check your best novels here

Wednesday 1 March 2017

NAWAFF!!! 47/59

[26/02 15:14] Abba Gana: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page47 & 48

.....Sai wajen shaďaya suka tashi, dan zan iya cewa kusan lokaci ďaya suka tashi, yasmeen jinta take wani fayau kamar isaka zata ďauketa, yanzuma saida ta'kara shiga ruwan zafi, tagasa jikinta tayi wanka, bawata kwalliya tayiba fauda kawai tashafa sama2 sai kwalli, tasaka siket da riga na atanfa, tana son fita gaidasu momcy amma tanajin kunya, bakuma taso ta haďu da Nawaf, takoma bakin gado ta zauna shiru, maganganu takeji 'kasa2 afalo, tami'ke ahankali tafito, dai dai nan Nawaf shima yafito sanye cikin farar shadda ďinkin zamani, kallo ďaya tayi masa ta ďauke kai, su ladidi suka rissana suna gaishesu, kusan atare suka amsa.
   Yasmeen ta ce, "sannunku da 'ko'kari ladidi harkun gyara waje haka??, talatu ta ce, "ai tun ďazuma mukayi hajiya yanzuma abincine momy tasamu mu kawo muku.
      ayya to sannunku da 'ko'kari kunji, ALLAH yabiyaku ya baku miji nagari.
   Sukace ameen suna dariya, dan sunajin daďin addu'arta.
  Bayan fitarsu tawuce kichin batareda ta kalli ko'inda Nawaf yake zauneba, binta yayi da kallo harta shige, tafiyarta ta canja, gsky tabashi tausayi, shima saidaga baya yagane yayi 6arna baikuma tausayamata ba, to asannan idanunsa yarufe baya tana komai, harta fito yana zancen zuci.
    Shayi tahaďa masa da sauran kayan break ďin, tazo gabansa ta ajiye saman tebirďin tsakkiyar falon,  dan tasan baya cin abinci a dinning, tagama jerewa takoma gefe tazauna da kofin shayi ahannunta batareda tayi masa maganaba.
    Shikuma sai binta yake da kallo kamar yau ya fara ganinta, ahankali ya furta xarah!, wani zuuuuuuu yasmeen taji acikin kanta, bakowa yake kiranta da ainahin sunantaba fateema barema xarah, saitaji sunan wani iri kamar banataba kokuma wani (SABON AL'AMARI) sabon littafina mai zuwa insha ALLAHU.
   Jin tayi shiru yakuma faďin xarah!!, wannan karon har tsigar jikinta saida ta tashi, dan saida yaja sunan, ta ďago manyan idanunta tana kallonsa, shima kallonta yakeyi, ta kauda idonta daga kallonsa ta ce, "ina saurarenka.
   Ya gyara zamansa har yanzu idonsa yana kanta, ya ce, "zonan kiji mana, batareda ta kalleshiba ta ce, "kafaďa ahaka mana aii inajinka, yakai hannu yana shafa gemunsa tareda kwantar da bayansa jikin kujera, ya ce, "plz kizo kici abinci".
    Saida ta kalli kofin shayin dake hannunta sannan ta ce, "bagashi ina shaba.
    Shayi aiba abinci bane xarah, ana shanshine kawai dan hanji ya warware, saida taďan ta6e baki sannan ta ce, "karka damu nikam ya isheni, tasowa yayi yanufo inda take danyaga magana bazata yimasaba, ya zauna kusada ita sosai, saita matsa, ya ce, "tofa fancy face guduna kikeyi kuma??.
   Ta haďiye shayin data kur6a sannan ta ce, "ai mugu abin gudune, yaďan zaro ido nine mugun??, tami'ke tsaye tana faďin kaima shaidane aii, nikam saidai nabawa wasu labarin muguntarka, tana gama faďa tashige bedroom tarufe.
   Yabita da kallo yana murmushi lallai yarinya kina nufin ba'azo 'karsheba kenan?? Aii dolene kiyi ha'kuri dan nariga nayi winning game ďin, kekuma kinada game over, result kaiwai nake jira, kujerar daya taso yakoma yahau cin abincinsa.
   Bayan ya kammla ya gyara wajen, yanason zuwa gaida su momcy yana tsoron haďuwarsa da papa, yasan momcy tanada saurin fushi amma tanada saurin sauka, amma papa sai a hankali, yanzu yana zuwa zai hau kansa da faďa ALLAH ne kawai zai kwacesa, kamar daga sama yaji sallamar mas'ud, ya amsa yana faďin bismillah dama gunka zani ďan haďi, mas'ud dake shigowa ya ce, "ďan haďi ko ďan faďar gsky, Ameena ma ta shigo, Nawaf ya ce, "ALLAH yasoka harda Ameena dasai ka yabawa aya za'kinta.
