check your best novels here

Tuesday 21 February 2017

NAWAFF!!! 13 to 17

[09/12/2016 16:04] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 13

.....A yaune aka kawo gagarumin lefen yasmeen, gsky su hajiya jummai sun taka rawar gani, dakaga lefen zakasan anyishine domin d'an gata.
   Tunda lefen ya iso yasmeen tashige d'aki tana kwasar kuka, dukkan mutan gidan idan ka kallesu zaka gano basa cikin walwala, saidai suna iya bakin k'ok'arinsu wajen yin fara'a koda iya ta hak'orice.
    Bayan masu kawo lefe sun tafi umma ta shiga d'akin yasmeen dan tasan tana cikin damuwa, cikin bargo ta tarar da ita kuwa tanata rawar sanyi da'alama bata cikin k'oshin lafiya.
    Cikin hanzari umma ta k'arasa gareta ta yaye bargo, wani irin zafi taji ajikin yasmeen ga rawar sanyi.
   Ba ab'ata lokaciba wajen kaita asibiti taga likita, da haka aka cigaba da hidimar biki, wanda gidansu faisalne kawai suke farinciki.
    A yaune kuma faisal ya diro k'asarsa ta haihu, iya yensa sunyi farinciki da ganinsa, babu abinda ya canja arayuwarsa sai lalacewa daya k'ara yi, saidai zamu iyacewa ya k'ara girma da wayewa mara amfani.
    Bayan ya huta da yamma ya aiki balarabe wai yaje ya d'akko masa yasmeen, lamarin yabama balarabe mamaki, ya za'ayi ace budurwa ce zatazo gidan saurayi???, haka dai yaja mota yatafi yana waswasi.
    Yaro yasamu ya aika saboda gidan yau akwai mata dayawa, anata hada2r biki.
   Yasmeen tafito dan taga wake kiranta, daka ganta zaka gano matsananciyar damuwar dake tare da ita.
   Takarasa wajen balarabe suka gaisa, ta ce, "balarabe wayake nemana.
   Ya ce, "dama ogane ya ce, "nazo nad'aukeki.
   kad'aukeni kuma??, to kakaini ina??.
   Wai na kaiki gidansu yanacan yana jiranki.
   Wata uwar harara ta sakarma balarabe kamar shine da laifin, ta ce, "kaje kasanar masa na ce, "bazan zoba, tana gama fad'a tashige gida.
    Balarabe baiga laifintaba dan hakan datayi shine dai2, ta burgeshi wlhy.
    Amma dayaje saiya cema faisal ya je bata gida, wai sunfita da k'awayenta.
   Hannu kawai yad'agama balarabe dan gsky yaso yasmeen tazo, wayarsa ya d'auka yakira wata number, ana d'agawa ya ce, "su had'u agidan daya nuna mata d'azu.
    Tashi yayi ya shirya ya d'auki makullin mota ya fice, kai tsaye gidanshi yanufa inda za'akai yasmeen, babu k'arya gidan ya had'u, anzuba komai amarya kawai ake jira, anan ya tarar da wata kod'ad'iyar mace wadda bilicin yayma k'awanya. lamarin yayi matuk'ar b'ata mini rai, lallai yasmeen taga takanta, dan nakula faisal bunsurune, inagama yasa ad'akko masa yasmeen d'inne  dan ya........hummm shege d'an iska.
   Tun afalo suka fara k'auce hanya, bak'in cikine yasani nabaro gidan dan bazan iya ganiba.

Haka biki yacigaba da gudana, yasmeen dai tak'i yarda faisal ya ganta, yabi duk hanyoyin dazai ganta amma ta rufe masa k'ofa, daga k'arshe abin ya b'ata masa rai ya tattarata ya watsar, dan yasan nanda wani d'an lokaci zata kasance agidansa dole, kuma duk wulak'ancin datake masa saiya rama.

NAWAFF
    a yaune Nawaff ya sauka Najeria saboda kwallo dazasu bugama Najeria, wanda yakasance na Africa, kuma Najeria itace mai masaukin bak'i.
   Mas'ud da Abdallah da Anwar ne sukaje tarbosa, sunyi farin cikin ganinsa, shima yayi farincikin ganinsu.
   Mas'ud ya ce bro's kudai ba'a ganinku saida dalili, turai ta kwace mana kai gaba d'aya.
   Nawaf yay dariya, su sun isa su kwace ni ahannunku, kawaidai nad'an lokacine, amma ni nakune.
   Abdallah ya ce, "yaya watanka 6 fa kenan da barin k'asarnan, yanzuma badan zakuyi wasannan ba dabazamu gankaba fa sai hutun k'arshen shekara.
    Nawaf yay murmushi kawai batarda ya ce komaiba.
   sunata hirarsu har suka isa gida, momcy ta tarbi Nawaf cikin farinciki, Nawaf ya narke murya cikin shagwab'a ya ce, "momcy nayi missing naku wlhy, ina papa ko yana wajen aiki ne??.
    Yana can momcy tafad'a, amma nasan yana hanyar dawowa,  yakamata kadaina shagwab'a haka nan modeebbo, kagirma fa.
    Su Anwar suka tuntsure da dariya, ya wurga musu harara, sannan yadawo da kallonsa wajen momcy ya ce, "momcy ni ban wani girmaba.
   Momcy ta shafa kansa tana dariya, ta ce, "ina mas'ud wai?, Nawaf ya ce, "ya koma asibiti, dan yace yanada aiki sosai.
   ALLAH sarki Mas'ud sarkin k'ok'ari kenan. momcy tafad'a.
    Nawaf ya mik'e momcyna barinaje nayi wanka jikina duk yayi tsami, to abincin fa?, mom sainayi wanka sannan, yanzu zan dawo, dan nayi missing d'in girkinki.
    Momcy tayi dariya to aii yau zakaci kamore.


