check your best novels here

Wednesday 1 March 2017

NAWAFF!!! 31 to 34

[26/02 13:31] ‬: ☆☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF  
☆☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page31 & 32

.....koda yasmeen tafita zamanta tayi a waje, tanajin motsin fitowar Nawaf ta samu wani lungu ta 6uya, 6angaren momcy yanufa tasan zaije gaishesune, ďaki takoma ta ďakko hijjab itama, tana shirin shiga yana fitowa, tamatsa masa ya wuce batareda kowa ya kalli ďan uwansaba, yasmeen ta ta6e baki tareda shigewa.
   Shima mota yashiga ya bar gidan.
   Yasmeen zamanta tayi a 6angaren momcy har azuhur, sanan tadawo nasu 6angaren, har sanan Nawaf bai dawoba, tayi sallah ta sake wanka, falo tadawo ta zauna zuciyarta cike da tunani, yau kwana uku ke nan kullum sai faisal ya kirata, amma bata ďagawa, gsky tana fargabar Nawaf yagani, da sauri ta ďago domin jin sallamar ameena..
  Taje ta rungumeta cikin tsananin farin ciki, Ameena ta ce, "kai yasmeen irin wannan 'kyawu haka, miye sirrin??.
   Yasmeen ta ajiye kayan hannunta tana hararar Ameena, 'yar duniya abinma harda zagi, aii kobaki faďaba kowa yaganki yasan kina jin daďi, kodai oga mas'ud yayi ajiyane??.
   Dariya Ameena tayi tareda shan lemon da yasmeen ta kawo mata, ta ce, "kin rama kenan??.
    Dariya sukayi suduka.
   Yasmeen ta ce, " 'yar uwa inatason shigowa wajenki amma ina tsoron na tambaya a hanani, ya amarci??.
   Ameena tayi far da idanu ta ce, "amarci muna ci kam, kamar yanda nasan kuma kuna shan naku.
   Yasmeen tayi murmushin takaici, ta ce, "k ni babu wani amarcin dana keci saima shan wahala, amma ba wannan bane mafi girman damuwata amina!.
   Ameena ta gyara zama, yasmeen miye damuwarki???, humm amina faisal ne damuwata.
   Ameena ta 6ata fuska tana hararar yasmeen, "k yasmeen kiji tsoron ALLAH wai da baki so faisal ba sai yanzu dakike agidan mijinki, karfa ki manta mijinki yafi faisal komai wlhy 'kyau aji ilimi wayewa, dan iskanci da shaye2 bashi bane wayewa.
   Yasmeen ta kamo hannun Ameena ta matse anata, Ameena ki saurareni nakai 'karahen zancena mana, kema kinsan bazan ta6a son faisal ba arayuwata, baki bari nafaďi abinda ke raina bane.
   Abinda yasa kikaji na ce, "miki faisal ne damuwata shine, yau tsawon kwana uku kenan kulum sai faisal ya kirani, gashi yay ta turomin sakwanni, shiyyasa ma kwana biyu na daina chatting kwata2.
  Ameena ina tsoron mugun nan ya gane, na tabbata bazai ta6a fahimtata ba.
   Ameena ta ce, "tofa, ba ance tun randa faisal yazo gidanku da safennanba washe gari yabar 'kasar??, nimadai haka naji, amma fa number dayake kirana da ita ta 9ja ce.
    Ameena taja numfashi, ta buďe baki da nufin yin magana.......sai Nawaf da mas'ud sukai sallama, dole suka katse hirar tasu.
    Su Nawaf suka zauna, mas'ud ya ce, "tunda ku kun'ki zuwa mu gashi yau munzo mu kwashe ladan.
   Yasmeen da Nawaf sukayi dariya, yasmeen ta ce, "ayi ha'kuri muma zamuzo, Nawaf ya ce, "kinga ishirunki, ranar aii saida naje gidan, shiko tunda aka gama biki bai zoba, saboda santin amarci, ranar har momcy daida ta tambayeshi.
  Mas'ud ya zaro ido kai da gsk kakeyi.
   Nawaf yay dariya yana faďin eh mana.
   Nandai sukaita hirarsu, har la'asar, mas'ud ya ce, "Ameena ta tashi su tafi, dole tabi umarnin mijinta, amma badan tasoba, dan tanaso su 'kare maganar da suka fara da yasmeen.
   To itama yasmeen ďin taso hakan amma bayanda zatayi.
  Har get ta rakasu sanan ta dawo dan harda Nawaf suka fita, tunda lokacin sallah yayi.

_________________________________   haka rayuwa taci gaba da tafiya, yau da gobe sai ALLAH, Nawaf yanata shirya musu tafiya katsina, amma dan rainin hankali bai sanar da yasmeen ba, tagadai yanata sayo abubuwa yana ajiyewa, itako ko kallo bai ishetaba bare ta tambaya.
   Dan yanzu ba sosai suke shiga harkar juna ba.
   Yau su duka suna falo amma babu wanda yadamu da abinda ďan uwansa yakeyi, yasmeen tana zaune akasa ta shinmiďa farin hankici ta ďora 'kafarta akai tana yanke farce.
   Nawaf kuma yana kwance saman doguwar kujera yana kallon kwallo.
   Wayar yasmeen tashiga 6urari, takai dubanta ga wayar faisal ne, cikin rashin gsky ta kalli Nawaf, idanunsa suna kan tv amma hankalinsa yana kanta, ta gefen ido yake kallonta.
  Ta kauda ido daga kallonsa alokacin wayar ta tsinke, cigaba tayi da yanke 'kumbarta.
  Aka 'kara kiran wayar nanma harta tsinke bata motsaba, shikuma kuma yaci gaba da kira, saida yakira sau 6 ana bakwaine yasmeen takai hannu zata ďauka, da sauri Nawaf ya kawo hannu shima da nufin ďauka, saiya dafe hannun yasmeen.