    Mas'ud da ameena suka zauna suna dariya, mas'ud ya ce, "malam mika isa kamin nidai gsky nafaďa aii, babu wani gsky malam kazo kawai kayimin haďi awajen su momcy, yanzu haka tsoron zuwa gaida papa nakeyi.
   Hhhhh gay kace kotu zaka shiga babu lauya kawai,, Nawaf suka gama gaisawa da ameena sannan ya ce, "aiko maga takaddama babu, suka tuntsire da dariya su duka.
  Yasmeen tabuďe ďaki tafito danjin an ambaci sunan Ameena, cikin farin ciki ta rungume Ameena saidai fuskarta tana nuna kamar batajin daďi, Ameena ta ce, "yar uwa ykk, lfy lou 'yar uwa ya 'karfin jikinki??, Alhmdllh, aini sainaga kema kamar bakida lafiya?, saida ta kalli Nawaf sannan ta ce, " 'kalau nake sister mikika ganine??, ba komai nagankine fayau.
   Mas'ud yakali Nawaf kallon tuhuma, da ido yay masa magana wai lafiya, Nawaf ya datsa hannunsa saman ďayan tafin hannunsa Alamar yagama aiki, ido mas'ud yazaro ya ce, "kai haba??.
    Nawaf yay wata 'yar dariya yana faďin angaya maka nina wasane, am winning wlhy.
    Yasmeen duk tana kallon zancen kurman dasukeyi, dan haka suna haďa ido da Nawaf ta harareshi, yay ďan murmushi yana shafa sumar kansa, tami'ke takawo musu ruwa da lemu, saida tagama basu sannan takama hannun Ameena suka shige bedroom, mas'ud ya ce, "za'ayi gulmarmu ne??, Ameena tajuyo tana faďin idan kunsan kunyi abin gulmar ba.
   Nawaf yaďago daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, mutumina kaima kasani zata gumtsa matane kawai, mas'ud yay dariya amma kaimafa ďan iskane, tokaida bakada lafiyama ina kaga 'karfi.
   To sarkin 'yanson gulma ina ruwanka, nida wajenkama zani samo mata magani saikuma naga momcy tabata wani, amma kamarfa bai mata aikiba, naga tana tafiya bayanda tasaba ba.
    Kai ďan duniya kana nufin har momcy tasani?,, kabari kawai nima wlhy banso hakanba, amma tazo ta ritsani..
   Hhhhh lallai kacika mara kunya kuwa Alhaji,, Nawaf ya harareshi, nida kai a tantance mara kunya, jiyafa inajinka sama2 kana koro rashin kunya,, hhhh aini akan aikina nake ehe.
   Ummmm lallai kam su aiki manya....

Suma su yasmeen ana 'kuryar ďaki itada tata aminiyar, Ameena ta ce, "yasmeen mike damunkine wai??, yasmeen tayi kwalkwal da idanu tana shirin yin kuka, cikin rawar murya ta ce, "Ameena mugunnan yasameni abanza batareda yafara sonaba kamar yanda muka shirya dake.
    Ameena tazaro idanu kai sis... garin yaya hakan tafarune?, yasmeen tafaďa mata yanda sukayi da umma jiya, taďora dafaďin dagafa bashi ha'kuri yay min faďe, dan nidai faďe zan kira wannan wlhy.
   Ameena tayi dariya A'a babu wani faďe, mutum da matarsa sai ace yayi faďe, kice 'yar uwa angirma,, yasmeen ta harareta kin ganki ko zaki fara.
   Ameena tadafata tana dariya yiha'kuri amarsu, haba shiyyasa naga Nawaf yanata fara'a ga 'kyallin angwanci yanayi.
   Harrarta yasmeen tasakeyi, tana kaimata duka da filo, itakuma Ameena tana tuntsura dariya dabata ha'kuri, tari'ke filon tana sassauta dariyarta, kinga yi ha'kuri na daina, yanzudai ya ake cikine??.
   Yasmeen ta ce, "ai saina garashi nima, dan bazai shani abanzaba, duk muguntar dayayimin saina rama,, A'a yasmeen kawai kishare, kinga ko ada kema kina masa rashin kunya, kinga kenan kowa yana ta6a kowa, kawai ki ringumi mijinki ku zauna lafiya, fatanmu yanzu kuma muga sakamako kawai, kayan harka na nan zan aiko haleematu takawo miki.