YASMEEN.
   rana bata k'arya inji masu iya magana, yaudai aka d'aura auren faisal da yasmeen, d'aurin auren yatara manyan mutane masu fad'a aji ak'asarnan, saka makon babansa sanannen mutumne, kuma d'an siyasa.
   Sai dai abinda yabani mamaki duk d'unbin taron jama'ar nan babu ango awajen.
   Ana cikin shafa addu'ar k'atshe saiga faisal tamkar mahaukaci dagashi sai wando iya guywa da riga mara hannu, kutsa kai yake kawai cikin jama'a, har ya isa gabn liman, ya tsaya k'erere yana wurga idanunsa dasukayi jajur.
   Alhaji buba yamik"e da sauri yana tambayar d'an nasa lafiya???.
   Faisal ya yamutse fuska ta reda fad'in abba and'aura aurennan kuwa??.
   Alhaji buba ya ce, "emana faisal and'aura yanzu kazama ango.........hannu yad'aga wa mahaifinsa ya ce, "to abba awarwareshi yanzunnan.
   Alhaji buba yazaro idanu faisal kamarya a warware??, cikin k'araji faisal ya ce, "kamar yanda aka d'aura narantse da sarkin dake busamin numfashi bazan zauna da karuwaba, dan haka sai an warware shi.
   Gaba d'aya gurin yayi tsit ana kallon sarautar ubangiji.
  abin maganar dake hannun liman faisal ya kwace, yajuya yana kallon mutane, ya ce, "kamar yanda kuka shaida and'aura auren faisal da yasmeen, to haka nakeso ku shaida faisal ya saki yasmeen saki uku!!!!!!!!!!!!!!!!!.
    Gaba d'aya wajen akad'au "INNALILAHI WA INNA ILAIHIRRAJI'UN....................


Hummm nikaina dabana son wanga aure, saida na girgiza domin jin furicin faisal!!!.






Bilyn Abdul
   Mrs Abdus'salam
        LUV U OLL MY FAN's
[10/12/2016 09:30] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 14

.....Cikin b'acin rai Alhaji buba ya wankama faisal mari, faisal yadafe kumatu yana kallon baban nasa, mahaifin yasmeen kuwa fad'uwa yayi, dukda baya son auren abin yay masa matuk'ar ciwo.
   Gurin ya rud'e da surutai, kowa yana fad'ar albarkacin bakinsa, zuwa sannan an yayyafama abban yasmeen ruwa ya farfad'o, ya fashe da kuka yana fad'in yanzunan irin cin mutuncin daza ayimin kenan saboda anganni talaka, banida komai bani da kowa.
    Wani dattijo naga ya mik'e tareda dafa Abban yasmeen, ya ce, "kanada kowa malam, kuma ka kwantar da hankalinka, indai ka amince zan d'aurama d'ana aure da d'iyarka yanzunnan.
    Abba yabi dattijon da kallo, gsky ne dattijon mutumne mai kamala da dattako, yatabbata bazayayi dana sani da tayinsaba.
   Liman ya ce, "malam ka amince na tabbata bazaka tab'a dana sanin hakanba, Alhaji sa'eed mutumin kirkine, yakuma bama d'ansa cikkiyar tarbiya.
   Abban yasmeen ya ce, "shikenan nabashi!!, ALLAH yasa haka yafi alkairi.
   Liman da dattijo suka amsa da amin.
   Har mutane sun fara tafiya akayi sanarwa adawo za'a sake d'aura aure, mutane kam sun amsa kira, dandanan gurin yay tsit aka nutsu ana jiran mizaije yadawo.
   Nantake dattijo ya ajiye sadaki dubu hamsin, nakasa kunne naji dawa aka d"aura amma hayaniyar mata dake cikin gida yahanani, dole na hak'ura.
    Bayan angama d'aurin aure komai ya natsa, zuwa sannan labari yashiga cikin gida, dafarko umma taji bak'inciki, amma da'aka sanar da ita k'arshen al'amarin saitaji farinciki mara musali, nutsuwa da annashuwa suka bayyana saman fuskarta.
    Ammafa nakasa gano muku amarya bare nasan halin datake ciki.

GIDANSU NAWAFF.
    papa yashiga gidan fuskarsa cikeda fara'a, momcy ta taryeshi, bayan yasha ruwa ta ce, "Alhaji lfy dai naganka cikin farinciki haka??.
   Papa yay murmushi har wushiryarsa ta bayyana, ya ce, "ummul'khairi ina cikin farinciki yau, kuma kema idan kikaji nasan zaki tayani farin ciki, kamar yanda nagaya miki zanje d'aurin aure to daga can nake, bud'e kunnanki kisha labari.
   Momcy tayi dariya tareda fad'in ina sauraraenka Alhaji.
   Papa yagyara zama tareda zayyane mata abinda yafaru, yad'ora da fad'in wlhy mutumin yabani tausayi, dan idan nine akayima haka, to idan na suma bazan far fad'oba.
   Dan haka atake agurin nabiya sadaki aka maida d'aurin auren akan MODEEBBO!!!!.
    momcy tad'an zaro idanu, Alhaji modeebbofa kace??, papa ya gimtse fuska ya ce, "ashe kin jini!!.
  Ta ce, "amma kana ganin baza'a samu matsala a wajen modeebbo ba??, papa ya kwantar da kansa ajikin kujera, ya ce, "aii bana fata na haifi d'an dazai bijirema umarnina, ko mas'ud nace na d'aurama aurennan dole ya amince bare NAWAF.
   momcy ta ce, "kayi hak'uri Alhaji bahaka nake nufiba wlhy, ina farin ciki da umarninka, ALLAH kuma yasanya alkairi, wlhy tun kafin naga yarinyar ma tashiga raina, kuma ina k'aunarta tamkar yanda nakeson su modeebbo.
   Papa yay murmushi yana tashi zaune, yakama hannun momcy yana murzawa, ngd ummul'khairi, ngd da had'in kan dakika bani, inaso ki taimaka mini wajen fahimtar da modeebbo.
   Momcy ta zare hannunta daga nashi tana fad'in Alhaji kar yarannan su shigo su gammu.
  Murmushi papa yayi batareda ya ce, "komaiba, waya ya d'auka yana kiran Nawaf!.
   Nawaf yana kwance ad'akinsa  yanaso yay barci, dan yau zaitafi abuja da yamma, ya mik'a hannunsa yana laluben wayarsa datake wringing, da sauri yamik'e zaune dan ganin papane yake kiransa.
   Cikin ladabi ya ce, "papa barka da rana, barka kadai papa yafad'a, ya ce, "kana inane??, cikin ladabi ya ce, "ina d'akina papa!.
  To kazo kasameni.
To Nawaf yafad'a tareda mik'ewa yafito domin amsa kiran papa.