   Suka ďago lokaci ďaya suna kallon juna, har wayar ta tsinke basu saniba, kallo sukema juna mai cike da 'kauna, Nawaf yafara janye idanunsa saboda sake kiran wayar da akayi.
   Yasmeen ta sake danne wayar sosai da hannunta, cikin zafin nama Nawaf ya cire hannunta, ya tsaida kallonsa ga mai kiran wayar FAISAL!!!!, ya maimaita sunan ahankali, ďaukar wayar yayi ya koma saman kujera.
   Yayinda yasmeen tayi mutuwar zaune, kiran faisal yayi, jikin faisal yana 6ari ya ďaga azatonsa yasmeen ce, NAWAF yay shiru batareda yayi maganaba.
   Faisal ya ce, "my luv plz kizo gareni, idan ba hakaba zan iya mutuwa, ina nan kwance tsawon satu uku babu lafiya, ki taimaka kizo na ganki my luv!!!.... Nawaf ya rintse idanunsa, danjin 'katon banza yana kiran matarsa my luv!!,  wata razananniyar tsawa ya dakawa faisal.
   Kaiiiiiiiiiii!!!, wawa jaki jahili, wlhy ka sake kiran matata my luv saina kasheka dan ubanka, kai wane irin jakine zaka rin'ka kiran matar aure jahilin banza!!!!,  wlhy daga yau yazama na 'karshe dazaka sake kiranta, inko ba hakaba zakayi dana sani kaida jahilan iyayen ka, yana gama faďa ya yanke wayar.
   Kwala wayar yayi da bango aiko ta ta rarratse, yatashi yanufi wayar kamar wani mayun wacin zaki, yasmeen ta rintse idanunta azotonta wajenta yanufo saitaga ya wuceta.
   Yasa 'kafa ya take waya ya 'kara takata, sannan ya buďe ya cire sim cart ďin ya karya shi, itadai yasmeen sai jikinta yake 6ari.
   Yana gamawa ya dawo kanta ta rungume jikinta tana kuka, gashin kanta ya dam'ke ahannunsa ya fisga da 'karfi, tari'ke hannunsa tana kuka, idanunsa sunyi jajur saboda 6acin rai.
   Cikin muryarsa tamakar zaiyi kuka ya ce, "ya ce, "kin cuceni kina gidana kina soyayya da wani, ke wacce iri jahila ce???.
   Cikin 6acin rai yasmeen ta ce, "ka daina ce mini jahila, danni ban aikata abinda kake zargina dashiba???, dan haka ka sakar mini gashi.
   Yakuma murďe gashin tareda wanka mata mari, cikin 'karaji ya ce, "idan ba haka bane uban mi yasa yake kiranki, ubanmiye a tsakaninki dashi, wlhy zan iya kasheki shima na kasheki, sannan na kashe kaina.
   Yasmeen ta fashe da kuka,  tana faďin ka kasheni ALLAH yasani gsky na faďa maka.
   Ahankali ya saki gashinta yana cije baki, yakoma 'kasa ya zauna da6as kamar ďan bori, kai ya dafe yana jujjuyawa, yashiga hargitsa sumar kansa tamkar mai ciwon hauka.
   Yasmeen ta tsura masa idanu tana hawaye, ga tsoro fal cikinta  dan ganin yanda Nawaf keta jujjuya kai kamar ďan kwaya.
   Sunkai awa biyu ahaka kowa yana jinyar kansa, daga baya Nawaf ya shige bedroom, kaitsaye bathroom ya wuce, shawa ya sakarma kansa, batareda yacire kayan jikinsaba, yakai minti30 ahaka, saidaga baya yay wanka ya fito, shiryawa yay cikin 'kananun kaya, ya fito.
   Har yanzu yasmeen tana gurin daya barta tana kuka, ko kallon inda take baiyiba ya fice.
  Ahankali ta tashi taje tayi wanka itama, tayi sallah ta kwanta, wani wahalallen zazza6i ya rufeta, gado ta haye ta kwanta tana rawar sanyi.
       Har dare Nawaf bai dawoba zuwa sanan yasmeen ta gama gala baita, duk abunnan da yake faruwa Nawaf yana 6an garen momcy yana hirarsa, dan yarage 6acin rai. 
   Momcy ta ce, "wai ina ďiyata??? modebbo, Nawaf ya ce, "tanaca karatu takeyi shiyyasa kikaga bata zoba.
   Okey aii nazata ko batada lafiya, A'a lafiyarta 'kalau.
   Sai 'karfe tara yakoma 6angarensu, bedroom ya wuce ya kai kallonsa ga yasmeen dake saman gado 'kudun dune a bargo, ya đaukr kansa daga kallonta, cigaba yayi dayin harkokinsa, yagama  komai na al'adar rayuwarsa.
   Yay tsaye abakin gadon yana faďin ke wai mikike nufi da kwanciya a gado, kinsandai bazan kwanta saman kujeraba ko??.
   Jin tayi banza dashi yasa kai hannunsa ya yaye bargon, wani hucin zafi ya dakeshi, yay sagare yana kallonta, zama yayi abakin gadon yakai hannu ahankali saman wuyanta, idanunsa ya runtse tareda fitar da huci mai zafi.
   Baisan sanda yakai hannu yana shafa gashintaba ahankali, ta buďe ido tana kallonsa, da sauri ta tashi zaune tana jujjuya ido.
   Ya gimtse fuska yana faďin mike damunki, cikin rawar murya ta ce, "zazza6i.
  Mi'kewa yayi batareda yayi magana ba, ya buďe durowar gefen gadon ya ďakko magani harya mi'ka mata saikuma ya janye hannunsa yana faďin kunci abinci??.
  Ta girgiza kai alamar A'a, maganin ya mayar ya fita, babu daďewa yadawo hannunsa ďauke da kofin shayi, ya mi'ka mata, yatsine fuska tayi tana faďin nifa na'koshi.
   Batareda yayi magana ba ya zauna kusada ita, yaja filo yajingina mata ajikin gado, kamata yayi ya jinginata da filon, itadai sai kallon ikon ALLAH takeyi, kofin yasaka mata abaki, dole ta buďe bakin ta kur6a, haka yayta bata tana sha, amma babu magana tamkar wasu kurame.
   Saida tasha rabi sanan ta ce, "na'koshi, harararta yayi ya ce, "kar6a bana son yawan magana.
   Kar6a tacigaba dayi harta shanye tas, sanan ya ďako maganin yabata, ta yatsine fuska kamar zatayi kuka dan bata son magani.
   Ya 'kara ďaure fuska, "k ni ki kar6a kona tashi na kwanta dan barci nakeji, tana hawaye ta kar6a ta shanye tana rintse idanu.
   Tana gama sha tafara yun 'kurin amai, da sauri ya rungumota zuwa jikinsa yana shafa bayanta kamar wata jaririya, saida aman ya lafa sanan ya ďagota yana faďin kin daina jin aman ko??.
   Kai ta kaďa masa.
   Ya gyara mata kwanciya ya lullu6eta da bargon, dandanan barci yay gaba da ita, shikuma yakoma saman kujera ya kwanta, aiko yadaďe baiyi barciba.
   Nima na lalla6o na firo.
_________________________________ da asuba tunda yafita bai dawoba sai wajen 'karfe 7:30am tare suka shigo da mas'ud, zuwa sanan  masu aiki sun gama gyara gidan tsaf, ita kuma tana kichin tana haďa break.
   Yashiga bedroom bata nan ya fito yana faďar kaga yarinyarnan ko yanzu haka tana wajen su momcy.
   Mas'ud ya ce, "A'a, kadai duba kichin naji kamar motsi.
   Nawaf yanufi kichin batareda yayi magana ba, bakin 'kofa ya tsaya yana kallonta saidai fuskarsa babu walwala, da sauri ta juyo danjin tamkar mutum abayanta.
   Karaf suka haďa ido da Nawaf ta kauda kai daga kallonsa, ya ce, "keda bakida lafiya miye nawaniyin girki.
   Kanta a'kasa ta ce, "aii naji sau'ki.
   Ya ďan ta6e baki, wannan ba hujja bace, ki sauke abinda kika ďora kizo ga mas'ud yazo zai dubaki, yana gama faďa yafice.
   Ta sauke abinda ta ďora dama ya nuna, falo tafito, ta gaida mas'ud, ya amsa tareda tambayarta ya jikin??, ta ce, "da sau'ki.
   Tambayoyi yay mata tana bashi amsa yana rubutawa, bayan ya gama ya ce, "bari naje zuwa anjima zan kawo miki magunguna, ta ce, "to, ka gaishemini da Ameenar, yafita yana faďin zataji.
  Kichin ta koma bayan fitarsu, dan tare suka fita da Nawaf.
   Mas'ud ya kalli Nawaf ya ce, "mutumina gsky yasmeen tana cikin damuwa, dan damuwarce ta haddasa mata zazza6in.
   Nawaf ya ce, "badole damuwa tasa ta zazza6iba tunda gangar jikinta ce a gidana zuciyarta tana wajen tsohon mijinta.
   Cikin mamaki Mas'ud ya ce, "ban ganeba,  Nawaf ya zayyana masa duk abinda ya faru jiya.
   Mas'ud ya ce, "bawai ban yarda bane, amma yakamata ka sake yin bincike, danni amina tabani labarin komai.
  Nawaf yay shiru baice komaiba, mas'ud ya ce, "bari nawuce saina dawo.
   Sanda Nawaf yadawo yasmeen tana wanka, ya zauna saman kujera yana jiran fitowarta, ta daďe abakin 'kofa tana tunanin yanda zata fito da tawul, kamar ance Nawaf ya juyo suka haďa ido da yasmeen da sauri ta koma cikin bayin.
   Ďan 'karami tsaki Nawaf yayi, tareda mi'kewa yanufi hanyar bayin, ahankali ya ce, "kifito ki shirya ni na koma falo, ki kuma shirya kayanki kala huďu dan zamuje anguwa, yana gama faďa yafice.
   Saida taji batajin motsinsa gaba ďaya sanan ta fito, agurguje ta shirya dan bataso yazo ya ritsata.
   Saida ya daidaici tagama sanan ya shigo, ya ce, "kin haďa kayan dana ce??, ta ce, "A'a, bayi yashige batareda ya sake maganaba.
   'Karamin akwatinta ta ďakko ta haďa kaya biyar da duk abinda zata bu'kata, tai sauri ta koma falo, taďanyi break kafin ya fito.
   Shima daya fito saiya shirya kayansa a ďan akwatinsa irin na maza, falo yafito ya isketa ya zauna yaci abinci, tana zaune a gefe tana kallonsa.
   Yagama tsaf yami'ke, ya ce, "tashi muje muyima su momcy sallama.
  Yasmeen ta ce, "azuciyarta wai wanan wace irin tafiya ce babu shiri???, na ce, "yasmeen yazakiyi, mulkin kenan aii.
    Sallama sukaiyima su momcy, anan takejin garin da zasuje, kafin Nawaf yagama tattaunawa da papa yasmeen tadawo ta gyagygyara abinda ya dace, sanana su talatu suka kaimata akwatinan wajen mota, saida suka jira mas'ud yakawo mata magungunan ta sanan, suka tafi su momcy suna ďaga musu hannu.
_________________________________ tunda suka fara tafiya babu wanda ya tankama wani, saida suka kusa fita kano sanan ya tsaya gidan mai, aka cika musu tankin mota taf, ya shigo suka ďauki hanya bayan yayi addu'oi, itadai nata ameen.