   Cikin rashin fahimta yasmeen ta ce, "miye kuma kayan harka??, saida ameena tayi 'yar dariya sannan ta zayyane mata komai, tab ALLAH yakiyaye yasmeen tafaďa, ni nasha wani abu, kina ganin ba'kar wahalar danasha hannun mugunnan jiya, ke kobansha wahalaba babu abinda zansha inma gaya miki gsky, kawai saina zauna nayita ďirkar magani batareda ciwoba, 'katon banza yayta shan romo yana raina mini hankali ko,, aii badan wannan nazo duniyaba 'yammata.
   Oh oh yarinya zaki shane, ina zaune zakizomin da zancen, idan ALLAH yabaki fitinannen miji irin mas'ud wlhy dole kisha, kuma ina nan dake zaki bani labarine.
   Baki yasmeen ta ta6e ke nifa bazan zauna yamaidani wata kasar takawarsaba,, dan haka kima daina saran zan sakko wataran.
   'yammata kenan mudai 'yan kallone, yasmeen ta ce, "uhmmmm keni mubar wannan zance kitso najeson yi yaza'ayine?, wake miki kitso?.
   Uhmmmm wata yarinyace a 'kasan layinnan, idan kin shirya sainasa su halimatu su kawo miki ita, to shikenan amma kinsan halimatu bata zuwa gidannan saboda momcy ko??.
   Hhhh ke bar 'yar iska amma ai batajin kunyar yin zancen Abdallah gaban mami ko?.
   A'a shima ai hakan take, ko agaban papa labarin masoyiyarsa yake, ranar inaji modebbo yana masa masifa wai bashida kunya.
   Tofa kaji manya su kunyar garesu?, 'k wai kema modebbon kike cemasane??, yasmeen ta ta6e baki keni duk sunan dayazo min nasa faďa nakeyi wlhy,  A 'yammata yakama acanja masa suna.
   Yasmeen ta ce, "k bayanzuba saiya jigatu sannan, dan idan nabarsa haka yaga lagona.
   Hummm yarinya kidaibi ahankali, mazan nan sunada hanyoyin maganinmu kala2, danhaka atafi a slowly..
  Suka tuntsure da dariya harda tafawa. 
     Nawaf yaturo 'kofar yashigo da sallama, Ameena ce kawai ta amsa masa, ya ce, "masu hira bari muje masallaci, kuma kutashi kuyi sallah.
   Ameena ta ce, "to, saikun dawo, harya kai 'kofa saikuma yadawo, yadu'ko ya sumbaci kumatun yasmeen, dasauri taďago tana kallonsa saiya ďaga mata gira yana murmushi ya fice.
    Ameena tayi dariya tana faďin soyayya ruwan zuma, 'yar uwa kibada kai kaiwai bori ya hau, tunda kuduka kun kamu, harararta yasmeen tayi tashige bayi domin yo alwala.
   Ameena taci gaba da dariyarta tana faďin anaso ana kaiwa kasuwa.
   Bayan sun idar da sallah suka dawo falo, abincin dasu talatu suka kawo yasmeen ta jera musu akan daining.  
   Suma su Nawaf bayan sun dawo daga sallah wajensu momcy sukaje suka gaishesu, zuciyar Nawaf tanata dukan uku2, amma abin mamaki papa baimasa faďanba, yasan saboda suna tareda mas'udne shiyyasa ya 'kyaleshi.
    Yasmeen ta kalli Ameena, wlhy 'yar uwa inason zuwa gaidasu momcy amma inajin kunya, wannan gay ďin dukshi yaja min wlhy, saitaji Nawaf ya ce, "zomuje narakaki tunda nine naja miki.
    Dasauri suka juyo inda maganar tasa take, ashe tun đazu sun shugo suna tsayene kawai suna kallonsu yasmeen.
   Su mas'ud suka 'karaso suka zauna, yasmeen ta zuba musu abincin amma ta'ki yadda su haďa ido da Nawaf, ta turama kowa gabansa, ita kuma tazuba ďan kaďan, Nawaf ya kalleta xarah wannan abincin fa??,    ta ce, "kamar yaya??, yajawo kujerarsa kusada ita batareda yayi maganaba, yabuďe kulan abincin ya 'kara mata, da sauri ta ce, "wazaici wannan abincin??.
    Ke mana, ko kina nufin zancigaba da barinki da yunwa? Tun jiya rabonki dacin abincifa, gama magani nan mas'ud yakawo miki, idan kin gama saiki she. 
     , ta shagwa6e fuska nifa lafiyata 'kalau, Nawaf ya murmusa nima nasan lafiyarki 'kalau fancy face, saidai yanada 'kyau kisha maganin dan tafiyarki tadawo dai2... ya 'kare maganar ahankali yandasu Ameena bazasujiba.
    Ya ďauki cokalin ya ďibi abinci yakai bakinta, ta kauda kai gefe tana faďin kabari zanci dakaina, A'a ban yardaba, ta ce, "ALLAH zanci dakaina.
   To naji kar6i wannan saina barki kici dakanki ďin, bataso suyita ja'inja agabansu mas'ud shiyyasa ta kar6a, yawani kashe mata ido ďaya wanda har murmushi yanemi su6uce mata amma saita dake, haka taita tura abincin badan yana mata daďiba, su Nawaf suna hirarsu amma ita tayi shiru abinta,     bayan sun kammla suka dawo falo suna hirarsu.
      Sai bayan la'asar su ameena suka tafi gida, dan mas'ud yanada aikin dare yau, tunda suka tafi yasmeen taje wajensu momcy tayi zamanta dukda ďunbin kunyar momcy datakeji, shima Nawaf bai dawoba sai bayan isha'i, shima 6angarensu momcy yanufa acan ya tararda yasmeen suna hira itadasu Anwar.
    Ya zauna suka gaisa da momcy, su Anwar suka gaisheshi, sunanan zaune shi yana latsa waya sukuma suna hira, soyake su tafi kafin papa ya ritsashi amma yarasa yanda zaima yasmeen maga, yana zancen zuci sai sukaji sallamar papa.
     Yashigo falon kowa ya rissina yana gaisheshi, ya amsa yana zama, momcy takawo masa ruwa yasha, yami'ke yana faďin modebbo zonan, jikin Nawaf asanyaye yabi papa ďakinsa, afalo suka yada zango, yasmeen yazauna 'kasa papa yana saman kujera.
    Papa ya ce, "modebbo dama abinda kake aikatawa kenan ban saniba??, Nawaf yaďago fararen idanuwansa yana kallon papa, cikin raunin murya ya ce, "papa miya faru??, cikin faďa papa ya ce, "o, bakasanma miya faruba ko??, papa yashiga yimasa faďa tamkar zai dakesa, ta inda yake shiga batanan yake fitaba, saida yaymasa tatas sannan ya ce, "ni tashi kabani waje mutumin banza.
   Nawaf ya ce, "kayi ha'kuri papa na amsa laifina amma insha ALLAHU hakan bazata sake faruwaba, kuma mun daidaita itama nabata ha'kuri.
  Papa ya ce, "wannan kuma kaika sani, idan kabari ta su6uce maka aikaika jiwo baniba, tashi kabani guri nace.
     Nawaf yami'ke yafito dama yasan papa bazai saurareshiba a yau saiya huce.
   Yafito falo wajensu yasmeen fuskarsa babu walwala ya ce, "yasmeen tashi mutafi,, ta ďaure fuska katafi ni anan zan kwanafa,, shuru yay yana kallonta, yazata momcy zata mata magana amma saiyaji tayi shiru bata samusu bakiba, ya daure ya ce, "bangane anan zaki kwanaba?, gidankifa?, yasmeen tayi kwalkwal da ido kamar zatayi kuka ta ce, "nidai anan zan kwana kawai.
    Jiki asanyaye yafice batareda ya'kara maganaba bare ya ce musu "saida safe", itako mom 'kala batace musuba, daga 'karshema saita tashi ta tafi ďakin papa.
    Nawaf yafaďa saman gado yana maida numfashi, yakula mitin aka haďa saboda shi kenan,, zaikuwa basu mamaki, zai nunawa yasmeen shima bai damu da itaba.
   Itako tayi kwanciyarta acan abinta, shikam haka yayta zarya tsakanin falo da bedroom, yazata daga baya momcy zata saka yasmeen ta taho, amma shiru kamar an aiki bawa garinsu, daga 'karshe yaha'kura yakwanta.

Haka sukaita 'yar wasan 6uya shida yasmeen har tsawon kwana huďu, tayi zamanta a ďakin momcy, kotana falo dataji sallamarsa saita koma ďaki ta kulle, tun Nawaf yana ďaukar abin wasa har yafara bashi haushi, yakoma bashi tsoro, dan akowace da'ki'ka son yasmeen 'karuwa yake azuciyarsa, gashi kuma ta hanashi damar dazai nuna mata ainahin gsky sa, momcy kuma tayi kunnen uwar shegu dasu, ta'ki tayima yasmeen magana ko kaďan, dukda tana kallon zaman doya da manjan dasukeyi, amma saita maida kanta makauniya.
    Itama yasmeen a 6angarenta tana jigatuwa da horon datakemusu dan harda kanta take horawa, kewar Nawaf dukta gallabi zuciyarta, idan yashigo haka zatayita le 'kensa ta kafar makulli, dukta rame akwana huďu, sai wani fari datayi fauu.
   Amma haka zata cigaba da daurewa har komai ya daidaita. 
    
Yau dawuri mutan gidan suka kwanta sakamakon gajiya dasukayi, dansunje wani biki, kowa yana ďakinsa kwance wasuma harsunyi barci irinsu yasmeen, Nawaf kam yanacan yakasa rintsawa, ya buďe wardrobe ya ďakko kayan daya cire, wani mukulli yaďakko acikin aljuhun rigarsa yakallesa yay murmushi, tirare ya 'kara fesama jikinsa, yasaka silifas yafice bayan yakashe komai.
    Ahankali yatura 'kofa yashiga 6angaren momcy ta 'kofar baya, yashgo ta kichin dan ba'a kulleta dama.
   Falon babu kowa anma kashe fitilar, dagaji kasan kowa yayi barci, Nawaf yay murmushin mugunta, yasaka key ďin yabuďe ďakin momcy, yamaida yakulle ahankali, fitilar ďakin akashe take, danhaka yataka ahankali zuwa bakin gadon, wayarsa ya danna ya haska yasmeen dake kwance ta 6ararraje tana sharar barci agadon momcy, yasaki wani 'kayataccen murmushi, yaďaga bargon ahankali yashige, tareda rungume yasmeen zuwa jikinsa.
     Afirgice tafarka, tako buďe baki zatayi ihu, Nawaf yay saurin toshe mata baki da hannunsa ďaya, cikin kunnenta ya ce, "k karki taramin mutane ninefa...................


Tofa 'ka'karaka 'ka'ka, kudai biyoni kawai







©2017


bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
          luv u oll my fan's
[26/02 15:14] Abba Gana: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 49 & 50

.....Iya 'karfinta ta tureshi, tana faďin bangane kaineba?, miya kawoka nan??.
   Nawaf ya kunna fitilar dake saman durowar  gefen gado haske ya gauraye ďakin, ya maida kallonsa ga yasmeen data koma can nesa dashi, yaďan murmusa sannan yamatso kusada ita, ta ce, "wai miye haka?, zakazo katasheni ina barcina.
    Ya kamo hannunta ya rumtse anasa, batayi yun'kurin hanashiba dan tayi kewarsa itama, cikin taushin murya ya ce, "fancy face kinso ki tashine kawai, kuma mutum da matarsa ace miyasa yazo wajenta??.
   Yasmeen ta ta6e baki to amma kasan bai daceba ko?, a ďakin mom mukefa, shima bakin yata6e yana faďin ainasan a ďakin mom ďin muke bake kika kawomuba, ni kinga zuwa nayima kimin tausa wlhy jikina sai ciwo yake wannan bikin da papa yakwashemu mukaje.
   Yasmeen taďan zaro idanu lafiyarka kuwa malam??, tafaďa tana fisge hannunta daga nasa,, yakuma kamo hannun yana wani 'kasa2 da idanu, lafiyarce takawo haka xarah, idan ba keba wazance yay mini tausa?.
   Yasmeen tazame takwanta, saida taja bargo sannan ta ce, "nima ďin bayimaka zanyiba kaini bamma iya wata tausaba, idan ka fita karufo mini ďakin, ta kwantar da kanta saman filo.
    Okey karki damu 'yammata, tashi yay kamar gsk ya kashe fitila, yaďaga bargon yashigo, da sauri yasmeen ta yun'kura zata tashi, yay saurin ri'kota ya matse a 'kirjinsa, tafara 'ko'karin kwacewa amma takasa.
    Yasaki sassanyar dariya acikin kunnenta, yasmeen ta rin'ka ture fuskarsa, ya kamo hannun ya ri'ke, yana faďin haba xarah na, kina nufin haka zan cigaba da rayuwa ni kađai, duk wannan 'kamshin dakike zubawa ni bazan sha'kesaba naji daďi.
   Ninefa modibbonki mai sonki da 'kaunarki, i luv u my zarah, kece farincikin Nawaf modebbo.........dasauri yasmeen ta katseshi bayan wani daďi da farinciki sun gauraye dukan sassan jikinta, ta ce, "humm malam karka cikani da surutu kana yaudarar kankane kawai, kada kayi tunanin zaka iya wasa da hankalina mana.......da sauri yarufe mata baki da lallausan hannunsa, karki damu, bata baki kawai ake bayyana so ba akwai hanyoyi dayawa, yashiga aika mata sakwanni, itakuma tana tureshi tana masifa, dayaga zata dameshi da hayaniya harma wani yaji saiya haďe bakinsa da nata.
   dagudu nafito

Humm su Nawaf manyan 'yan duniya, koda ya daidaita saiya shiga lallashinta da faďa mata kalamai masu daďi, ya'kara jaddada mata iri son dayake mata, yasmeen sai hawayen daďi take zubarwa, jitake tamkar ta rungumeshi tahaďa masa harda 'kyautar kiss to amma bazata nuna masa tama yarda dashiba, ta tureshi ta mirgina gefe tana cije la66a dan itafa yauma tanajin ďan zafi, tashige bayi, shikuma yana binta da kallo yana murmushi, ahankali ya lumshe fararen idanunsa masu yalwar gashi, afili ya furta 'yammata kaďan yarage kizo hannu, shima saiya sakko yanufi bayin.
   Yamurďa kofar ahankali yashiga, dasauri yasmeen tabuďe ido tana kallon 'kofar, tami'ke zummbur tana 'kudundune jikinta, cikin rawar murya ta ce, "wai miye hakane??, yafara zame kayan jikinsa batareda ya tanka mataba, taisaurin dur'kusawa tarufe idonta da hannayenta.
   Yagama cire kayansa ya'karaso inda take, ruwa ya ďiba yazuba mata, taďago da sauri zata yimasa kwakwazo yasa hannu yarufe bakin, "k wai lafiyarki kuwa??, darenefa kuma su papa zasu iya jinki ki kula mana.
   Harara ta watsa masa tana zum6ura baki, ya murmusa kai xarah kina 'kyau da harara plz kicigaba karki daina, shiru taimasa, shikuma yafara 'ko'karin yimata wanka, tanata kauce2 dahaka aka gama wankan suka fito, badan tasoba tayarda suka kwanta gado ďaya babu daďewa barci yay gaba dasu.
    Da Asuba koda yasmeen ta tashi saitaga babu Nawaf, tajawo filon daya kwanta ta rungume tsam a'kirjinta tana murmushi, afili ta ce, "sarkin wayo, wato danayi barci saika gudu ko??, karka damu lokaci yana zuwa dazan baka kulawa ta musamman wadda zakayi alfahari dani ina sonka mijina, abinda kaiminne yasa nakasa fahimtarka, nazata nikaďaice nake dakon soyayyarka ashe kaima ka kamu, ta lumshe ido tana murmushi, saidatiji ana 'ko'karin shiga sallah sannan ta tashi.
       Shikam Nawaf tunda yaga tayi barci ya lalla6a yafice dan bayaso su momcy su gansa da safe, musamman ma papa dayake fita sallar asuba dawuri kuma hardasu Anwar.
   Tunda suka tashi yau momcy take bin yasmeen da kallon mamaki, dan duk wanda yaganta yasan tana cikin farinciki, sai wata walwala takeyi, suna cikin yin break Nawaf yashigo, ya rissina yana gaida momcy sannan ya haye saman tebir ďin shima, su Anwar suka gaisheshi, yasmeen ma ta gaisheshi, ya ce, "k wai bazaki bani abinci bane??, yasmeen tafara zuba masa tana zum6ura baki,, suna haďa ido ya kannemata ido ďaya, da sauri ta kauda kai.
   Nawaf ya ce, "momcy papa fa?, momcy ta ce, "yafita aiki modebbo,, da wuri haka momcy?, eh wai yanada aikine kuma shari'ar mai zafice yace,, tofa ALLAH ya yayyafa mata ruwan sanyi, yakamatama papa ya huta kahanan yayi ritaya kawai.
   Gsky ne wlhy abi, Abdallah yafaďa, momcy ta ce, "to saiku tayashi da addu'ar fatan alkairi, sukace to momcy ALLAH yaza6a mana abinda yafi alkairi.
   Suka cigaba dacin abincinsu, duk ďagowar da yasmeen zatayi sai sun haďa ido da Nawaf, momcy tana kallonsu, azuciyarta ta ce, "kwadai gama gulmarku yara, nidai babu abinda zance muku.
   Dahaka suka gama cin abinci, Nawaf ya ce, "zaije wajen mas'ud, momcy ta ce, "to adawo lafiya.
   Fitarsa babu daďewa halimatu tazo itada mai kitso, tunda suka shigo taketa kasa da kai, momcy ta ce, "ohni ďiyata Abdallah yaraba mana zuminci, yanzu bakison zuwa gidannan ko??, ta tsugunna tana gaida momcy kai a'kasa, yasmeen ta ce, "momcy barta kwanannan zamu yayibota tadawo gidanma ganmba đaya, inaga haka za'ayi yasmeen.
   Itadai halimatu sai murmushi take kai asunkuye, Abdallah yana gefe ya tsura mata idanu, ta ce, "aunty gamai kitsonnan aunty ameena ta ce, "nakawo miki ita.
    To 'kanwata ngd, amma yau anan zaki wuni koh?, da sauri ta girgiza kai tana murmushi, momcy ta ce, "aiko yau agidannan zaki wuni, yasmeen kuje 6angarenku ai dole ta sake dai acan, yasmeen ta ce, "to momy.
   Tashi sukai zuwa 6angarensu yasmeen bayanda halimatu zatayi dole ta amence zata wuni, suna tafiya Abdallah ya faki idon momcy yatake musu baya.
    Momcy ta ce, "oni ALLAH ya shirya minkai Abdallah.
    Na ce, "ameeeeeen.
   Yasmeen tazauna gaban mai kitso tana faďin manya za'ayi saratu.
      Halimatu ta ce, "kai aunty wannan gashin naki ai bazaiyi manyan kitsoba, wai miyasa masu gashi basusan 'kananun 'kitsone, aigara ki barsa atsefe ma.
   Yasmeen tashafa gashinta, wlhy nagaji dazama dashi haka, dole kullum saika gyara, azuciyarta ta ce, "ga wannan fitinatun yanasani ji'ka kai kusan kullum.
   Saratu ta ce, "to wanne iri za'ayi, eh yimini shikku banason yasauka abayana zai ringa damuna, shikku kam dana ďaure shikenan, okey to bari mugani.
   Abdallah yashigo da sallama, suka amsa masa suduka, yasmeen ta ďora da faďin to bita zaizai harka taho.
   Abdallah ya zauna yana dariya kai aunty keda kanki, koda yakema ai wajenku na koya keda yaya, dan soyayyarku abin koyi ce, đazufa ina kallonsa yana...........yasmeen ta zaro idanu yana mi??, habawa kabada himma yajika wlhy.
    Abdallah ya ri'ke baki, tab danaga ta kaina, dan saiyayi kamar ya cinyeni.
    Dariya suka saka suduka, halimatu ta ce, "dama ya haďa maka da duka aii........ta 'kare maganar da rufe baki, Abdallah yakoma kusada ita yazauna haba my luv ke kinyarda azaneni, yasmeen ta ce, "harma tabada gudummawar bulala kuwa.......ta kare maganar ahankali dan shigowar Nawaf.
   Ya watsama Abdallah harara, Abdallah yay kasa da kai yana faďin kai malam kana soyewarka nikam baxaka hananiba nima, azuciya yake maganar, halimatu kuma da saratu mai kitso suka fara gaisheshi, ya amsa yana shiga bedroom.
   Itadai yasmeen batace 'kalaba saima ta maida hankalinta wajen kallon hotuna awayar Abdallah daya ďakko jiya awajen biki.
   Abdallah ya mi'ke yana faďin aunty bani wayata na kama gabana, idan boss yafita saina dawo.
   Yakar6a yafice, sukuma suna dariya, yesmeen ta ce, "ALLAH yasa yajika.
   Suna cikin dariya Nawaf yale'ko yana kwala kiran Abdallah!!, yasmeen ta ce, "yafitafa tun ďazu, baice komaiba yakoma cikin ďakin, kwanciyarsa yayi yahau barci.
   Sukuma suna kitso suna hirarsu da dariya, ammafa kitson yana bada ma'ana, dan yarinyar ta"iya sosai.
    Sai wajen 'karfe ďaya Nawaf yafito cikin 'kananun kaya yasake wani wankan, shikansa kitson ya bala'in burgeshi amma saiya basar saboda basu kaďai bane, yaďan kalli yasmeen ya ce, "kutashi kuyi sallah tukunna lokaci yayi, nima nawuce masallaci.
   To adawo lafiya yasmeen tafaďa, su halimatuma sukace haka
    Nawaf ya ce, "halimatu kinaso kema Abdallah yamaidake mara kunya kamar shi ko??, kan halimatu a'kasa ta ce, "A'a yaya.
   To miyasa kike biye masa, ko kinaso yahure miki kunne ki'ki karatu kamarshi??, nanma kai tagirgiza,, to indai bakiso hakan tafaru kidaina biye masa, kibari harsai kin kammala karatunki kinji ko!!, to yaya insha ALLAH ngd sosai, yafice yana faďin karki damu saina dawo.
    Bayan fitarsa yasmeen ta ce, "oh ke halimatu tamkar zaki iya, halimatu tayi dariya, zan iya mana aunty, nima saida na ce, "masa mudaina nunawa harsai mun kammala karatunmu, shine ya ce, "wai dazafi zafi ake dukan 'karfe.
    Yasmeen tayi dariya, iko dai da gskyr sa, bagashi yanzu kowa yasaniba, tafaďa tana tashi, bayan sunyi sallah suka dawo kan aikinsu, su ladidi suka kawo musu abincin rana.
    Sukaci suka 'koshi sannan aka koma aiki, sai wajen karfe uku aka gama, suka koma 6angaren momcy, alkairi mai yawa momcy tayima saratu mai kitso sannan ta tafi, halimatu kuwa sai dare.
    Bayan sallar magriba momcy take cewa idan ALLAH yakaimu gobe zasuje abuja wajen wata 'kawarta, kuma harda su Abdallah.
   Yasmeen ta ce, "mom nima zanje,, momcy ta ce, "to ki tambayi mijinki idan ya yarda saimu tafi kwana ďayane xamuyi, yasmeen tayi shiru dan tana tunanin yanda za'ayi ta tambayeshi, momcy ta ce, "indai baki gaya masaba tom ke kaďai zamu bari agidannan, zumbur yasmee ta mi'ke tanufi 6angarensu, momcy tayi murmushi kawai.
    Afalo ta iske Nawaf saman doguwar kujera kwance, hannunsa ri'ke da remote yana canja tashoshi, tayi tsaye abakin 'kofa tana kallonsa, yana ganinta ta gefen ido shima amma yay shiru kamar bai gantaba, takai tsawon minti bakwai awajen, Nawaf yaďago ido yana kallonta, ahankali ya furta 'karaso mana.
   Tayi shiru kamar bazata zoba, sai kuma ta tako ahankali zuwa kusadashi, tayi yin'kurin zama a 'kasa, Nawaf yari'ko hannunta da sauri, no karki zauna a'kasa fancy face, tashi yayi zaune yajawota saman cinyarsa.
    Taďan ďaga ido tana kallonsa da niyyar yin maga, ya watsa mata wani kallo dayasakata yin shiru, taďan lumshe idanunta ta buďe.
   Ya zame ďankwalin kanta yana faďin woow!!! Xarah na, amma kitsonnan yayi miki 'kyau, yazame ribomďin data ďaure kitson dashi, kitson ya watsu ahannunsa, yakama jelar yana wasa da'ita, cikin kunnenta ya ce, "dolene nabiya mai kitsonnan na musamman.
   Yasmeen taďan ta6e baki, yakai hannu yana shafa la66anta kinsanfa banason ta6 e baki ko??, ko kinaso mukoma 'yar gidan jiyane?.
    Yasmeen tayi shiru dan ita tana neman hanyar dazata tanbayeshi zuwa abujane.
   Yaďan girgizata kaďan, taďago da sauri tana kallonsa, ya sumbaci goshinta yana faďin miye matsalar fancy face!, yasmeen ta lumshe idanu, idan nagaya maka zakamin maganinta, yaďanyi jim sannan ya ce, "indai batafi 'karfinaba zanyi.
    Ta gyara zama ajikinsa tareda kwantar dakanta saman kirjinsa ahankali ya lumshe idanu tareda kara rungumota sosai,, ta ce, "dan ALLAH kabarni nabisu momcy abuja gobe idan ALLAH yakaimu.
   Da sauri Nawaf yabuďe idanu, shifa azatonsa zata bashi hakurine tace kuma tana sonsa, amma saiyaji sa6anin haka, yayi shiru kamar baijitaba, taďan ďago idanu tana kallonsa, suka tsurama juna idanu.
    Kallon juna suke cikeda so da 'kauna, ahankali Nawaf yafirta i luv u xarah, i luv u so very much ya rungumeta tsam a'kirjinsa yana hawaye,, cikin kunnenta ya ce, "plz & plz xarah, dan ALLAH kisoni, ki manta da abinda yafaru baya, mu ďauka munyi kuskure, wlhy zarah ina tsananin 'kaunarki, tun farko kena fara so, tun aranda nafa ganinki akan titi cikin gosilo naji nakamu da 'kaunarki, nima kisoni xarah karkice ba'kya sona, idan kika furta haka akwai matsala.
      Ahankali yasmeen taďago tasaka hannuwanta tana sharema Nawaf hawaye, itama kukan takeyi, dan haka shima yasa hannu yana share mata nata, ta lumshe ido sanan ta ce, i luv u too my man!! nima ina 'kaunarka wlhy mijina, dama kaine nake kokwanton hakan daga gareka, plz kaci gaba da 'kaunata harmu koma ga ALLAH.
   Nawaf daketa faman murmushi yay saurin haďe bakinsa da nata, wata zazzafar sumba yake bata, itama saita bada kai bori yahau lol............








©2017



bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
         luv u oll my fan's
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *