansu suka nufo suna mai farin cikin ganin Nawaf, gaisuwa aka shiga yi irinta al'adar larabawa, ummu habeeba kam saita tokare agefe ta'ki zuwa, Nawaf yana ganinta ya shareta, saida ga baya kuma ya mi'ke ya nufeta.
   Tana sanye cikin ba'kar jallabiya ta naďe kanta da ďankwalin kamar yanda larabawa keyi.
   Ya tsaya yana kallonta, ta harareshi nagode abi tafaďa tana turo baki gaba.
   Yay ďan murmushi minayi miki kike yimini godiya??, tai far da idanu, ta ce, "kaima kasani.
   Yay murmushi har fararen ha'koransa suka bayyana, yasan inda ta dosa amma saiya basar, ya ce, "kinga koma mikike ganin nayi miki to ki share ki tayani murnar aurena kamar yanda kikayi niyya tun farko, wananne zuwanki 9ja na farko ko??.
   Bataso aka daina waccan maganarba amma yazatayi tunda ya nuna bayaso, ta ce, "eh shine na farko, ahaka dai sukaita hirarsu, cikin harshen larabci.
_______________________KAMU.
   Yau takama kamu, kamu kuwa za'ayi irin na saudia ne, a harabar gidansu ameena za'ayi saboda yafi girma, an 'kawata gurin da kwalliya mai tsari, an baza 'katuwar darduma inda amarya da ango zasu zauna, agefe kuma an jere fararen kujeru inda sauran mutane zasu zauna.
    Hajja ce tazo da kanta ta ro'ki su umma akan abarasu suma suyi al'adarsu ta larabawa a wajen kamu, su umma sukace babu damuwa suma sunada iko akan komai aii.
    Wajen 'karfe 4:00pm na yamma aka gama shirya amarya cikin ba'kar doguwar riga ba'ka mai ďan karen 'kyau, gashinta yasha gyara an ďaureshi abaya wanda bai saniba saiya ďauka itama balarabiyar ce, dan NAFISAR KADUNA ce ta tsara mata kwalliya wadda amaren zamani suke yayi.
   Kowa ya hallara sai amarya datake falo tana jiran isowar ango, dan tare akeso su fito.
   Bayan kamar minti10 ango ya iso da tawagar abokansa, kowa ya zauna inda ya dace, aka raka ango inda zai ďakko amaryarsa.
  Kai kawai ya tura cikin falon batarda yayi sallamaba, tana zaune akujera hankalinta yana kan waya tana game.
    Ai gogan naku yana tsaye ya daskare dan ganin tsarin hallita irinta ubangiji, gsky koba komai yayi dacen mata 'kya'ky'kyawa rashin kunyartane kawai matsalarsa.
    Jitai kamar alamar mutum yana kallonta, ta ďago da sauri, Nawaf tagani tsaye kamar gunki yayi masifar 'kyau cikin kayan larabawa wando da riga farare, anyi musu kwalliya da golden ďin zare, sumarsa tasha gyara daka gansa kaga cikakken balarabe.
   Saida ta murguďa masa baki ta ce, "malam lafiya??, katasani gaba kana kallo, mi naci naka??.
   Hararar ta yayi ya ce, "ki ajiye makaman rashin kunyarki har zuwa nanda kwana uku, domin yanzu ina kan bin umarnin iyayenane, bazanyi abinda zai 6ata musu rai ba agaban ďumbin jama'ar dasuka tara.
    Yay wani murmushin mugunta, yaďora da faďin amma nanda kwana uku, ko ance ki kalleni kimin rashin kunya wlhy baza kiyiba, dan zanyi maganinki 'karamar mara kunya kawai.
  Ta buďe baki domin mayar masa da amsa sai aka turo 'kofar.....wata 'kanwar momcy ce Fateema, ta ce, "Abbuna ku ajiye wannan soyayyar taku sai nan da kwana uku dan yanzu mutane suna jiranku.
   Nawaf yaďan sosa gefen wuyansa ya ce, "sorry Abla(aunty kenan) muna zuwa.
   Ya juyo ya harari yasmeen sanan ya 'karasa wajenta, hannunta yakama, jikin yasmeen yay wani yarrrrrrr, shimadai gogan naku saida sassan jikinsa suka amsa, Abla fateema ta gyarawa yasmeen ďankwalinta tabaya, sannan ta rufe mata fuska da wani jan gyale.
    Nawaf ya ce, "Abla ai bata gani, idan ta faďi fa??.
   Abla tayi dariya kai ka bari tafaďi bayan kaine ďan jagora.
    Ya ce, "hakane idanma kin amince na ďauketa gaba ďaya naje na dire awajan.
   Abla fateema ta tuntsure da dariya ta ce, "babu ruwana.
   Yasmeen ta ce, "azuciyarta mugu saika nemi wadda zaka ďauka amma baniba.
   Catake a zuciya take magana bata san afili takeyiba dan Nawaf yana jinta, amma Abla bataji tunda da hausa take maganar kuma ahankali.
    Bayan sun fito gurin ya ďauki tafi, wajen kujerar da'aka tanadar musu mai ďan faďi sukaje suka zauna, saidai sun matsu juna sosai, yasmeen sai takurewa takeyi.
   Agaban kujera aka shimmfiďa dardumar daza ayi kamu.
   Ba6ata lokaci akayi addu'a ga ma'aurata, har yanzu fuskar yasmeen a rufe take.
   Nawaf tya ce, "malama nifa kin matseni.
   Dariya bin yabama yasmeen dan haka tayi murmushi, ta ce, "kanka akeji wai mahaukaci ya faďa ruwa.
   Nawaf yay murmushi mai sauti, kema za'aji kankine yarinya, dan ďazu ina jinki.
   Idan kagansu saika ďauka hirar arzi'ki sukeyi.
   Bayan angama addua aka fara shirin kamu, ango da amarya suka sakko 'kasa kan dardumar, suna fuskantar juna fuskar yasmeen arufe.
   Wani haďaďďen kwando aka ajiye agefensu wanda yake cike da turarurruka kala2 masu tsada da 'kamshi, abla ta su'ko tanama Nawaf magana acikin kunne da larabci, wanan yasa yasmeen bataji abinda suke faďaba, yay murmushi tareda jan kwandon gabansu.
    Saida akasaka wa'ka wadda akayima ngo da amarya amna da larabci, sannan aka bama ango umarni yashiga cikin gyalen da'aka rufe fuskar yasmeen dashi.
   Ya yaye ahankali ya rufa akansa, yazama su biyune aciki.
   Kan yasmeen na 'kasa Nawaf ya ce, "ina fata dai al'adarmu ta 'kayatar dake, taďan ďago ta kalleshi ganin ya kafeta da idanu yasa ta maida kanta 'kasa da sauri.
   Turare ďaya aka mi'ko masa yashiga fesama yasmeen, harda mugunta saida ya 'karar da turaren duka ajikinta, saboda 'karamar kwalba ce, fitinannen 'kamshin ya gauraye wajen.
    Ya yaye mayafin daga fuskokinsu, gaba ďaya gurin aka saka tafi, daganan kowa yataso saiya ďauka a kwandon yazo yaďan fesa musu, saida kowa ya fesa sanan aka rufe taro da addu'a kowa ya kama gabansa.
____________________________
    Yau aka ďaura auren mas'ud da Ameena, ALLAH yasanya alakairi mas'ud.
    Da yamma aka tafi bababan filin kwallo na kano anan za'a buga wasan biki, wanda (KANO PILLAS SUKA SHIRYA DOMIN KARRAMA ANGO) an tsara wasanne 6angaren ango da amarya, abokansa 'yan kwallo dasukazo daga 'kasashe daban2 da 'yan kano filas, 'kuria aka yi idan ka ďauki 6angaren ango kona amarya to suzaka bugawa.
    Wasankuwa ya 'kayatar dan har a labari aka nuna, antashi 8 da 5, ango 5 &amarya 8.
------------------------------------------
   Da daddare aka shirya kai amare ďakinsu anan naga kuka, yasmeen kuka take kamar ranta zai fita, sai nasiha da lallashinta akeyi, hakama ameena.
    Da 'kyar aka 6an6are yasmeen daga jikin umma, tanata kuka dafaďin bazatajeba itafa tafasa aueren, amma ina, tuni aka dannata amota, sai gidan ango.
   An mi'ka Amin gidansu mas'ud yasmeen kuma gidan su Nawaf, a ďakin momcy.
   Bayan kamar minti30 aka shiryasu zuwa wajen gagarumar dina da abokan Nawaf suka shirya, amma sun haďe harda mas'ud, ammafa wajen ya 'kayatu sosai.
   Amare sunsha shiri cikin rigunan aure,  yasmeen sai masifa takeyi, wai rigar arna, Nawaf yana jinta yay mata banza.
   Komai ya 'kayar agurin, amma wajen bada cake Nawaf saida ya ciji hannun yasmeen, tai wata 'yar 'kara, wadda tasa muta nen gurin ihun dariya a zatonsu duk cikin soyayyane lol.
    Sai shabiyu aka tashi, idanun yasmeen cike da barci, suka fiffito tana tangaďi, ga wani dogon takalmi data saka, tako goce zata faďi da sauri Nawaf ya tarbota ta faďo jikinsa, sai kawai ta lumshe idanu dan barci takeji.
   Girgizata yayi da 'karfi, ke dallah malam tashi karki karya mini hannu, inko ba hakaba zan sakeki ki faďi 'kasa ALLAH.
   yasmeen batasan yana yibama, Kausar ta ce abi! ka ďauketa kawai wlhy barci takeyi tagaji dayawa ne.
    Bayaso danginsa su gane komai gameda auren, dan haka ya sa6eta kawai sai ďakin momcy, ALLAH ya taimakesa ma 'yammatan ne a 6an garen momcy, kuma babu wadda yake jin kunya acikinsu.
   Ruwa ya ďauka a saman madubi da wata tasha tarage, yazuba ahannusa ya shafa afuskar yasmeen, tako kawo numfashi.
    Ahankali ta buďe idanu tana kallonsa, ya ce, "ke kitashi kicire wanan rigar, sanan ki kwanta yana gama faďa yafice, da'kyar ya iya tashi tacire, ta koma ta kwanta................

    Na ce, "asuba tagari yasmeen.










©2016



bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
         luv u oll my fan's
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Blog Archive

Contact Form

Name

Email *

Message *