Afalon momcy ya tarar dashi, ya rissina ya gaishesu, suka amsa, papa ya ce, "Modeebbo miye matsayina a wajenka?.
   Cikin matuk'ar mamaki Nawaf yad'ago yana kallon mahaifan nasa, ya daure ya ce, "papa kai mahaifinane, wanda banida kamarsa aduk fad'in duniya.
   Papa ya jin jina kai, tareda cewa masha ALLAH, to modeebbo amatsayina na mahaifinka na zartar da umarni akanka yanzunnan, nan papa ya labratawa Nawaf duk abinda ya faru.
   Atsorace Nawaf yake kallon papa yayinda zufa keta ambaliya adukkan sassan jikinsa, ya daure cikin rawar murya ya ce, "papa aurefa kace??.
   Papa ya ce, "kwarai aure nace modeebbo, kuma ina fata amatsayina na mahaifinka zaka yimini biyaya, zaka kuma karb'i k'yautar da ubangiji yay maka da hannu biyu, natsuwarka nake buk'ata da farin cikinka, bana son wannan lamarin yatab'a rayuwarka bare kasamu matsala akan abinda kazoyi Najeria.
   Nandai sukaita lallashinsa, dayi masa wa'azi mai shiga jiki.
  Jiki a sanyaye Nawaf ya tashi yanufi d'akinsa, koda yashiga d'aki saiya zube afalo yana zabga zufa yadafe kai yana jujjuyashi, gsky yabani tausayi matuk'a.
   Ahaka mas'ud yazo yasameshi, arikice yake tambayarsa lafiaya, amma Nawaf yakasa magana, da hannu yaymasa nuni daya basa ruwa, ruwa mas'ud yabashi, tunda yakafa kai saida ya shanyeshi tas.
   Mas'ud dai kallonsa yakeyi cikin matuk'ar mamaki, saida suka d'uki tsawon minti goma ahaka, sannan Nawaf ya daure yabama mas'ud labarin abinda yafaru, mas'ud yay murmushi cikin tsokana ya ce, "haba mutumina kace kai yau angone, shiyyasa naji kana k'amshin angwanci.
    Harara Nawaff ya watsa masa tareda jan k'aramin tsaki.
   Mas'ud yay dariya ya ce, "ALLAH yasanya alkairi bro's, amma ka kwantar da hankalinka iyayenmu bazasuyi abinda zai cutar damuba, nima bari nazo nafara neman aure kafin ayi sadaka dani!, tunda anfara ta kanka.
   Duka Nawaf yakaima mas'ud, mas'ud ya kauce yana dariya.
   Nan yayta tsokanarsa har Nawaf yad'an saki jikinsa.

AMARYA YASMEEN
    zuwa yanzu labari yaje kunnan yasmeen, tayi farin ciki da faruwar hakan, saidai tana fargaba kuma da sabon mijin nata wanda batasan koshi waye ba, wannan dalilinne yasakata kuka, wai ba'a rabu da bukarba an haifi habu, karin maganar ta hausawa.
    Umma da abba sunata lallashinta da mata nasiha.
   Amma gaba d'aya jikinta ya d'ume da zazzab'i mai zafi, dan danan tafar rawar sanyi, har hak'oranta suna had'uwa waje d'aya.
    Asibiti aka tafi da'ita cikin hanzari.

FAISAL.
   A gidansu faisal kuwa tunda labari yaje kunnan hajiya jummai ta yanke jiki tafad'i, saida aka yayyafa mata ruwa ta kawo numfashi, da kuka ta farka, lallai d'anta yayi ganganci, ya kumayi asara wadda tanada tabbacin bazai samu madadintaba.
   Sukansu danginta dana Alhaji buba sai masifa sukeyi, suna fad'in aii laifinsune dan sune suka sangarta faisal d'in, shiyyasa baya ganin kowa da daraja a cikin family d'in.
   Faisal kam ko ajikinsa, dan aganinsa hakan shine dai2, amma daga lokacin daya ci karo da sak'on wata takarda sai komai ya canja, ya daddage ya tsala ihu yana kiran yashiga uku!!.
    Dafarko babu wanda ya kulashi, amma da akaga ihun nasa bana k'arewa bane sai aka fara kawo masa agaji, wani k'anin Alhaji buba ne yad'auki takardar yana karantawa, shikansa arazane yake duba takardar.
   Dangi suka shiga tambayar lafiya??.
     Ya ce, "inafa lafiya, lallai faisal kayima kanka, maganin mutumin dabaya bincike bare ganin girman manya a harkokinsa, kuma ka d'auka abinda ka shuka shine kake girba.
   Sakina k'anwar hajiya jummai ta kwace takardar tafara karan tawa kowa yanaji.

   Assalamu alaika babban yaro!!
   lallai kacika dak'ik'i mara tunani, kodayake ALLAH ne ya kwaci yarinyar kirki daga hannun fasik'i, wanda bai d'auki sab'on ALLAH komaiba.
   Na taya yasmeen murnar barin hannunka.
   Faisal ban rama kashi goma daga cikin abinda ka aikata minba, kaine kayi sanadin lalacewar 'yar uwata, ka lalata mata rayuwa ka koya mata fasik'anci, ALLAH ya isa tsakanina dakai faisal.
   Kuma yasmeen ba karuwa bace, ita tsarkakrkiyace, kamilar mace, dama kun tursasatane itada mahaifanta akan ta aureka.
    To yanzu ALLAH ya bata miji nagari, mai k'yawawan halaye, d'an babban gida.
   Amma naso ace nine na auri yasmeen, kodan zuciyarka tabuga, sakari shasha.
   Sako daga abokinka mai sonka da k'aunarka
HISHAM AHMAD KT! !!!!!!!!!!!.
   Talek'o ta koma.

Gaba d'aya dangi suka d'auki sallalami, tareda ALLAH wadai da halin faisal.
   Wasuma ALLAH yakara suke cewa.
   Faisal kam sulalewa yayi a k'asa saboda bak'in ciki, dahanzari suka yayeshi zuwa asibiti.................

Lallaikam yau anayin rikita2 a Najeria





Bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        LUV U OLL MY FAN's

©2016
[11/12/2016 16:51] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
  NAWAFF  
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 15

....A asibiti kam al'amura sun dai2ta a b'angaren yasmeen, ansaka mata k'arin ruwa tanata barcinta.
    Sai yamma lik'is ta farka, dak'ar tasha tee aka bata magunguna, takai dubanta ga Abba dake tsaye jingine da bango, saitaga har yad'an rame, ya ce, "mamana sannu kinji!.
   Kai ta d'aga tana hawaye, umma tashiga sharemata hawayen tana rarrashi, yaseer yazo yazauna kusada ita, shikanshi duk yayi wani iri, cikin sanyin murya ya ce, "kiyi hak'uri aunty kibar kuka, na tabbata hakan alkairine agaremu, tunda ALLAH ya ku'btar dake daga hannun wannan d'an iskan!.
    Yasmeen ta share hawaye, ta ce, "yaseer gskyarka, na! kub'ta daga hannun faisal, saidai bansan hannun wa? kuma na fad'aba, ta'kare maganar cikin kuka mai tsuma zuciya.
   Abba yakaraso ya zauna d'ayan gefenta, hannunta yakamo yarik'e, yay d'an murmushin dauriya, karki damu mamana insha ALLAHU mijinki na yanzu mutumin kirkine, kuma nasan zakiyi alfahari dashi watarana.
  Duk da nima banganshiba, amma yanayin mahaifinsa da kamalarsa yanuna d'an nasama mutumin kirkine, kiyiwa mijinki 'kya'ky'kyawan zato kinji!!.
    Yasmeen tad'aga kai tana share hawaye, ahaka likita yashigo ya samesu, ya k'ara duba jikinta, yaga komai normal, babu 'bata lokaci ya sallameta, suka tattara suka nufi guda.
  Wannan kenan.

A'bangaren Nawaf kuwa yana cikin damuwa shima, shikam dayasan abinda zai tarar kenan a Najeria dabazaiyi fatan zuwaba, yafitar da huci mai zafin gaske daga bakinsa tareda cije le'bensa na kasa.
   Talatu taiyi sallam a 'kofar d'aki, banza yay mata bai amsaba bare yabata ixinin shigowa, takai minti biyar atsaye, jin ba'a amsataba yasa tadannakai cikin d'akin atunaninta baya nan.
   Saida gabanta yafad'i yayin datayi tozali dashi azaune, jikinta yana 'bari ta ajiye abinda takawo masa, ta rissina tana gaisheshi!.
   Maimakon ya amsa mata saiyaja tsaki tareda watsa mata harara, dasauri tatashi tafito tana rawar jiki.
   Kafa yasa ya ture kular, ALLAH yasama abincin bai zubeba, wayarsa tafara neman agaji, kallo d'aya yaymata ya d'auke kai, takatse aka sake kira, nanma yay burus, shikuwa maikiran sarkin naci saiya cigaba da kira.
   A'kufule Nawaf yad'auki wayar , amma yayi shiru ya'kiyin magana.
   Daga can akace modeebbo wai sai yaushe zaka shigo?, karka manta munyi dakai! zakataho yau da 'karfe 4, amma gashi har 5 tayi.
   Nawaf yaja siririn tsaki, ya ce, "saika bari kaga gari ya waye banzoba sannan kayimin 'korafi.
   Daga can akace to shikenan, amma yakamata kayi 'ko'kari kasandai kanada matu'kar muhimmanci a wasannan!!.
  Banza Nawaf yay masa, saima ya kashe wayar gabad'aya, yana bala'i, kabi ka isheni da surutun tsiya, bakusan abinda yadamu mutumba zaka wani dameni da kira, ku damuwarku kawai kuka sani, yaja tsaki tareda kwanciya ya lumshe idanu.
   Ahaka mas'ud yashigo ya sameshi, yad'an girgiza kai ta reda ta'ba Nawaf.
   Ahankali ya bud'e idanu yana kallon mas'ud.
  Mas'ud ya ce, "haba bro's yanaga baka shiryaba ne, kasanfa ka makara ma.
    Nawaf ya yatsine fuska yana yima mas'ud kallon gefe, har ya bud'e baki zaiyi magana saikuma yayi shiru.
    Azuciyar mas'ud ya ce, "yau kuma miskilancin ya motsa kenan?, ganin Nawaf ba amsa zai bashiba yasa yanufi bedroom d'insa, kaya ya had'àma Nawaf tsaf sannan ya fito.
    Kan hannun kujerar da Nawaf yake kwance yazauna, cikin sigar lallashi ya ce, "kayi ha'kuri my bro's, ka d'auki hakan amtsayi 'kaddararka, kasan kanada matu'kar muhimmanci a wajen wasannan.
   Inaso kacire duk wata damuwa ka ajiyeta gefe, ka kar'bi 'kautar da ALLAH yabaka, aure alkairine, kuma nasan wataran zakayi alfahari dashi, idan papa yaga kana cikin damuwa zai d'auka bakabi umarninsaba, ka daure ka kauda komai kaji!!.
    Nawaf ya d'ago manyan idanunsa dasukayi jajir ya ce, "mas'ud ina cikin damuwa wlhy, karka manta aurefa papa ya d'auramini batareda nasan yarinyarba, bansan halintaba batasan nawaba, bata sanniba.
      yo wai tayayama zamu kasance amatsayin ma aurata?, kokad'an banida niyyar yin aure yanzu kaima kasani, amma papa ya kama 'ka'kaba mini, wlhy idan zaka kasheni bansan yanda zan zauna da macebama ni!!.
    Murmushi mas'ud yayi, kaga d'an uwa kwantar da hankalinka, indai yanda zaka zauna da itane damuwarka to zan koya maka, yafad'a cikin tsokana.
    Harara Nawaf yasakar masa, aii kaga matsalarka kai bakomai kake d'uka serious ba.
   Mas'ud yay dariya kaiwai batareda ya ce, "komaiba.
   Nawaf ya mi'ke yanufi bedroom d'insa, bayi ya shiga yasakarma kansa tsawa, (nakula indai yana cikin damuwa yanaso yasakarma kansa ruwa, komiye sirrin hakan??. ) yakai tsawon minti goma ahaka, daga baya yay wankan sosai yafito.
   Yaudai ba'ayi wani gayuba sosai, danko sumarsa mai gyaraba yafito, amma yayi 'kyau ba laifi.
   Mas'ud dake zaune yana cin abinci ya ce, "yauwa kokaifa, yanzu sauranka abinci, kaci saimu wuce.
    Yatsine fuska yayi tamkar wata mace, ya ce, "babu wani abinci dazanci malam, dan konaci bazaiyi amfani ajikina ba.
   Mas'ud ya ce, dadai kadaure kaci.
   Hanyar waje yanufa yana fad'in kasameni a wajensu momcy.
   Mas'ud yay murmushi, wataran yakan rasa Nawaf wane irin mutumne?, yasan duk duniya babu wanda yakaisa sanin halin Nawaf bayan iya yensa, amma shi kansa wata sa'in lamarinsa yana d'aure masa kai, mutimne miskili, masifaffe, saidai bayason yawan hayaniya, ba kowa yake ganin dariyarsaba, bakuma harkar kowa yake shigaba, wannan yasa wasu suke masa kallon mutum mai wula'kanci kuma ba haka bane.
   Saika zauna dashi zakaga yanada su'kin kai da son mutane.

Nawaf yana zaune gaban papa sunata yimasa nasiha shida momcy.
   Papa ya ce, "yau dadaddare zamuje nida Alhaji khasim gidansu matar taka, abinda shawara tabayar zakaji a waya, saimuji lokacin daya dace ayi biki, kaima yakamata ace kaje kafin kawuce.
    Nawaf yad'ago da sauri, ya ce, "papa ayimin afuwa saina dawo, wlhy na makara sosai saikirana koc d'in yakeyi tun d'azu, amma nayi al'kawari idan nadawo zanje.
   To shikenan papa yafad'a, ALLAH yabaku nasara, amma zan kar'bi number ta na turo maka, dan kakirata ku gaisa.
    To kawai Nawaf yafad'a.
  Sun masa nasiha sosai, sannan suka tafi shida Mas'ud da Abdallah da Anwar, dan suma zasuje su kalli wasa.
   Tunda suka tafi Nawaf ya jingina da kujera ya lumshe idanu, shi kad'ai yasan damuwar dayake ciki.
   Mas'ud dasu Anwar ne kawai suketa hirarsu.
   A kaduna suka tsaya sukayi sallar magriba da isha'i, dan gudu sosai mas'ud yakeyi ahanya.
    Karfe 8:30pm suka isa cikin birnin abuja, mas'ud ya ce, "bari mufara kaika sanna mu nemi masauki ko??.
   Nawaf ya ce, "A'a kumuje ku fara neman masukin sannan.
   Hotel suka nufa, suka kama d'aki biyu, Abdallah da Anwar d'aya, mas'ud d'aya, bayan sun kammala komai suka d'auki Nawaf zuwa (trening cam)masukin 'yan wasa.
    Tunda suka shigo get d'in ake d'aga musu hannu, sauran 'yan wasa sukazo suka tarbesa sunamai farincikin ganinsa, shima dai dole ya daure ya kauda damuwarsa zuwa gefe yana amsa musu gaisuwarsu.
    Bayan komai yalafa su mas'ud suka nufi masaukinsu, sukabar Nawaf cikin takwarorinsa 'yan wasa.


FAISAL
    faisal kam yanacan likitoci sun rufu akansa, hajiya jummai sai kuka takeyi, bata son tilon d'anta ya ku'bce mata, shikad'ai ta mallaka a duniya batada kamarsa.
   Alhaji buba kuwa sai safa da marwa yakeyi, yakasa zune yakasa tsaye.
    Haka dangi sunyi jugum jugum, taron biki yazama taron jimami, dayanzu anacan ana cashewa, amma ango yaja musu zaman tagumi a asibiti.
    To shimadai likitoci sunyi nasarar farfad'o dashi, amma anhana kowa shiga wajensa, dan ba'aso ayi masa hayaniya..................






Bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        LUV U OLL MY FAN's

©2016
[11/12/2016 18:28] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 16

.....da daddare su papa suka isa gidansu yasmeen, tarba akayimusu ta mutinci, har cikin falon abba aka kaisu, aka kawo musu ruwa da abinda ya sauwa'ka, bayan an gama gaishe2 suka shiga tattauna abinda ya kawosu.
    Alhaji khasim ya ce, "munzone muyi muku godiya da 'kyautar dakuka bamu batarda kunsan ko su waye muba, ALLAH ya d'orar da wannan zuminci yakuma basu zaman lafiya.
   Abba ya ce, "ai mune da gidiya, domin kun kauda mana wata damuwa dataso ruguzamu alokaci d"aya, mungode ALLAH ya'kara dan'kon zumunci.
   Gaba d'aya aka amsa da amin.
 Anan abba yabadua cikakken tarinsa, bai 'boye musu komaiba, har baro garin kwangwalan dasukayi.
    Suma sun bashi nasu tarihin batareda sun 'boye komaiba.
  Daganan suka tattauna akan biki sainan da 'karshen shekara zuwa sannan yasmeen takammala NCE d'inta.
   Abba yaje yakira yasmeen da yaseer sukazo suka gaisheda su, abba ya ce, "ga d'iyar takunan, papa ya ce, "d'iyata zonan kusadani!, akunyace yasmeen taje kusada 'kafafunsa ta tsugunna.
   Papa ya ce, "masha ALLAHU, ALLAH yaymuku albarka kinji, yasaukar da alkairi akan wannan had'in namu.
   Suka ce, "amin.
  Nanadai akayi mata nasihohi, akan takula dakanta, tasan yanzu ita matar aurece akwai banbaci tsakanin da, da yanzu.
   Papa ya kar'bi number d'inta, yabata ta Nawaf da tashi da momcy da mas'ud da Abdallah da Anwar, yay mata bayani akan matsayinsu, ya ce, "kuma ta saurari kiran kowannanensu.
   Sukai mata alkairi sannan suka tafi, suna mai yabon zuri'ar yasmeen.
   Lallai sun yaba da tarbiyyar muta nen gidan.

Tunda suka tafi yasmeen tayi shiru tana tunani, indai yanda iyayen mijin nata suke haka mijin yake lalai ta more, dan taga dattako da kamala a tattare da iyayensa.
   To hakama abba da umma sunyi farinciki da samun suriki nagari.
   Yaseer ya ce, "gsky aunty kin more, ALLAH yasa haka mijinki yake 'kya'ky'kawa kamar abbansa.
   Yasmeen ta harareshi, kaifa nakula bakada kai wlhy, ni tashi kabani guri kazo ka cikani da surutu.
   Yaseer yay dariya, sisto plz ki kirashi mana tunda naga an baki number d'insa.
   Caja d'in wayarta ta d'akko tana fad'in kasan ALLAH idan baka tashiba zan zula maka ajiki.
   Yaseer yatashi yana fad'in A'a wlhy bara natashi, idan kika zulamin wanga caja ai sainayi jinya.

FAISAL
   Alhmdllh jikin faisal yana sau'ki, saidai uban sambatu dayake zubama mutane, babu abinda yake kira sai sunan yasmeen, shi sai yanzuma yasan yana sonta, yawan surutun dayakeyine yasa ake masa allurar barci.
   Da mutum yazo dubashi zaifara ro'konsa ya kawo masa yasmeen, dan ALLAH karsu bari ya rasata, wlhy yana sonta, dan ALLAH aje asaka wanda ya auri yasmeen ya sakar masa ita, shikad'aine ya dace ya zauna daita.
   Hajiya jummai ta matse hawaye tana fad'in Faisal ina saura, kayima kanka aii, nasan babu wani namiji dazai auri yarinya kamar yasmeen ya saketa, duk abinda namiji yake bu'kata awajen mace yasmeen ta had'asu, Tarbiya, ilimi, addini, nasaba, 'kyau.
   Duk ta had'a.
Danhaka ka d'auki 'kaddara kawai Faisal.
   Faisal ya 'kan'kame Hajiya jummai yana kuka, da sakin sambatun daya saba.
   Dole likita yazo yay masa allurar barci, sanna.
   Azuciyata na ce, "aii dama duk wanda ya taka rawar wani, yarasa filin taka tasa.


ABUJA. 6/7/2012
  8:30PM
     Abuja international stadium cike take da'kam da matasa maza da mata, kai harda yara da dattijai na 'kasashe daban2, dake Nahiyar Africa, harma da 'kasashen turai, domin kallon (Netion cup ).
    Yau Najeria da ghana zasu buga, babu abinda kakeji sai hayaniya irinta al'adar kwallo.
   Su Nawaf suka shigo cikin fili suna d'agama jama'a hannu, yayinda suma jama'ar suke d'agamusu hannu saboda 'kauna ko birgesu da 'yan wasan sukeyi.
   Bayan addu'a da taken Najeria da 'yan wasa suka gabatar, suma 'yan wasan ghan sunyi nasu.
   Sai aka fara 'ko'karin fara wasa, wasa kowannen su yakeyi cikin 'kwarewa.
   Can na hango Nawaf sanye da JC mai ruwan tutar Najeria, sunyimasa 'kyau matu'ka, saidai fuskarsa babu walwala, dan buga kwallon yake kamar bayaso.
   Gab daza'a tafi hutun rabin lokaci  ghana tasmu nasarar zira kwallo 1, nanfa mutanen ghana suka hau ihu da sowa.
   And'an fara wasa aka hura, domin tafiya hutun rabin lokaci, saidai 'yan Najeria sun d'an fara shiga damuwa.
   Dan haka koc d'in Najeria yaja Nawaf gefe, yana tambayarsa ko bashida lfy ne??.
   Nawaf ya ce, "lfyr sa 'kalao.
  Nan dai koc yashiga ro'konsu akan su dage, karyazama tun a kolfayin(colfine) su nuna gazawarsu.
    Bayan andawo hutun rabin lokaci, aka d'ora wasa, nanma dai ghana sunfi nuna 'kwazo akan Najeria.
   Kad'an ya hana Ghana cin kwallo ta biyu.
   To daga nanne fa Nawaf ya dage, minti 15 da dawowarsu ya zira kwallo a raga, karkaso kaga murna wajen 'yan Najeria.
   
   Zan iya cemuku harda Yaseer da yasmeen amasu murna, dukda basosai yasmeen take kallon wasanba, amma dayake suna tare afalo itada yaseer sai take d'an kallo.
  Ammafa har yanzu batasan Nawaf shine mijin nataba.
   Abba yafito yana fad'an ihun da yaseer ya kwala musu.
   Yaseer ya ce, "abba kayi ha'kuri wlhy modeebbo ne yaci mana kwallo.
   Abba ya ce, "to basai ayi murnar ahankaliba, amma irin wannan ihu haka.
    kwallo taci gaba da tafiya yanda ya kamata, dan yanzu Najeria sun dage, suma ghana sun dage, dan haka wasan ya d'auki zafi kowa yana so yazira kwallo tabiyu.
   Saura minti 4 atashi Najeria takuma zura kwallo da taimakon Nawaf wani d'an kwallon Najeria ya zura, woyyo ALLAH karkuso kuga murna, koda yake kuma masu karatu na hangoku kuna murna.
   Daganan najeria tafara jan 'kafa domin acinye lokacin abanza, aka 'kara minti7, shima dai ashiririta aka cinyeshi, Najeria sai fitar da kwallo suke, suna langyare, harda tsayawa akayi canjin 'yan wasa.
    Ahaka dai aka tashi 2-1
  Najeria-2 & ghana-1

Wasa yayi 'kyau Najeria sai murna sukeyi.
   Yaseer ya ce, "sisto dan ALLAH yakiga gay d'innan, jiba kiga yanda yake gara kwallo cikin kwarewa.
   Yasmeen tad'an ta'be baki, kaini wannan mugun baya wani birgeni, kai yake burgewa.
   Yaseer ya ce, "sisto muguntar mi yay miki??.
  Sai asannan ta tuna yaseer bai san komai daya faru tsaka ninta da Nawaf bafa.
   Ta ce, "sai yayimin wani abu zan kirashi mugu, kaga saida safe ni nagaji.
   Yaseer ya murgud'a mata baki ya mi'ke shima ya shige d'akinsa.................







©2016


Bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        LUV U OLL MY FAN's
[13/12/2016 15:37] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page 17

......Yasmeen zaune ta rabga uban tagumi, gaba d'aya tayi kewar school, tanaso takoma makaranta amma batasan yanda zata fiskanci abba da zancrnba, ta fesar da huci mai zafi tareda dafe kanta datakeji yana sara mata.
   Waya tajawo ta kira yaseer, kana ina?, naji tafad'a, bansan miya cemataba daga can nagadai ta ajiye wayar kawai.
   Babu dad'ewa yaseer yashigo da sallama, ta amsa batareda ta tashi daga kwanciyar datayiba, ya zauna abakin gadon yana fad'in gani auntyna!.
   Yasmeen ta ce, "yaseer shawara nakeso miyi.
   To wace irin shwara kenan?, yaseer sonake na koma makaranta amma ina tsoron tambayar abba!, ya kake gani za'a ayine??.
   Shiru yaseer yayi yana nazarin mafita, zuwa can ya ce, "ai inaga kibari kawai nafara yimasa magana saimuji amsar dazai bayar koya kika gani?.
   Eh yayi kakawo shawara mai 'kyau d'an uwa, yasmeen ta juya tana kallon wayarta datake wringing saidai batasan number d'in ba.
  Jiki a sanyaye ta d'auka saidai tayi shiru.
   Daga can akace salamu aliki!.
   Wa'alaikassalam yasmeen ta amasa.
Amaryarmu ykk??, ta ce, "lfy lao, ta d'ora da fad'in dan ALLAH wanene??.
   Mas'ud yay sasanyar dariya, ya ce, "sunana mas'ud khasim, d'an uwan mijinki kuma abokinsa.
   ta ce, "ALLAH sarki, sannu!.
   Ya ce, "yauwa kema sannunki amarya, dama zan fad'a mikine ki saurari zuwanmu yau da yamma.
   Muryar yasmeen na rawa ta ce, "saina ganku.
  Ya ce, "to nagode, sai anjima.
                      Yaseer daya tsura mata idanu tun d'azu ya ce, "sisto keda wa??, ta had'iye wani yawu sannan ta ce, "wanine wai mas'ud!.
     Mas'ud kuma?, yaseer ya maimaita sunan, ya ce, "sisto kodai abokin mijinki da aka baki number shi jiya.
   Yasmeen ta girgiza masa kai batareda tayi maganaba.
   Murmushi yaseer yasaki, ya ce, "tomiya farune?? Ko zasuzone??, nanama kai ta kad'a masa alamar eh.
   Yaseer yami'ke yana fad'in bari nasanarma umma to.
   Da sauri yasmeen ta ce, "malam ban saka kaba, ko saurarenta bayyiba ya fice, yanaji tana kwala masa kira amma yay mata banza.
   'Dakin umma yanufa, tana zaune tana linke kaya, ya zauna kusada ita.
   Umma ta ce, "autana lafiya dai ko??, yaseer yay murmushi yana fad'in lafiya lao umma, dama aunty ce zatayi ba'ki shine na ce, "bari nasanar miki, dan kinsan itadai ba fad'a zatayiba.
   Umma ta ce, "gsky ne d'an albarka, amma wad'anne irin ba'kine??, mijinta ne zaizo.
   Umma tayi murmushi ta ce, "madallah, ALLAH yakawoshi lafiya, sai azo ashirya musu kayan tarba kenan.

Abuja (Trining cam).
Nawaf zaune bisa kujera agefen fili, yana zaune yana hutawa bayan sun gama trening shida sauran 'yan wasa, zaune yake amma ya kwantar da bayansa a jikin kujerar, hannunsa ri'ke da waya, da'alama yana chatting ne, dan naga saifaman murmushi yakeyi.
   ya d'auki d'aya daga cikin wayoyinsa dake wringing, cikin murmushi ya ce, "shegen sama sai yanzu katuna dani.
   Mas'ud ya ce, "A'a dama kana raina, banaso na takura makane ko kana uzuri.
   Ayya Nawaf yafad'a, kunje gida lafiya??, lafiya lao mukazo wlhy.
   Zaka shigo yaune?, ito gani dai, idan na samu dama zan zo, idan kuma banzoba zan kalla anan insha ALLAHU.
   wane uzuri gareka dazai hanaka zuwa kallon wasanmu na yau??.
  Hhhh, zanje ganin amaryane.
 Amarya kuma?, a ina??.
Hhhh lallai mutumina kana sha'aninka, to zanje ganin amryarkane, dansu papa sunce yakama naje kafin kadawo.
   Tsaki Nawaf yaja, tareda gyara zama.
   Tomiye najan tsakin, ko bakaso naje saika dawone?.
  Kaga malam idan zaka kabar tsayani, idan kaje kabar tunawa dani, ALLAH idan wannan maganar tasa ka kirani to zan kashe wayata, inada aikinyi.
   Mas'ud ya ce, "to kashe mana, idan kakashe sai akace maka zanji haushi......
Kafin mas'ud yarufe baki Nawaf yakashe wayar d'if,, dariya sosai mas'ud yakeyi, saida yayi mai isarsa sannan yami'ke yana fad'in wannan man d'in wlhy d'an yawane..

4:30pm 
  Karfe hud'u da rabi direba ya sauke su mas'ud a 'kofar gidansu yasmeen, dayake shi yakawosu papa ranar, dan haka papa ya ce, "yakawo su mas'ud gidan.
   Wayarta mas'ud yakira ya ce, "munzo amarya.
   Yasmeen ta ce, "to, gaba d'aya batada walwala, daka ganta zaka san tana cikin damuwa, ita azatonta harda mijin nata aka zo, dan haka gabanta yafara dukan tara2.
   Yaseer ta turo ya kaisu falon abba, Abdallah ya ce, "lallai indai kaine 'kanin antyn mu, to kuwa yayanmu ya more.
   Dariya kawai yaseer yayi ya ce, "musu yana zuwa.
   Babu dad'ewa yacika musu gaba da kayan ciye2, saida yagama kawo komai sannan yasmeen tashigo falon 'kirjinta yana dukan uku uku.
    Kujera ta samu nesa dasu ta zauna, sanye take cikin ba'kar atamfa  riga da sket, ta yafa farin mayafi har saman kai.
    Suduka kallonta sukeyi, ta ce, "ina yininku??, mas'ud ne kawai ya amsa, Anwar yataso yadawo gefenta, ya ce, "aunty aiimu 'kannenki ne, muzamu gaisheki, ina yini, kad'an ta d'ago tana kallon Anwar saida gaban ta yafad'i domin ganin yayi mata kama da wani data tab'a sani.
   Ta amsa tana murmushin ya'ke, Abdallah ma yadawo d'ayan gefenta ya gaisheta, nanma ta amsa masa cikin murmushi.
   Mas'ud ya ce, "amaryarmu!!.
  Na'am ta amsa tareda d'ago kai tana kallon mas'ud, suduka sukaima juna kallon mamaki, kardai ace wanan ne mijin nawa yasmeen tafad'a a zuciyarta.
 Saida kama tatuna daya kirata ya ce, "shi abokin mijintane, toko ina mijinki oho? ?
    Mas'ud ya ce, "dama kece amaryar tamu, lalali nayi matu'kar farin ciki da faruwar hakan ALLAH ya sanya alkairi.
   Ita dai yasmeen ta kasa furta komai, amma idanunta sun cika da kwalla, dan batasan waye zai kasance mijintaba, tunda gashi har abokinsa yazo shi yakasa zuwa.
   Kamar mas'ud yasan tunanin datakeyi, ya ce, "megidanki yana neman afuwarki, shima ya nan zuwa nan bada dad'waba, dan yanzu haka yana abuja, amma nanda nextweek zaizo insha ALLAH.
     'Dan murmushi yasmeen tayi tareda fad'in babu damuwa ALLAH yakaimu.
    Sukace amin dai.
      Nan Abdallah da Anwar suka shiga zuba mata surutu, har saida mas'ud ya ce, "su tashi su tafi.
    Bayan sun shiga sun gaida su umma sannan suka tafi.
   Ji sukayi kamar karsu tafi, dan matar yayan nasu ta burgesu, gata 'kya'ky'kawa, ko amota hirarta sukayi tayi har suka isa gida.
     Nanma sukaita bama momcy labarin surukarta, da karramasu da akayi musu agidansu yasmeen.
    Momcy taji dad'i sosai, itama ta 'kagara taga surukar tata.
     Yaseer yataya yasmeen kwashe manyan  ledoji dasuka kawo cike da sayayya ta birgewa.
    Lamarin yabama yasmeen mamaki, amma taji har azuciyarta zata iya zama da mas'ud amatsayin miji, inhar dashine mijin nata, dan alamunsa suna nuna mutumne mai ha'kuri.
   Yau ko abincin dare bata ciba tana d'aki kwance abinta.
   Abba ya ce, "aje akira masa ita, koda yaseer yashiga d'akin saitayi kamar tana barci.
   Yaseer yadawo ya ce, "barci takeyi..
             Bayan fitar yaseer babu dad'ewa wayarta tahau wringing, tayi kamar bazata d'aukaba, saida takusa tsinkewa sannan ta d'auka ta kara akunnenta.
   Amma daga can an'ki yin magana, ta daure tayi sallama, nanma akayi mata shiru, a'kufule ta ce, "wai dan ALLAH wanene??.
   Cikin gadara taji ance, zaki baya fad'ar kansa, saidai risinawar namun daji ta bayyanar da matsayinsa.
    Yasmeen ta ce, "huuuum saidai kayi rashin sa'a ni mutum ce ba dabba ba.
   Tana kaiwa nana taja tsaki ta kashe.
   To shima dagacan tsaki Nawaf yaja, yana wani yatsine, fuska, shifa dama papane ya takura masa akan saiya kirata, shine zata wani kashe masa waya, lalaima yarinyar nan zanyi maganinki kwarai da gsk.
   Juyawa yayi wajen 'yan uwansa 'yan wasa dan dama wasa zasu fara, yakirata kafin lokaci yacika.

9:00pm
   Yauma dai Abuja international stadium cike take da 'yan kallon wasa.
   Yau Najeria zasu buga da kamaru.
  Bayan shigowarsu Nawaf cikin fili, sukayi addu'oi da sauran abinda yadace, aka fara wasa.
    Yaukam wasan yana tafiya dai dai, dan 'yan Najeria suna nuna kwazo, cikin kwarewa suke gara kwallon, yayinda 'yan bayan fage suketa zugasu da ihu.

    Har d'aki yaseer yaje yataso yasmeen wai tazo ta kalli kwallo, hararasa tayi takoma ta kwanta, dan tana cike da haushin rainin hankalin da'aka yimata yanzu a waya.
   Dayaga zata b'ata masa lokaci saiya fito kawai dan ya kalli wasansa.

har aka tafi hutun rabin lokaci, babu wad'anda suka zura kwallo.
   Dan haka da'aka dawo kowa yayta 'ko'karin akan son yaga yazura kwallon, amma har lokaci yarage saura minti10 babu abinda ya canja.
    Ana saura minti1 atashi Nawaf yasami nasarar antayawa Najeria kwallo a raga nantake 'yan Najeria suka hau ihun murna gurin ya kwaure da hayaniya.
   Da'kar aka lafa, bayan 'kara minti 7 da akayi.
   Acikin minti na 5ne kamaru suka so zira kwalloamma golan Najeria ya cireta.
   Antashi 1-0
 Najeria tanada 1 & kamaru 0

   Can na hango Nawaf yad'aga gorar ruwa yana kwan kwad'a, yayinda suke tafawa da hannu d'aya da sauran 'yanwasa, kowa yazo akad'an tafa saiya wuce, wasu kuma sai an d'an rungumi juna.
   'Yan kallo kuma sunata d'aga Najeria suna wa'ka.
   Yayinda muta nene kamaru kowa fuska ahad'e.
....................







© 2016


Bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        LUV U OLL MY FAN's
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Blog Archive

Contact Form

Name

Email *

Message *