    Gudu Nawaf yashiga shararawa kamar zai tashi sama, cikin awa ďaya da rabi suka isa tsanyawa, fitsari ya 'kullema yasmeen mara amma takasa gayama Nawaf, saida suka ďauki hanyar katsina sanan Nawaf ya kalli Yasmeen, cikin ďaure fuska ya ce, "waike motse2n mi kikeyine haka??.
   Tayi 'kasa da kai tana faďin babu komai, ya ďauke kansa ya maida bisa titi, ahaka suka isa safana, harta fara murna sunzo, saitaga ya ďauki wata hanyar kuma, tun suna bin birji mai 'kyau har suka koma mai ramuka, yasmeen tagadai tafiyar bamai 'karewa ba ce, harta fara zargin kodai sayar da ita Nawaf zaiyi, ga azababben fitsari yana cinta, haka ta daure, suka wuce wani 'karamin 'kauye tazata nanne, amma saitaga sun wuce, saida suka wuce 'kananun 'kauyuka uku, sanan sukaje wani 'kyauye amma babban garine shi saidai shima 'kyauyene sosai.
    Tunda suka shigo garin yara ke binsu abaya suna faďin ga mota ga mota.
   Yasmeen ta ce, "tofa.
  Nawaf yanajinta yay mata banza.
    A'kofar wani gida suka tsaya, amma shi shafe yake da suminti, dukda ginin 'kasane, Nawaf yabuđe mota yafito batareda yayima yasmeen maganaba.
   Itama saita buďe ta fito, ya danna kai cikin gidan tabi bayansa.
    Suna shiga gidan aka taresu da murna, dan har yara sunkai labarin zuwansu, yasmeen ta ce, "ma wata 'yar buduwa dan ALLAH ina bayi yake 'kanwata, yarinyar ta ce, zona rakaki.
   Buta ta ďakko ta rakata, cikin hanzari yasmeen tashige, babu daďewa ta fito suka koma inda aka shimfiďa musu tabarma, a 6angaren wata 'yar tsohuwa.
    Sai asanan yasmeen ta lura da muta nen gidan suna kama dasu Nawaf musamman ma Abdallah dan shi yake kama da papa sosai.......................





Kuyi ha'kuri yau babu yawa,  ina busy ne.










©2016


bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
         luv u oll my fan's
[26/02 13:31] ‪: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page33 & 34

.....Gidan babbaban gidane, wanda za'a iya kira family house, saidai 6angare2 ne, wannan yasa yasmeen tagaza tattance adadin yawan muta nan gidan, dan danan aka cika musu gaba da nau'in kwanikan fura kala2.
    Gaishe2 aka fara da tambayar juna bayan rabuwa, amma sukan haďa da fulatanci, wanda Nawaf shima yana yarawa, lamarin yabama yasmeen mamaki, bata ta6a tunanin yanajin fulatanciba.
   Nawaf ya ce, "wai inasu baffa??, 'yar tsohuwa mai ran 'karfe ta ce, "suna gona, wasu kuma suna kasuwa.
   Ayya ALLAH yadawo mana dasu lafiya, amin saura suka faďa, bayan wani ďan lokaci kowa yafita yabarsu dansu ďan sha furar kafin a kammala abinci.
   Ita dai yasmeen bin kowa take da kallo, dan bata sansuba, tagadai wasu awajen bikinta, wasu kuma bata gane suba.
   Nawaf ya juyo yana kallonta, ya ce, "wannan ita ce, hajiya iya kakarmu kenan, kowa ya mutu yabarta, ya'karashe maganar da tsokana.
   Hajiya iya tayi masa da'kuwa, Nawafa kaci gidanku, kenan sokake na mutu.
   Nawaf da yasmeen suka tuntsure da dariya, cikin dariya ya ce, "nikam ba sunan Nawafa ba, shiyyasa saboda ke bana son zuwa garin nan.
   Aii dama ba zuwa kakeyiba, sa'idune kawai da umma (momcy)suke zuwa, saisu Abdu, amma kai basai ka haďa shekara biyu bamu gankaba.
   Nawaf ya tsaya da dariya ya ce, "bahaka bane hajiya iya, niďin nan dakike gani nafi kowa son garinnan, kawaidai yanayin sana'a tace haka, amma kiyi ha 'kuri tunda yanzu nayi amarya zan runga zuwa ganin uwargida sosai.
   Yakamata kam, dan babu abinda yafi zumunci daďi, shiyyasa nakeson sa'idu fiye da kowa acikin 'ya'yan gidanan, tafaďa tana bubbuďe kwanukan da matan gidan suka tara, ko ina furace da tasha damu da nono mai 'kyau, hajiya iya ta ri'ke baki, to su waďanan ina suke nufin zakukai wanan uwar hura haka sakace masu cikin zani.
    Nawaf ya ce, "karki damu duk zamu iya shanyewa kinsanni da son fura.
   Tami'ke da 'yar sandarta tana faďin to saiku bada himma, kishiya kisha dayawa ďanyar fata bata fashewa.
   A'a hajiya iya, sokike cikin matata ya fashe, nazama naki ke kaďai.
   Hajiya iya tafita tana faďin ďan nema mizanyi da ďan ta maula.
   Bayan fitarta yasmeen ta ce, wai kana nufin wannan itace ta haifi papa?.
   Nawaf ya girgiza kai, wanan kishiyar kakarmu ce, duk yawan matan nan dakike gani daga matan 'ya'yanta sai na jikokinta, kakarmu papa kawai ta haifa, ALLAH yay mata rasuwa tuni itada kakanmu.
   ALLAH sarki yasmeen tafaďa, ALLAH yagafarta musu sukuma.
   A la66ansa ya amsa da ameen.
   Yami'ke yana faďin bari naje nayi sallah lokaci yayi.
   Yafice yasmeen tana binsa da kallo.
  Bayan dawowarsa sukaci abinci, zuwa sanan mazan gidan sun fara dawowa, kowa yagansu saiyayi farin ciki da zuwansu, dan sunsan yau sun warke.
   Zuwa dare Nawaf ya dam'kawa kowa tsarabarsa, sai murna da godiya sukeyi, har makwafta suma an kakkai musu.
   Nawaf yana 'kofar gida cikin danginsa anata hira da wasa da dariya, dan kokaďan baya 'kyamarsu, yanason danginsa sosai, ya kira musu papa a waya sukasha hira, sai wajen karfe tara suka shigo kowa yanufi ďakin matarsa.
   Yasmeen ma harta fara barci a ďakin hajiya iya, Nawaf yashigo da sallama hajiya iya dake gyangyaďi ta buďe ido, Nawafa ina kashiga kabar yarinya ita kaďai ga gajiya ga ba'kunta, baywar ALLAH harma ta fara barci anan.
   Nawaf ya ce, "hajiya iya aii anan zata kwana dama, miyasa bataje wajensu kuluwa tayi hiraba?, A'a ni ce, "na hanata dan naga tagaji wannan garin naku mai nisan tsiya.
   To shike nan ni bari naje na kwanta, sai da safe.
   Kaga dawo ka tada ita, saitafi sakewa acan, anan aii takura zatayi, dan yaran su hanne fitsarin kwance sukeyi, kuma anan suke kwana, dan haka tada ita kuje can, itama zatafi jin daďi aii.
   Batare da ya ce, "komai ba, yashiga kiran yasmeen! Yasmeen!!, ahankali ta buďe adanunta, danji take lamarin kamar amafarki, yauce rana tafarko dataji ya kira cikakken sunanta, amma "k shine sunan dayake kiran ta dashi, koyace mara kunya.
   Ya ce, "tashi mana, tami'ke tana murza idanu, hajiya iya ta ce, "bita ahankali mana, saida safenku, nasa salmanu yakai muku kayanku tun ďazu.
   Nawaf ya ce, "to saida safe, yay gaba yasmeen tabishi abaya tana tangaďi, ahanya tayi karo da bishshiya dalbejiya, Nawaf ya ri'ke hannunta yana faďin waike idan kina barci saiki zama tamkar 'yar kwaya??.   
    Itadai batace masa komaiba saima 'kara matse hannunsa datayi cikin nata.
   Wani 6angare suka shiga agefe da alama shine 6angaren papa, idan kuma sunzo nan suke sauka.
  Ďaki ďaya yanufa, wanda aka kunnawa fitilar kwai, 'katuwar katiface aďakin, dan haka suna shiga yasmeen ta kwace hannunta ta kwanta, dan barci takeji sosai.
   Nawaf ya girgiza kai, yana faďin yarinya kamar 'yar kwaya?, ya canja kayansa zuwa na barci, "k kitashi ki cire waďannan kayan mana!.
   Yasmeen ta gyara kwanciyarta dan ALLAH kabarni ALLAH na gaji barci nakeji, tsaki yayi ya ce, "dallah ca akayi kitashi ki cire waďan nan kayan, yasmeen ta tashi tana murza idanu, ya hawo katifar ya kwanta, yana mita, zaki wani ishi mutane da faďin kin gaji to waye bai gajiba?, nida nakawo mu nan bance nagajiba saike!!.
   Banza tayi masa, tasaka hannu ta kashe fitilar kwan dakeci.
   Nawaf ya ce, "wane irin iskanci?, ne wanan zaki kashema mutane fitila?, saida ta murguďa baki kamar yana ganinta, ta ce, "to kaya zan cire.
   Tsaki yaja yakoma ya kwanta, aikin banza ubanmiye abin kallo ajikinki dazaki wani rainama mutane wayo, ya 'kare maganar da kwafa, kyaaaaaak!!!
   Yasmeen ta ce, "oho dai nidai baza kayi daniba agidan mutane, shiru yayi kamar bai jiba.
   Tagama shiryawa tai tsaye tana tunanin inda zata kwanta, dan bazata haďa makwanci da 'katoba, ta ce, "kabani bargon na shinfiďa a'kasa na kwanta.
   Ya ce, "zoki kwata mana.
  Shiru tayi bata tankaba, azatonsa ta kwanta a'kasane, yaďauki wayarsa ya kunna fitila, saiya ganta gefensa tsaye jingine da bango, ya ta6e baki yakashe fitilar ya juya mata baya.
    Ta saka hannu da niyyar yaye bargon, caraf ya dam'ke hannunta, ya mirďe, ta kwalla 'kara, ya fincikota ta faďo jikinsa.
   Ya ce, "ni wai sa'ankine??.
    Tai masa shiru tana hawaye, fitilar wayarsa yasake kunnawa, ya haske mata idanu, ta rintse idanunta kam.
   Ya ce, "matsoraciyar banza, nizaki yayema bargo, ta ce, "nifa ba ďauka zanyiba, ya ce, "to mizakiya.
   To kasakeni basai na gaya makaba., ya ce, faďi ahaka mana.
   ALLAH zan cijeka idan baka sakar mini hannuba,, hhhh yaro man kaza, ki cijeni mana, aii kinsan halina sarai.
   Shiru tayi masa, gata ajikinsa ga hannunta amurďe, damma yau bai murďeba sosai, ganin bashida niyyar sakinta saikawai ta maida kanta saman 'kirjinsa ta kwanta, dan barci takeji.
   Nawaf ya lumshe idanu tareda sakin sassanyar ajiyar zuciya, yasmeen tana jinsa.
   Ahankali ya janyeta daga jikinsa, dan yanda yakejinsa  ďinnan zai iya aikata mata aika2 wlhy.
   Kwanciyarta yagyara tacigaba da barci abinta.
   Ya haska fuskarta yana murmushi, wanda shi kansa baisan na miyeba, dahaka barci yay awon gaba dashi shima.

WASHE GARI 
     da safe hayaniyar yara ta tada ita, tunda tayi sallar asuba takoma barci, shima Nawaf tundaga sallah bai dawoba, ta tashi ta share wajen, sai asanan taga tsarin wajen, yanada girma babu laifi, akwai ciki da falo sai ďakuna ďai2 guda uku, sai kichin da bayi, ginine dai irinna 'kauye, amma shafe yake da sumunti kamar ko ina agidan.
    Tayi wanka ta shirya tsaf cikin les tayi 'kyau.
    Tana shirin fita Nawaf yashigo ya bita da kallo yana faďin sai ina??, ta ya tsine fuska, zanje nagaida su hajiya iya ne!, ya ce, "to sarkin zumuďi, aidai 'kya jira na dawo ko??, itadai batace masa komaiba.
   Ya shiga ciki batareda yasake tanka mataba, dole ta biyoshi, amma sai tayi zamanta awaje, tana nan zaune yafito dagashi sai tawul, da sauri ta kauda kai, shima saiya ta6e baki yawuce.
   Koda yafito baibi takantaba yashiga yashirya tsaf cikin 'kananun kaya, harda jibga rigar sanyi mai'kyau dan garin anaďan sanyi, yafito batareda yayi maganaba ya nufi hanyar fita, itama saita mi'ke ta take masa baya.
    6angaren baffa sunusi suka fara zuwa, bayan sun gaishesu ya ce, "nanane 6angaren baffa sunusu, shida iyalinsa, shine yake bima papa.
   Sanan sai 6angaren baffa lurwanu, sai 6angaren baffa Ďahiru, sai 6angaren baffa haruna.
   Sanan yakaita wajen 'ya'yansu kowa da matarsa, daganan suka koma wajen hajiya iya.
  Suka gaisheta, ta ce, "aiida yanzu zanzo na tasoku, sukayi dariya suna faďin aigamu mun tashi, nan yaran suka fara shishshigowa, yasmeen tana tambayar sunayensu.
   Nawaf ya ce, "ashe zaki gaji, dan koni bansan yawan adadin yaran gidannan ba wlhy.
   Saida suka karya sannan Nawaf ya ce, "zasuje su gaida dangi, daga nan har wasu 'yan 'kyauyika dake kusa zasuje.
   Zaikai yasmeen taga dangi.
  Hajiya iya ta ce, "tozata iya kuwa, dan kasan mota bata shiga.
   Ya ce, "karki damu hajiya, itama aii ba'kyauyarce zata iya.
   Yasmeen ta harareshi, shima ya rama.
   Cikin gari suka fara zagawa gidajen dangi, duk inda sukayi sai kallonsu akeyi,, garin ya burge yasmeen, ta ce, "kai garinku ya haďu gsky, wlhy kamar karna tafi.
   Murmushi Nawaf yayi batareda ya ce, "komaiba.
  Bayan sun gama zaga gari, Nawaf ya 'kar6i mashin ďin salmanu ya ce, "yasmeen tahau.
   Tsyawa tayi tana kallonsa, ya ce, "k nifa kina 6ata min lokaci, cikin marairaicewa ta ce, "wlhy tsoro nakeji, kaje ka kadani abanza.
    Nawaf yaďan murmusa, 'yar rainin hankali mikika maidani??, yarinya ni tausayinki naji dan wlhy kafin mu dawo kin galabaita, kuma sonake muje ko ina yau, dan gobe zamu koma safana, dan haka idan kinga zaki hau ki hau.
   Jiki a sanyaye ta kama mashin zata hau saida ta rirri'keshi sanan ta iya hawa, ya tada mashin suka tafi.
   Aikuwa da gskyar Nawaf, tabbas da a'kafa sukazo dataji jiki, ammafa atsorace take bisa mashin ďin, bata san lokacin datasaka hannunta biyu tai masa zobeba, ta kwantar da kanta abayansa.
   Ahaka suka isa wani 'kauye, Nawaf yatsaya awani 'kofar gida na jar 'kasa,, ya ce, "to ba'kauya sauka, kinbi kin wani 'kan'kameni, kinsa sai kallonmu akeyi.
   Ta sakeshi ta sakko tana faďin, wlhy suyita kallo, ai babu wanda yasanni, da asara gara gidadanci.
   Yakafe mashin ďin yana dariya, to ke idan kin faďi wayayi asarar.
   Ta ce, mutane dayawa kuma harda kai aciki wlhy.
   Kai haba ALLAH yakiyaye, ni aii narabu da 'kayama".
   Tsaki yasmeen tayi, ta ce, "aikai kafi 'kayarma.
   Gaba yayi yana faďin idan mun koma gida zaki maimaita.
   Suka shiga gidan da sallama, wata dattijuwa ta ďago tana amsawa da fara'arta, ta ce, "wanake gani kamar Nawaf, Nawaf yay 'yar dariya nine kuwa inna, kai lale daku, sannu dazuwa kinji ďiyata.
   Yasmeen ta amsa da 'yauwa, inna ta kwala kiran dijengala!!, wadda aka kira dijangala ta amsa tana le'kowa.
  Inna ta ce, "kawo tabarma maza.
  To tafaďa tana komawa cikin ďakin, sabuwar tabarma dijangala tazo ta shinfiďa, tana faďin yaya na birni sannu da zuwa. 
   Nawaf ya ce, "yauwa dijengala ya garin??, ta ce, "gashinan 'kalau, ta ce, "sannu amaryar yaya, yasmeen ma ta amsa tana murmushi, bayan tagama suka zauna, aka shiga gaishe2, da tambayar juna bayan rabuwa.
  Dijangala ta kawo musu ruwa, itadai yaameen sai kallonsu takeyi, dan ganin yanda suketa zabga sururutu, misamman ma dijangala, dan ita adole son Nawaf takeyi, shiyyasama ta'ki aure, tun abin yana burge yasmeen haryakoma bata haushi.
    Babu kunya dijangala ta ce, "yaya na birni nimafa nagaji da zaman nan gsky, Nawaf ya ce, "tokiyi aure mana, baga su sa'a nan ba harsun haihu, kuma kin girmesu.
   Tai far da idanu, to ai kasan kainake jira ko??, wata bazawarar dariya Nawaf yayi, ya ce, "yarinya kin ďakko dala babu gammo, bakiga matata tafiki 'kyauba, kuma ni mijin ta cene.
   Dijangala ta rage fara'a, dan tadaďe tana nunama Nawaf tana sonsa, amma saiya maida abin wasa, dayake abokan wasa suke.
   Nawaf ya katse mata tunani dafaďin inna kinji wani ďigimi wajen dijangala, ko inani ina auren baiwata?.
   Inna habi ta ce, "aii komai na ALLAH ne, (WAYASAN GOBE??,)    Nawaf ya ďan ta6e baki dan yasan itama innar duk jirgi ďaya ya kwasosu da 'yar tata, ya ce, "sai ALLAH, amma yakama ku aurar da dijangala kafin tarasa miji a 'kauyenana wlhy.
   Dijangala ta ďaure fuska tamau kamar zatayi kuka, agaban matarsa yake gaya mata haka saboda wula'kanci.
    Itama ran inna habi ya 6aci, jitake kamar ta doke Nawaf, dan itama tana fata dijangala ta auri Nawaf kodansu 'kara hutawa.
   Nawaf ya kalli yasmeen data cika tayi fam kamar zata fashe saboda kishi, shi dariyama ta bashi, amma saiya gimtse ya ce, " 'yammata tashi muje munada sauran gurin zuwa.
   Yasmeen tami'ke tana zuzzun6ura baki, sukayi musu sallama suka fito, bayan Nawaf ya ajiye musu kuďi da tsaraba.
   Amma ko godiya basu yimasaba, shima bai damuba, dan hakan yafi sau'ki, inashi ina wannan kucakar yarinyar mai kamada 'yar bori.
    Koda suka fito yasmeen sai wani shan 'kamshi takeyi, Nawaf ya ce, "yammata tunkan nayi auren har kin fara nuna kishi??.
    Yasmeen ta murguďa baki tana harararsa ta ce, "ALLAH ya kiyaye, miye abin kishi awurinka, ai abinda kakeso kakeyima kishi.
    Dariya Nawaf yayi yana faďin aii kuma kin makaro yarinya, fuskarki ta nuna sirrin zuciyarki, dan haka babu abinda zaki faďa na yarda.
   Tsaki yasmeen tayi tana faďin matsalarkace dai.
   Yahau mashin ďin yana faďin kokuma takiba, kina ba'kinciki nasamu amarya, aiko saidai ki fashe nanda wata shekarar za'a sha biki.
   Banza tayi masa ta haye mashinďin tana hawaye.
   Yanajin shashshekar kukanta, yayi murmushi kawai, azuciyarsa ya ce, "yarinya ta kamu.
   Haka sukaita zagaya dangi har yamma, sanan suka koma gida, aďakain hajiya iya suka yada zango, ta ce, "sannunku, kishiya kinsha yawo ko?, yasmeen tayi dariya tana faďin ai daďi, naga gari.
   Hajiya iya ta ce, "yayi 'kyau.
  Bayan magriba ta tafi 6angaren su kuluwa matar basiru, dayake duk sa annintane, saidai kowaccensu tanada yara uku zuwa huďu, idan ka gansu saika ďauka sun haifeta, yasmeen ta ce, "azuciyarta dayanzu nima haka nakoma a kwangwalan, kai ALLAH na gode maka.
   Hira tazauna sunayi, suna labarin bikinta da 'kauyancin dasukayi awajen anata tuntsura dariya, firera matar salmanu ta ce, "aini da akaje wajen dakuka saka waďan nan rigunan kamar aljanu, da hasken wajen ya haskani saina ruďe nashiga ďimuwa, saida basira ta taimaka mini.
   Gaba ďaya suka kwashe da riya, hira sukeyi sosai har wajen 'karfe tara, mazajensu suka fara shigowa gida, yasmeen tami'ke tana faďin bari naje na kwanta nima, wlhy duk nagaji.
    Tana tashi ta kwalla 'kara, ta zube awajen, cikin tashin hankali suka shiga tambayarta lafiya??.
    Ta ce, "wani abu ya cijeni a'kafa, wayyo ALLAHna, da sauri sha'aibu mijin barira ya haska, zuwa sanan Nawaf ya 'karaso waje danjin 'karar yasmeen.
   'Katuwar kunama suka gani ba'ki'k'kirin, ta tada bindi sama, sha'aibu ya ďauketa da hannunsa, ya kashe, Nawaf ya'karaso wajen yasmeen daketa zabga zufa.
   Ya ďagota zuwa jikinsa, ta ce, "modebbo ka taimakeni tafiya takemin, sai asanan kuluwa tai saurin cire ďankwalinta ta ďaura mata a'kafar.
   Nawaf ya rungumota zuwa jikinsa yana share mata zufar, yana faďin sannu kinji yi ha'kuri, salmanu yazo yasaka mata magani, sai sannu suke mata, aka zuba wani aruwa aka bata tasha, dandanan zufar ta 'karu,        salmanu ya ce, "yaya ka ďauketa kujecan zata faďi insha ALLAHUi.
     Nawaf ya ce, "to, cak ya ďauki yasmeen zuwa 6angarensu, suka rakasu da ALLAH ya kiyaye gaba.
     Saman katifa ya direta tanata zufa, ya ce, "sannu".
   Ta kaďa kai tana hawaye.
   Ya ce, "haryanzu tana miki yawon??, tace ba sosaiba amma.
    insha ALLAHU zata daina gaba ďaya, bari acire miki waďanan kayan kinga kinata zufa, batareda yajira amsartaba, yakama zip ďin ya sauke zuwa 'kasa, yasmeen ta rintse ido tana huci, yakama bra ďinta xai cire, da sauri tajuyo tana kallonsa, shima kallonta yakeyi, amma yaďan ďaure fuske, ya ce, "kafiya??".
   Cikin rawar murya ta ce, "plz kabarsa kawai, ya ta6e baki yana faďin keni bana son iyayi, bakida lafiyarma saikin jawo munyi, ko ba'kya ganin zufar dakikeyine??,.
   Ta ce, "to kafita zan cire da kaina nidai.
   Tsaki yayi saidai idan bazaki cireba kuwa, dan wlhy babu inda zanje.
  Ta ce, "to maidamini zip ďin rigata, tunda ni yaronkine ba, yafaďa yana kwanciya.
   Hijjabi ta jawo tasaka, sanan ta cire rigar, taja zaninta zuwa sama, yana kallonta tana ta zufa, ya ta6e baki, daga nan ya ďauki wayarsa yana danne2nsa, sai wajen karfe goma kunamar ta faďi, yasmeen ta mi'ke waizata tayi wanka.
    Nawaf yashiga tuntsura mata dariyar mugunta, cikin jin haushi ta ce, "malam lafiyarka kuwa??, Nawaf yacigaba da dariyarsa batareda ya kulataba, harta kai 'kofa zata fita, ya ce, "wlhy kije kiji'ka tadawo sabuwa, kezakai sha wahalarki ke kaďai, danni ficewata zanyi nabar miki ďakin wlhy.
   Ita sai yanzuma tatuna idan kunama ta harbeka ba'a saka ruwa, tadawo bakin katifar ta zauna ta rabga tagumi.
    Nawaf yacigaba da dariyarsa ta rainin hankali, itadai banza taimasa ta'ki kulasa.
   Yafara faďin modebbo ka taimakeni tafiya takemin.
   Tagane kwaykwayon muryarta yakeyi, dan haka ta harareshi tana murguďa baki, ya ce, "yarinya ashe zaki sake shan wata wahalar wlhy.
    Ta ce, "wlhy saidai musha, dan ba 'kyaleka zanyiba, yatashi daga kwanciyar dayayi, ya ce, "sake murguďa wannan bakin maikama da na tsintsaye kigani.
    Saida tazamo daga katifar sanan ta murguďa.
  Tami'ke da sauri, zata gudu, taku ďaya yayi ya dam'kota, yamaidata saman katifar, saman cikinta yahaye, yakama fuskarta da hannu biyu, ya haďe bakinsa da nata yashiga kissing ďinta.
    Itako sai mutsu2 take nason ta kwace amma takasa, gashi ya danne mata ciki, saida yayi mai isarsa sanan yasaketa yana maida numfashi, tabirkice zuwa rubda ciki tana kuka, tana tofar da yawu, 'kazami kawai, zakawani ta bani yawunka inasha, sai ALLAH yasaka mini wlhy.
   Kusada ita yakwanta, yadafa bayanta, 'yammata gobema ki 'kara yimini murguďa baki ki gani, saina miki abinda yafi haka, ya 'kare maganar yana dukan bayanta.
   Ta mirgina 'kasa tana cigaba da goge baki da hijjab, Nawaf kuma yana mata sassanyar dariya, yajuya ya kwanta yana murmushi wanda shi kansa baisan na miyeba, a hankali yafurta 'yar rigima.
     Saida taga yayi barci sanan tadawo saman katifar, takwanta agefe nesa dashi kamar yanda tayi jiya.
      Washe gari tunda safe saddiqu ya wankema Nawaf motarsa, zuwa 'karfe goma suka baro 'kauyen cike da kewar muta nan garin, masu kirki da karrama ba'ko, yasmeen harda hawaye.
   Suma 'kyauyen sun tafi sun barsu da kewarsu.
    A safana suka yada zango, gidan wani abokin papa, nanma sun zaga dangi, ananma yasmeen taga 'yammatan dasukaje bikinta dayawa, sunyi farincikin ganinta itama haka.
   Anan batare suka kwana da Nawaf ba, aďakin matar abokin papa ta kwana, shikuma ďakin ba'ki.
   Washe gari suka haďa inasu2 suka garzayo kano, cikeda uwar tsaraba, yasmeen takali Nawaf daketa wani ďaure fuska, ta ta6e baki tana faďin mutum tamkar mai aljanu, yanzu zaka gansa yana dariya, yanzu zai ďaure fuska kamar rundunar sojoji, har suka iso kano basa wata hirar arzi'ki, saidai ita dake tambayarsa sunayen garin dasuke wucewa, ada'kile yake bata amasa, itama daga baya saita kulle bakinta gam.
   Dahaka suka iso kano, cikin farinciki su momcy suka taresu, momcy ta ce, "ďiyata kinyi ba'ki wlhy, yasmeen tai murmushi tana sissine kai, hajja ta ce, "Nakuwa haďa muku abinci mai daďi na tarba, dan haka saiku shirya ci.
   Nawaf ya ce, "kai hajja da kanki, amma kinyi 'kokari.
   Ta ce, "nayi kewarkune shiyyasa.
Nawaf ya ce, "to mungode miki hajjarmu abin alfaharinmu.
   Yasmeen ta ce, "momy wai ina su Anwar???, suna islamiyya fateema, amma nasan suna hanyar dawowa, dan tun safe ake shirye2 dawowarku.
   Yasmeen tayi murmushi tana faďin ALLAH yadawo dasu lafiya...................



Assalamu alaikum 
Nagode da sakwanin gaisuwarku gareni, harma waďanda basu sami damaba,,,,, happy juma'at khareeeeem! !!!
    Luv u oll



©2016



bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        luv u oll my fan's
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *