check your best novels here

Sunday 26 February 2017

NAWAFF!!! 23 to 26

[17/12/2016 14:56] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆







NA BILKISA IBRAHIM




page 23 & 24

......WASHE GARI...su papa sukazo shida 'kaninsa dayazo daga katsina, dakuma Abban mas'ud, bayan angama gaishe2 suka shiga tattauna abinda yakawosu.
   An 'kar'kare magana za'ayi shagalin biki nanda sati hud'u masu zuwa, (1monch )sananan su Nawaf sun gama wasan kofin africa kenan, kafin yakoma Spain sai asha shagalin biki kawai.
   kai zamu shabiki, kowaya yashirya masu karatu.
    Bayan an 'kar'kare magana yasmeen tashigo ta gaidasu, 'kanin papa ya yaba kam da tarbiyyar yasmeen , yanada tabbacin Nawaf yayi dace!!!!!!!.

-------------------------------------
   Yau dai gaba d'aya family d'in suna falon papa, Nawaf yana kwance a kujera mai zaman mutum biyu, Anwar yana saitin kansa ri'ke da littafin larabci, Nawaf yana koya masa, Abdallah kam hankalinsa yana kan tv dan shi dama d'an a hutane.
   Papa da momcy suna gefe zaune papa yana nazarin wasu manya2 littatafai shida momcy, da alama bincike yakeyi akan wata shari'ar, momcy tana tayashi, tunda itama mai ilimince.
   Nawaf ya ce, "Abdallah tashi kakawo mini lifton.
   Abdallah yad'an turo baki gaba, yaya dan ALLAH bari ad'an wuce nan.
   Harararsa Nawaf yayi, ya ce, "to uncle Abdallah bari najiraka, da sauri Abdallah yatashi dan yasan gatse yay masa, yana kuskurewa saiyasha mari abanza, dan Nawaf akwai saurin hawa kamar filawa lol.
   Momcy ta ce, "ya ALLAH kashirya mini Abdallah.
   Sukace amin.
Papa ya ce, "aii Abdallah shike bama kowa ciwon kai agidannan.
  Abdallah yashigo d'auke da butar shayi mai 'kalli da 'karamin kofi da cokali, agaban Nawaf ya dire batare da yayai maganaba.
   Girgiza kai kawai Nawaf yayi yad'auka yazuba yana sha, ya ce, "yaro nafika zafin kai.
   Papa ya ce, "yau modebbo yaushane zaka koma abuja??.
   Papa gobe idan ALLAH ya kaimu da yamma.
   Okey ALLAH yakaimu, aii momcy tamaka bayani akan tarewar matarka ko??, Nawaf yad'an rage fara'a, eh tagayamin, amma papa dan ALLAH abari saina koma Spain idan mun gama (KAKAR WASANNI), nadawo tunda muna samun hutu awanan lokacin saita tare!!.
   Kagafa ko inda za'a ajiyeta babu, amma zuwa sanan an kammala ginina!!. 
   Agidan Nawaf yake gini tacan baya, saboda papa yanada burin zama da iyalin guru ďaya yasa yasayi filin dake haďe da nasa yazagayeshi kowa ya girma cikin 'ya'yan saiya gina 6angarensa.
   Toshi Nawaf yaďan fara ginin ya watsar, gashi koma aure yaro yanzu. 
   Girgiza kai papa yayi, ban yardaba Modebbo, kafin katafi za'ta tare, 6angarenka za'a gyara muku yanzu saiku fara zama anan, anjima ka cire dukkan abinda kakeso daga 6angarenka kadawo dasu ďakin kusada nawa, dan za'a gyara 6angarenka asake komai naciki insha ALLAH.
     idan kazo wanan hutun saika tafi da matarka kawai, munriga mun gama yanke magana, yanzu hakama 'yan katsina sunsan komai, kuma yau dasafe nakira 'yan saudia na sanar musu, nextweek ma (MAHER da ZAID) zasuzo, 'kannanen momcy ne.
   Shiru Nawaf yayi dan zucuyarsa sai tafarfasa take, yanzu sai kawai abokansa suzo suga wanan 'yar yarinyar ya aura, gata mara kunya, kuma 6angarensa bedroom ďayane, kenan papa yana nufin a bedroom ďaya zasu zauna kenan???......
    Momcy ta katse masa tunani da fad'in yakamata ka sanar da abokanka, tunda yazu zamanine mai sau'ki komai zaka iya yi ta hanyar SOCIAL MEDIA.
   Nawaf ya ce, "to momcy zanyi 'ko'kari nida mas'ud, amma sainake ganin abun kamar babu shiri??.
   Miye rashin shiri anan modebbo, acikin wata d'aya mu zamu shirya komai, shiyyasa na ce, "su maher suzo!.
    Su Alhaji buba ba muta nen kirki bane, zasu iya aikata duk abinda tu naninsu yabasu.
  Momcy ta ce, "gsky ne Alhaji.
    Su Anwar suka shiga tsallen murna, za'ayi biki agidansu, shi dama Anwar bai ta6a ganin anyi taro agindansuba tunda shine auta, gara Abdallah yaga taron sunan Anwar d'in.

_________________________
    Ita madai yasmeen wanan labarin ya iso mata, saidai suna hanya d'aya da ango itama batayi murnaba, saima kuka data zauna tanayi, umma ta ce, "hawayen gareki dayawa yarinya, ke komai akayi sai kuka saikace hanyar ruwa, haka zakije gidan mijin dayayi miki abu ki hau kuka??, AĹLAH yabaki sa'a.
   Abba shidai lallashinta yakeyi, yayinda yaseer keta kwasar dariya danshi farinciki fal cikinsa.
    Da yamma Nawaf da mas'ud sukazo, fuskar ango da amarya babu walwala, bayan ta gaishesu mas'ud kawai ya amsa mata, ya ce, "Amarya ina 'kyauta ta??.
   Yasmeen tayi d'an murmushi, ta ce, "bari nakira maka ita, tana son tashi tana tsoron Nawaf ita kuma bazata tambayeshiba wlhy, kamar daga sama sai sukaji sallamar Ameena, yasmeen ta ce, " 'yar halak.
   Ameena ta zauna tana faďin to miya faru??.
   Tunda tashigo mas'ud ya yaba, kuma insha ALLAH yasamu matar aure kenan, Ameena ta gaishesu, amamakin yasmeen saitaga Nawaf ya amsa harda murmushi, ya ce, "Ameena zaki auri tuzurin abokina kuwa???.
   Harararsa mas'ud yayi ya ce, "kai malam waye tuzurun???.
    Cikin dariya Nawaf ya ce, "kai mana, aii itama tasan kai tuzurune 27years babu aure fa.
   Mas'ud ya ce, "ashe kaima tuzurinne??, yasmeen kinji tuzuru kika aura!!. 
    Haka sukayita tsokanar juna, kuma anan aka kulla 'kya'ky'kyawar ala'ka tsakanin amina da mas'ud.
   Ficewa sukayi suka bar Nawaf da yasmeen a falon, suma suka tafi domin yin tasu hirar.
   Nawaf ya mirtike fuska, ya ce, "k kice su papa su tsaida maganar bikinnan dasuke shirin yi!!.
   Yasmeen ta yaysine fuska, "kai miya hanaka ka fad'a musu naga kaine Namiji.
   Harara Nawaf ya sakar mata, sai akace miki ni mara kunya ne irinki!!!.
   Baki yasmeen ta ta6e tace ashe....
    Yay saurin cewa ashe mi???.
 ta murguďa baki tana faďin sainaji zafin ma'kara.
   twoow tsaki Nawaf yayi yana fad'in yarinya ki ajiye rashin kunyarki a gefe dan wlhy yanzu wahala zakisha bata wasaba.
  Yau ba shirmenki ya kawoniba dan inada abinyi, gobe zan koma abuja, duk abinda kike bu'kata ki sanarma mas'ud.
    Hummm kaidai kasha cizo malam, yasmeen tafaďa a zuciyarta.
   Saida ya'kara mirtike fuska sanan ya ce, "ki koma makarantarki idan kina ra'ayi.
   Cikin murna yasmeen ta ce, "dgsk??, harararta yayi ya ce, "k bana son shirme kinji.
   Baki ta murguďa masa, ya ce, "dawa kike???, ta ri'ke 'kugu da wanda ya tsargu mana.
    Nawaf yay murmushi danshi dariya ma tabashi, yakula ta rainashi da yawa, amma zai koya mata hankali kwanan nan,     ya ce, "habawa yarinya wataran ko ance kiyi mini rashin kunya bazakiyi ba wlhy.
   Kud'i ya ajiye mata 'yan dubu2 ďauri biyu, ya mi'ke, karki ďauka dan bananan ko dannance ki koma makaranta ki ďauka kinsamu hanyar yawo, nasaka masu kulamin da shigarki da fitarki, idan naji wani abu sa6anin dokar dana kafa, tofa kiyi kuka da kanki, yana gama faďa ya fice.
   Harara yasmeen tarakashi da ita tana faďin sai an karya dokar taka, tunda ba dokar ALLAH ba ce, "mutun ya rin'ka abu saikace wani ubana.
   Tashiga kwaykwayon maganarsa yanda yakeyi aģadarence.

__________ABUJA________
 Bayan kammala (colfine second round) da akayi, Najeria ta tashi da maki 7.
   To ayau kuma zasu buga da Egypt, (colfine cotter pineal) wasan daf da 'karshe ke nan.
   Wasa yayima 9ja daďi, dan antashi 1-0, 
    9ja 1 & Egypt 0
 Karkuga murna wajen 'yan 9ja.

2days later.
   (Seme pineal) wasan kusada 'karshe, 9ja da South Afirica, wanan kuma ankai ruwa rana, dan sai ana saura minti2 atashi, cosee!, wani ďan wasan 9ja yay wani fasin da Nawaf yasamu damar antayawa 9ja kwallon cikin ragar south Africa, guri yaruďe da ihu Najeria sai murna mukeyi.
   Dukkanin wasanan yasmeen ta kalla, dukda bawani burgeta yakeyiba, amma takanji tana sha'awar kalla, da antashi zakaga yaseer yakirashi yana masa murna, takan ta6e baki ta ce, "ma yaseer uban 'yan shishshigi kawai, ďan san asani.
   Oho dai yaseer yafaďa, kema san asani ďin yasa kike kallon kwallon yanzu tunda da ba'ka kallo da.
   Duka ta kaimasa ya kauce, cikin shagwa6a ta ce, "umma kinga yaseer ko yana tsokanata.
   Umma ta ce, "kunfi kusa, kubar sakani ashirmenku kunji.
   Yaseer yatashi yafice yana mata gwallo.
    Kwafa tayi ta ce, "zaka dawo ka sameni yaro.

Yaune za'a buga wasan 'karshe, yaukam stadium d'in abuja babu masaya tsinke, dan yau harda shugaban 'kasar NAJERIA shima yazo.
   Bayan gama addu'a da abinda yadace,Najeria da Algeria suka fara buga wasa, kowa iya 'ko'karinsa yake a wasanan, dan haka har aka tashi hutun rabin lokaci babu wanda ya zira kwallo.
    Bayan andawoma gwagwar maya aka cigaba dayi, amma ina komai bai canjaba, tun ana saran wani zai ci har aka fitar da rai, lokaci yacika aka'ara, shima ya shuďe babu wanda yaci, dole saidai ayi (peneritty).

 *Algeria tafara zirama 9ja
 *Najeria sai 9ja itama ta zira
 *Algeria 
 *Najeria 
 *Algeria 
 *Najeria 
 *Algeria 9ja tazubar
 *Najeria 
 *Algeria 
 *Najeria Nawaf ya zira mana ta 'karshe.
    Dukkan filin da sassan gidajen kwallo dake Najeria suka d'au ihu na murn, bakin kowa abuďe, shugaban 'kasa yayi murna sosai.

  Duk da kwallo bata burge yasmeen to yau tayi murna sosai, sai murmushi takeyi dan daďi.
   Na ce, "humm yasmeen kodai???????.
   Bayan shugaban 'kasa ya karramasu kowa yanufi inda yafi wayo, (club club nasu kenan)
 Shidai Nawaf kano yataho..................




©2016



Bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
          luv u oll my fan's
[17/12/2016 20:21] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page 25 & 26

....To shima dai mas'ud a6angarensa komai ya dai2ta, har ankawo kuďi dan anaso ayi bikin tareda na Nawaf, yasmeen tayi farinciki sosai da faruwar haka, bare ameena amarya, ai tafi kowa farinci, dan tana son mas'ud sosai.
      Yau kuma aka kawo lefensu su duka akwatuna bakwai2, komai iri ďaya, wanan aikin papa ne, dan shida momcy suka haďo lefen.
     Wannan shi ake Kiran lefen 'yan gata, mutanen anguwa da dangi duk sun yaba.   
        Filin jirgin na kano cike yake da matasa domin tarbar NAWAF!!.
   jirgi yafara shawagi neman muhallin sauka, bayan tsayawarsa fasinjoji suka fara fitowa, Nawaf shine na 6, ahankali yake sakkowa kamar bayaso,  jikinsa sanye da 'kananun kaya, ya ďora 'katuwar rigar sanyi fara, ya saki hular a baya, sai tashin 'kamshi yakeyi, yagoyo jar jakka abayansa wadda aka rubuta (Adidas)na ce, "kai gay ďinnan handsome ne gsky.
    Da gudu anwar yaje ya rungumesa, shima cikin farinciki ya rungume shi, yana faďin i missing u autan momcy.
   Missing u too yayana.
   Gaba ďaya 'yan uwa da abokan arzi'ki suka taso gareshi, 'yan jarida kuwa sai 'kutsa kai sukeyi domin samo bayanai.
   Da'kyar suka barshi yashiga mota mas'ud yaja suka nufi gida, anata ďaga masa hannu shima yana ďagawa.
   Abdallah ya ce, "yaya dabamu samu mun gudoba dasai yamma zamu baro filin jirginnan.
   Nawaf ya ce, "gsky ne brother shiyyasa naso na sauka da daddare.
   Mas'ud yay dariya ai koda daddaren ne sai mutane sun jiraka tunda anuna a labarai zaka sauka kano yau, aii ko randa kazo daga Spain mutane basu taru hakaba??.
   Abdallah ya ce, "to ba sunga ya cimusu kwalloba yau, suka tuntsure da dariya su duka.
   Anwar ya ce, "nifa wani tsareni yayi saina bashi number yaya, na ce, "masa banida waya kuma ban ri'ke number ba.
   Mas'ud ya ce, "hummm autan momcy sarkin wayo.
   A babban tsakar gidan sukai Parking, Nawaf yasha mamaki dan ganin dangi cike da gida, 'yan katsina da saudia, duk sunzo, dangi sai rungumeshi ake ana murna, musamman 'yan saudia dansu dama al'adarsuce.
   Family falo suka nifa inda sauran dangi suke harda kakarsu Nawaf ta wajen uwa tanan darai hajja humaira kenan.
   Hajja humaira ta ringume Nawaf tana farin cikin ganinsa, ta ce Masha ALLAH mai gida ka 'kara 'kyau da girma, kodai an canja mini kaine??, Nawaf yay dariya A'a hajjana ba a canja miki niba ninedai maigidanki na 'karfen!!!.
    Gaba ďaya akasaka dariya, ta ce, "kamanta damu ko Nawaf!!?, da sauri ya 'kara rungume hajja ya ce, "ni na isa na manta daku, uwargida sarautar mata, hajja nayi missing ďinki sosai.
   Hajja ta ce, "ďan nema kai dai bazaki hausarba bare larabcin?, turawa sun 6ata mana ka!!.
   Nawaf yay murmushi yabi dukkan iyaye da kakannin yana gaishesu, har 'yan katsina.
   Ya ce, "ni banga sauran sisters ďina ba??, kobasu zoba??.
   Tab wazai 'kizuwa bikin ka (Abi)yaya kenan, kowa yazo, sauran suna gidan amaryarka, muma yanzu za'a kaimu, wai a al'adar hausawa yaune ('kunshi)to zamuje mu ganine!!.
   Nawaf yay murmushi, lallai kam idan kun gani saiku koya koh??, dariya ameera tayi ta ce, "to Abi!!.
    Duk da larabci suke maganar, ina fassara mukune yanda zaku gane lol.
    D'akin kusada papa ya shiga inda ya maida kayansa kafin yatafi, yay wanka, yaci abinci, kwanciya yayi domin yaďan huta.
   Sai wayarsa ta hau wringing, mas'ud ne yake kiransa, ya ce, "ďan uwa ya akayine??, ya ce, "tambayata ma kakeyi?? To kafito muje wajen kamu.
   Nawaf ya yatsine fuska, miye kuma kamu??, dariya mas'ud yayi ya ce, "idan munje zaka gani, kai malam nidai hajja haka ta ce, "mini sai gobe.
   Dariya mas'ud yayi ya ce, "nima wasa nake maka, bari nabarka kayi barci ka huta, sai mun haďu anjima.
   Okey bye Nawaf yafaďa yana ďaga masa hannu kamar yana ganinsa.
____________________________
    A 6angaren yasmeen kuwa suna gidan su ameena anan ake zaman 'kunshi, gidan cike yake da 'kawayensu da dangin Nawaf larabawa da 'yan katsina, muta nen saudia dai basa jin hausa saidai turanci, dan haka gurin yazama dandalin turanci, tunda duk sunaji.
   Wata mai 'kunshi aka ďakko tanama amare yasmeen da Ameena ta iya sosai, saikuma wasu su biyu sunayima 'kawayen amre suma kam gwanayene, yasmeen bata cikin walwala, amma bataso dangin Nawaf su gane dan haka ta saki jiki anata hira, Ameena ce kawai take gane damuwarta.
   suma sai jida ita sukeyi, wata budurwace dai yasmeen takula batada walwala, tunda sukazoma tanemi guri ďaya ta zauna ita kaďai, (ummu habeeba ce) tana mutuwar son Nawaf, ita ce Nawaf ya ce, "ta cika 'kyau, kuma gsky ya faďa dan tafi sauran 'yammatan 'kyau gsky.
   Sai dare aka maidasu gidansu Nawaf,, Nawaf yana zaune a harabar gidan tareda sauran samarin 'yan uwansa na katsina dana saudia, anata hira da raha.
   Moto ci suka fara sauke 'yammatan, wajansu suka nufo suna mai farin cikin ganin Nawaf, gaisuwa aka shiga yi irinta al'adar larabawa, ummu habeeba kam saita tokare agefe ta'ki zuwa, Nawaf yana ganinta ya shareta, saida ga baya kuma ya mi'ke ya nufeta.
   Tana sanye cikin ba'kar jallabiya ta naďe kanta da ďankwalin kamar yanda larabawa keyi.
   Ya tsaya yana kallonta, ta harareshi nagode abi tafaďa tana turo baki gaba.
   Yay ďan murmushi minayi miki kike yimini godiya??, tai far da idanu, ta ce, "kaima kasani.
   Yay murmushi har fararen ha'koransa suka bayyana, yasan inda ta dosa amma saiya basar, ya ce, "kinga koma mikike ganin nayi miki to ki share ki tayani murnar aurena kamar yanda kikayi niyya tun farko, wananne zuwanki 9ja na farko ko??.
   Bataso aka daina waccan maganarba amma yazatayi tunda ya nuna bayaso, ta ce, "eh shine na farko, ahaka dai sukaita hirarsu, cikin harshen larabci.
_______________________KAMU.
   Yau takama kamu, kamu kuwa za'ayi irin na saudia ne, a harabar gidansu ameena za'ayi saboda yafi girma, an 'kawata gurin da kwalliya mai tsari, an baza 'katuwar darduma inda amarya da ango zasu zauna, agefe kuma an jere fararen kujeru inda sauran mutane zasu zauna.
    Hajja ce tazo da kanta ta ro'ki su umma akan abarasu suma suyi al'adarsu ta larabawa a wajen kamu, su umma sukace babu damuwa suma sunada iko akan komai aii.
    Wajen 'karfe 4:00pm na yamma aka gama shirya amarya cikin ba'kar doguwar riga ba'ka mai ďan karen 'kyau, gashinta yasha gyara an ďaureshi abaya wanda bai saniba saiya ďauka itama balarabiyar ce, dan NAFISAR KADUNA ce ta tsara mata kwalliya wadda amaren zamani suke yayi.
   Kowa ya hallara sai amarya datake falo tana jiran isowar ango, dan tare akeso su fito.
   Bayan kamar minti10 ango ya iso da tawagar abokansa, kowa ya zauna inda ya dace, aka raka ango inda zai ďakko amaryarsa.
  Kai kawai ya tura cikin falon batarda yayi sallamaba, tana zaune akujera hankalinta yana kan waya tana game.
    Ai gogan naku yana tsaye ya daskare dan ganin tsarin hallita irinta ubangiji, gsky koba komai yayi dacen mata 'kya'ky'kyawa rashin kunyartane kawai matsalarsa.
    Jitai kamar alamar mutum yana kallonta, ta ďago da sauri, Nawaf tagani tsaye kamar gunki yayi masifar 'kyau cikin kayan larabawa wando da riga farare, anyi musu kwalliya da golden ďin zare, sumarsa tasha gyara daka gansa kaga cikakken balarabe.
   Saida ta murguďa masa baki ta ce, "malam lafiya??, katasani gaba kana kallo, mi naci naka??.
   Hararar ta yayi ya ce, "ki ajiye makaman rashin kunyarki har zuwa nanda kwana uku, domin yanzu ina kan bin umarnin iyayenane, bazanyi abinda zai 6ata musu rai ba agaban ďumbin jama'ar dasuka tara.
    Yay wani murmushin mugunta, yaďora da faďin amma nanda kwana uku, ko ance ki kalleni kimin rashin kunya wlhy baza kiyiba, dan zanyi maganinki 'karamar mara kunya kawai.
  Ta buďe baki domin mayar masa da amsa sai aka turo 'kofar.....wata 'kanwar momcy ce Fateema, ta ce, "Abbuna ku ajiye wannan soyayyar taku sai nan da kwana uku dan yanzu mutane suna jiranku.
   Nawaf yaďan sosa gefen wuyansa ya ce, "sorry Abla(aunty kenan) muna zuwa.
   Ya juyo ya harari yasmeen sanan ya 'karasa wajenta, hannunta yakama, jikin yasmeen yay wani yarrrrrrr, shimadai gogan naku saida sassan jikinsa suka amsa, Abla fateema ta gyarawa yasmeen ďankwalinta tabaya, sannan ta rufe mata fuska da wani jan gyale.
    Nawaf ya ce, "Abla ai bata gani, idan ta faďi fa??.
   Abla tayi dariya kai ka bari tafaďi bayan kaine ďan jagora.
    Ya ce, "hakane idanma kin amince na ďauketa gaba ďaya naje na dire awajan.
   Abla fateema ta tuntsure da dariya ta ce, "babu ruwana.
   Yasmeen ta ce, "azuciyarta mugu saika nemi wadda zaka ďauka amma baniba.
   Catake a zuciya take magana bata san afili takeyiba dan Nawaf yana jinta, amma Abla bataji tunda da hausa take maganar kuma ahankali.
    Bayan sun fito gurin ya ďauki tafi, wajen kujerar da'aka tanadar musu mai ďan faďi sukaje suka zauna, saidai sun matsu juna sosai, yasmeen sai takurewa takeyi.
   Agaban kujera aka shimmfiďa dardumar daza ayi kamu.
   Ba6ata lokaci akayi addu'a ga ma'aurata, har yanzu fuskar yasmeen a rufe take.
   Nawaf tya ce, "malama nifa kin matseni.
   Dariya bin yabama yasmeen dan haka tayi murmushi, ta ce, "kanka akeji wai mahaukaci ya faďa ruwa.
   Nawaf yay murmushi mai sauti, kema za'aji kankine yarinya, dan ďazu ina jinki.
   Idan kagansu saika ďauka hirar arzi'ki sukeyi.
   Bayan angama addua aka fara shirin kamu, ango da amarya suka sakko 'kasa kan dardumar, suna fuskantar juna fuskar yasmeen arufe.
   Wani haďaďďen kwando aka ajiye agefensu wanda yake cike da turarurruka kala2 masu tsada da 'kamshi, abla ta su'ko tanama Nawaf magana acikin kunne da larabci, wanan yasa yasmeen bataji abinda suke faďaba, yay murmushi tareda jan kwandon gabansu.
    Saida akasaka wa'ka wadda akayima ngo da amarya amna da larabci, sannan aka bama ango umarni yashiga cikin gyalen da'aka rufe fuskar yasmeen dashi.
   Ya yaye ahankali ya rufa akansa, yazama su biyune aciki.
   Kan yasmeen na 'kasa Nawaf ya ce, "ina fata dai al'adarmu ta 'kayatar dake, taďan ďago ta kalleshi ganin ya kafeta da idanu yasa ta maida kanta 'kasa da sauri.
   Turare ďaya aka mi'ko masa yashiga fesama yasmeen, harda mugunta saida ya 'karar da turaren duka ajikinta, saboda 'karamar kwalba ce, fitinannen 'kamshin ya gauraye wajen.
    Ya yaye mayafin daga fuskokinsu, gaba ďaya gurin aka saka tafi, daganan kowa yataso saiya ďauka a kwandon yazo yaďan fesa musu, saida kowa ya fesa sanan aka rufe taro da addu'a kowa ya kama gabansa.
____________________________
    Yau aka ďaura auren mas'ud da Ameena, ALLAH yasanya alakairi mas'ud.
    Da yamma aka tafi bababan filin kwallo na kano anan za'a buga wasan biki, wanda (KANO PILLAS SUKA SHIRYA DOMIN KARRAMA ANGO) an tsara wasanne 6angaren ango da amarya, abokansa 'yan kwallo dasukazo daga 'kasashe daban2 da 'yan kano filas, 'kuria aka yi idan ka ďauki 6angaren ango kona amarya to suzaka bugawa.
    Wasankuwa ya 'kayatar dan har a labari aka nuna, antashi 8 da 5, ango 5 &amarya 8.
------------------------------------------
   Da daddare aka shirya kai amare ďakinsu anan naga kuka, yasmeen kuka take kamar ranta zai fita, sai nasiha da lallashinta akeyi, hakama ameena.
    Da 'kyar aka 6an6are yasmeen daga jikin umma, tanata kuka dafaďin bazatajeba itafa tafasa aueren, amma ina, tuni aka dannata amota, sai gidan ango.
   An mi'ka Amin gidansu mas'ud yasmeen kuma gidan su Nawaf, a ďakin momcy.
   Bayan kamar minti30 aka shiryasu zuwa wajen gagarumar dina da abokan Nawaf suka shirya, amma sun haďe harda mas'ud, ammafa wajen ya 'kayatu sosai.
   Amare sunsha shiri cikin rigunan aure,  yasmeen sai masifa takeyi, wai rigar arna, Nawaf yana jinta yay mata banza.
   Komai ya 'kayar agurin, amma wajen bada cake Nawaf saida ya ciji hannun yasmeen, tai wata 'yar 'kara, wadda tasa muta nen gurin ihun dariya a zatonsu duk cikin soyayyane lol.
    Sai shabiyu aka tashi, idanun yasmeen cike da barci, suka fiffito tana tangaďi, ga wani dogon takalmi data saka, tako goce zata faďi da sauri Nawaf ya tarbota ta faďo jikinsa, sai kawai ta lumshe idanu dan barci takeji.
   Girgizata yayi da 'karfi, ke dallah malam tashi karki karya mini hannu, inko ba hakaba zan sakeki ki faďi 'kasa ALLAH.
   yasmeen batasan yana yibama, Kausar ta ce abi! ka ďauketa kawai wlhy barci takeyi tagaji dayawa ne.
    Bayaso danginsa su gane komai gameda auren, dan haka ya sa6eta kawai sai ďakin momcy, ALLAH ya taimakesa ma 'yammatan ne a 6an garen momcy, kuma babu wadda yake jin kunya acikinsu.
   Ruwa ya ďauka a saman madubi da wata tasha tarage, yazuba ahannusa ya shafa afuskar yasmeen, tako kawo numfashi.
    Ahankali ta buďe idanu tana kallonsa, ya ce, "ke kitashi kicire wanan rigar, sanan ki kwanta yana gama faďa yafice, da'kyar ya iya tashi tacire, ta koma ta kwanta................

    Na ce, "asuba tagari yasmeen.










©2016



bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
         luv u oll my fan's
Share:

NAWAFF!! 20 to 22

[15/12/2016 20:51] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆





NA BILKISA IBRAHIM




Page 20

....da safe sukuku yasmeen ta tashi batada wata walwala, umma tana kula da'ita amma batace mata komai ba.
   Yaseer yagama shirin makaranta yafito bayansa goye da schoolbag, ya ce, "sisto wai mike damunki ne??.
   Yasmeen tad'an yatsine fuska ta ce, "ba komai bro's.
   Ya ce, "to bazakije makarantarba ne?, naji kince yau zaki koma kuma.
   Kwalla suka cikama yasmeen idanu ta ce, bazanjeba na fasa.
   Kin fasa kamar yaya??.
Zamewa tayi takwanta saman kujera batareda tace masa komaiba.
   Dole ya 'kyaleta ya fita danshima yaga yana neman makara.
   Umma tafito daga kichin tasamu yasmeen kwance tana hawaye, kusada ita ta zauna ta ce, "wai yasmeen mike damunkine??, ko bakida lafiya ne??.
   Yasmeen ta bud'e ido tana kallon umma, ta ce, "kaina yake ciwo tunjiya umma!.
   Umma ta ce, "o, ni kharima!! shine kuma bazaki fad'aba saidai kuka?, shidai d'an fari duk inda yake saiya nuna halinsa, to kitashi akwai magani ad'akin abbanku ki d'akko kisha.
  Jiki a sanyaye ta tashi taje ta d'akko maganin, koda tadawo sai ta tarar umma bata falon danhaka saita wuce d'akinta.
   Bayan madubi ta watsa maganin tana fad'in umma wannan bashi bane maganin ciwona, maganin ciwona yana hannun wancan mugun, ta 'karashe maganar da hawaye masu zafi.
   Na ce, "ALLAH sarki yasmeen yazakiyi aure kenan.

------------------------------------
    A6angaren Nawaf kuwa ko ajikinsa, yanzu hakama yana kwance a d'akin momcy bisa gado yanata barcinsa hankali kwance, dan tun asuba dayaje gaishesu ya kwanta.
   Dama wata sa'in yakanyi barci a d'akin momcy.
   Momcy ta kalli agogo 'karfe 9:30am ta ce, "modebbo yakamata katashi hakanan, gaban gadon ta 'karasa tana tashinsa, yad'an bud'e ido yana kallonta, saikuma ya maida ya lumshe.
   Ta ce, "Abbuna yakamata katashi hakanan kaga rana tayi, tafad'a tana jan baban yatsan kafarsa.
   Ahankali yatashi yana murza ido, ya ce, "momcy har 'karfe nawa nakai ina barci yau?, ta ce, "kalli agogo kagani mana, koda ya kalla saiya zaro idanu waje, ya ce, "kai ashe nadad'e ina barci, yaufa ko motsa jiki ban fitaba.
   Momcy ta ce, "hala kadad'e bakayi barciba jiya.
   Yad'anja tsaki, mara kunyar yarinyar nan ce ta hanani barci da da wuri.
   Yarinya kuma? a ina kenan?, momcy ta tambaya tana yatsine fuska, Nawaf yad'an sosa gefen wuyansa yana fad'in yasmeen fa momcy.
   Murmushi momcy ta saki ta ce, "o, ai nazata watace kuma.
   Mi'kewa yayi yana murmushi yanufi 6angarensa.
    Wanka yashiga yayi yafito yashiga shafa can, dangwala can, yagara jikinsa tsaf, yad'ora 'kananun kaya ba'kin wando da green d'in riga mai 'karamin hannu, yakawo ba'kar rigar sanyi mara hannu ya d'ora, yasaki hular abaya, yad'anja zif d'in sama kad'an amma baikai 'kirjinsaba, yayi 'kau sosai gsky, yafito yanata zabga 'kamshi.
   Gefen momcy ya koma, tana kichin suna aiki itadasu talatu, suka russun suka gaisheshi, sai satar kallonsa sukeyi, dan ita ladidi a haukanta har yanzu son Nawaf takeyi.
   Momcy ta ce, "modebbona sai ina kuma, yashafa sumar kansa data sha gyara, ya ce, "momcy wajen mas'ud zanje.
   Ta ce, "to break fa??, ya ce, "uhmm!!! Kumafa inajin yunwa gsky, bari nayi break sanan.
   Momcy ta ce, "to ladidi jeki had'a masa.....da sauri ya ce, "no, my sweet mom, tabarsa zanyi dakaina kawai, yafad'a yana yatsine baki, dan ganin ladidin awani hargitse, kuma momcy tana 'ko'kari wajen kula dasu da saimusu sutturu masu daraja, amma a banza.
   Shiyyasa bakomai Nawaf yakeso asakasu suyi masaba.
   danning yanufa yazauna abinci kad'an yaci yami'ke, lokacin momcy ta fito, ya ce, "mata yawuce.
   Ta ce, "adawo lafiya babban mutum.
   Nawaf yafita yana murmushi yanaso momcy ta ce, "masa abbu! ko babban mutum!, dayake sunan mahaifinta aka saka masa, shiyyasa papa yasaka masa modebbo saboda yana yima momcy kara.

Kai tsaye gidansu mas'ud yanufa, dukda yasan yana asibiti yanzu, wajen mami yashiga tana zaune afalo tana break dan yaran duk suntafi school, ta ce, "oyoyo my son!.
  Nawaf yazauna yana murmushi, yarissina yana gaida mami, ta amsa cikin fara'a, ta ce, "ina amarya?, saida yay 'kasa da kai yana wani sosa gefen wuya ya ce, "tana nan lafiya mami.
   Ta ce, "masha ALLAH agaishe mini da'ita, amma yakamata akawo mana ita mugani kafin ka koma, dukda muma zamuje muyima iyayenta godiya, dan ba kowane zaiyi kasadar bada d'ansa batareda yasan wanda yabamawaba.
   Nawaf ya ce, "karki damu mami za'a kawota insha ALLAHU.
   To ALLAH ya yarda.
Amin Nawaf yafad'a yana mi'kewa, ya ce, "mami bari na iske mas'ud a asibiti.
  To shikenan ALLAH ya tsare shima aii yau bai dad'e da fitaba dan ya makara.
  Nawaf ya fara tafiya yana fad'in ALLAH sarki, to bari na 'karasa.
   To Modeebbo nagode ALLAH yayi muku albarka kaji.
   Amin yafad'a yana fita.

Asibiti ya nufa wajen mas'ud, lokacin dayaje Nawaf yana duba marasa lafiya.
   Guri yasamu yazauna mutane sai kallonsa sukeyi, dan wasu sun riga sun sansa a magiji, saidai suna kokwanton shine koba shibane.
   Ga Nawaf baya son kallo dan haka sai yaji dukya takura, mota yatashi ya koma ya zauna, yad'an dad'e zaune amota yanata chattinga a awaya.
   Wata wayarsa tahau wringing, banza yay da wayar yaci gaba da chatting d'insa, saida aka 'kara kira sanan ya d'auka.
   Marakunya yaga ansaka, dan haka yay save d'in sunan yasmeen, saida ya ta6e baki sanan yad'aga, amma baiyi maganaba.
   Yasmeen ta ce, "assalamu alaika, muryarta can 'kasa tafad'a kamar mai mura.
   Sanin muhimmancin sallama yasa ya amsa.
   Sukayi shiru suduka harna tsawon minti2, ita a tunanintama yakashe saitaji ya ce, "dan wula'kanci kinsan bakida abin fad'a kika kirani!!.
   Cikin rawar murya ta ce, "plz dan ALLAH kabarni naje school d'innan wlhy idan kahanani zan cutu, kaga nayi asarar shekara d'aya da wata hud'u danayi ina zuwa kenan abaya.
   Plx duk abinda zakamin karka had'a da maganar karatuna.
   Banza yay mata kamar bazai tankaba, saikuma ya ce, "K!" Nifa ba'a sakani nayi abu dole, nafison idan na ce, "banason abu a 'kaleni, aii karatu ba dole bane ko?, duk kinbi kin wani dameni, kodai so kike kifita zuwa gidan tsohon mijinki daya sakeki ne??, yaja tsaki yana fad'in matsalar auren bazawara kenan!!!.
   Yasmeen ta rintse idanu dan jin yakirata bazawara, maganar tadaki zuciyarta sosai, wasu hawaye sukabi kumatunta, tayi shiru batarda ta 'kara firta komai ba.
   Shimadai shiru yayi baisake cewa komaiba, daga 'karshema saiya ajiye wayar batareda ya kasheba, kuma yana kallo itama bata kasheba.
   Daga baya yasmeen ta yanke wayar tana cigaba da kuka, ahaka ameena tashigo ta sameta, cikin mamaki take kallonta.
   Yasmeen ta ce, "ki zauna mana kika tsaya, Ameena ta ce, "ina naga tazama kina kuka, waike bazaki yarda da 'kaddaraba ne??, yasmeen ta share hawaye ta ce, "Ameena bazaki ganeba ne.
   To ganar dani Ameena tafad'a tana zama akusada yasmeen,, yasmeen ta gayama ameena yanda sukai da Nawaf tun jiya dasukazo, da kiran datayimasa da daddare, dakuma na yanzu, ta ce, "Ameena waini zai kira bazawara!!.
   Ameena ta ce, "kekam kinada abin haushi wlhy, to miye nawani kiransa saikace wadda take karatu aljanna, dammi bazaki share karatunba, idan kinada rabo nan gaba saikiyi, kuma ni banga abinyin kuka danya ce miki bazawara!!, aii kowa yasan keba bazawarar baceba ko??.
   To ki kwantar da hankalinki, dolefa kema saikin nuna masa baki damu dashiba sanan zaisan darajarki.
   Saidaifa 'kawata na tayaki murna, dan gay d'in handsome ne wlhy, saima yana gara kwallo a fili, gashi daga gani zaiyi soyayya.
   Harara yasmeen ta galla mata, ta ce, "kin ganki ko zaki fara.
   Ameena tayi dariya sorry my dear!, ammafa gsky nafad'a.
   Yasmeen ta ce, "Ameena yanzu kenan nayi wahalar banza a school.
   Bakiyiba wlhy tunda kin 'karu da wasu abubuwan,, kuma na tabbata zai barki kicigaba yana dai latsakine kamar yanda yasaba.
   Aiko saidai ya latsa kansa!, dan insha ALLAHU bazan sake yimasa maganarba.
   Hakan shine daidai 'yar uwa, nandai sukayita hira abinsu, Ameena tana 'kara koya mata dabaru.

,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,,
    To shima dai Nawaf bayan wasu 'yan lokuta tashi yayi yashige office d'in mas'ud batareda muta ne sun gama ganin mas'ud d'inba.
    Mas'ud yay murmushi, angon yasmeen kaine kake tafe.
   Harararsa Nawaf yayi ya ce, "kaifa sai ahankali, kulum saikaita abu kamar wanan 'katon kan naka baya kawo maka wuta.
   Dariya mas'ud yayi ya ce, "nida kai za'a tantance wanda kansa baya kawo wuta.
   Firij Nawaf ya bud'e yad'akko gwangwanin Moltina  yazauna yanasha.
   Saida mas'ud ya gama sallamar mutane sanan ya juyo gareshi.
   Nawaf ya ce, "likita bokan turai, dama haka mata suke safa da marwa a office naka.
   Mas'ud ya ce, "tomiye aciki?, baneman lafiya sukazoba?.
  Nawaf ya ce, "sunzo neman lafiya kukuma kuna kallesu ko?, ALLAH likitoci ma 'yan duniyane!!!.
   Hhhhh ku kuma 'yan kwallo 'yan lahira, malam kada kayi mana mummunar fassara kaji.
   Nawaf ya ce, "babu wani fassara alhaji, nikam gsky bazan bari 'katon banza yaduba mini mataba.
   Hhhhh mutumina har kafara kishi kenan?, lallai na yasmeen bada kanka asare kaje gida kace ya fad'i.
    Tsaki Nawaf yaja ya ce, "banza kawai wanda ba'a maganar arzi'ki dashi, ni kagama katuna min wai jiya da daddare saiga marakunyar nan takirani.
   Mas'ud yataso daga kwanciyar dayayi ajikin kujera, kai malam dgsk?, to mitace maka??.
   Nawaf ya ce, "magulmaci harda wani tasowa kai kaji gulma.
   To ai kaine magul macin tunda kaine ka kawo maganar, plz bani nasha bana son jan rai.
   Nawaf ya ta6e baki yashiga bama mas'ud labarin jiya, harda kiran data masa yanzu amota.
  Ido mas'ud yazaro, kai amma bakada kirki, dammi ka ce, "mata bazawara??.
    Nafad'a ba bazawarar ba ce?, A'a malam yasmeen ba bazawar bace, tunda ba a kaita gidan mijiba, anan aka d'aura yasaki aka baka.
   Nawaf ya kur6i moltina yana fad'in malam babu wani kwaskwarima daza kamin na yarda.
   Ai dama basai ka yardaba, d'an rainin hankali kawai.
  Yakamata yauma kashirya  da yamma muje, ko da daddare.
   Dawa zaka?, Nawaf yafad'a.
Dakai mana, ba matarka bace.
   Tsaki Nawaf yaja ashe zaku dad'e banjeba kuwa, jiyanma dan papa ya takura mini ne wlhy.
  Hhhhh malam wataran bama zansan ka lalla6a kajeba.
   Kai dallah saikace wani mara gsky.
   Dariya mas'ud yaytayi masa, ya ce, "malam inzaka fito fili ka fito kafad'a kana son yarinya, zaka wani zauna kana kauce2.
  Banza Nawaf yay masa ya d'au wayarsa yana dan danne............

Assalamu alaikum 
Kuyi ha'kuri yaudai babu yawa, 'yan nefa suna tamana iskanci da wuta.












©2016


bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        luv u oll my fan's
[16/12/2016 20:31] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 21 & 22

......yau tun farar safiya faisal yazo gidansu yasmeen, tana tana shara a tsakar gida yashigo, zumbur tami'ke tana fitar da numfashi cikin sar'kewa, saikace wadda tayi gudun fanfala'ke.
    A silo ya 'karaso gareta, hannu yakai da zummar ta6ata, ta kauce da sauri tana harara sa, cikin masifa ta ce, "kai malam bakada hankaline??.
   Murmushin takaici faisal yayi, ya ce, "indai akan sonkine to banida hankali yasmeen.
   Ya dur'kusa agabanta tamkar uwarshi, hawaye nata zirara bisa kumatunsa, cikin raunin murya ya ce, "yasmeen plz ki taimakeni ki dawo gareni, nine kawai nake miki soyayyar gsky, wlhy abinda kikaga yafaru sharrin shaid'an ne, da makircin hisham.
   Ta6e baki yasmeen tayi, ta ce, "kaga banida matsala da wannan, kuma ina mai gargad'inka daga yau karka sake koda kuskuren ta6ani, kai kanka kasan ada ban amince ka ta6a jikinaba bare yanzu danakeda aure....
   Da sauri abba yafito domin jin hayaniyar tayi yawa, turus yayi domin tozali da faisal tsugunne a gaban yasmeen.
   Abba ya 'karaso yana tambayar lafiya dai ko??.
      Suduka suka dawo da kallonsu gareshi, yasmeen tafara zubar da hawaye tana nuna faisal, shima dai faisal d'in kuka yake, ya mi'ke ahankali yaje wajen abba, dur'kushewa yayi agabansa ya kama 'kafafunsa yari'ke yana gunjin kuka.
   Hannu biyu abba yasa ya d'agoshi, haba faisal babba dakai ka zauna kana kuka?, miya faru kake kukane??.
   Hannu faisal yasaka ya share hawayen fuskarsa, yashiga zayyano kalaman nadama daban ha'kuri ga abba, da ro'konsa akan yabashi yasmeen a karo nabiyu zai gyara halinsa.
     Abba ya ce, "kayi ha'kuri faisal yanzu banida iko akan yasmeen, mijinta shike da iko da'ita, kayi ha'kuri ALLAH zai babaka wadda ya fita insha ALLAH.
   faisal ya langa6e kai yana hawaye, itama yasmeen hawayen takeyi dan jitake tana wani son faisal d'in yanzu.
   Ahaka yaseer da umma suka fito suka samesu, yaseer ya ta6e baki danshi faisal baya bashi tausayi ko kad'an.
   Itama umma lalashi da nasiha takeyima Faisal, amma faisal ba gane yaren nasu yakeyiba, danshi burinshi kawai abashi yasmeen, itace kad'ai nasihar dazatayi masa tasiri.
  Babu dad'ewa saiga hajiya jummai da dadyn faisal.
   Suma saisuka kama hawayen dan suna tausayin d'ansu, abba ya ce, "yakamata suje ciki dan wajen akwai sanyi.
   Bayan sun zazzauna afalo, su alhaji buba sukacigaba da ro'kon abba akan yabama faisal yasmeen a karo na biyu.
   Abba ya ce, "bansan irin bayanin dazan muku ku fahimceniba, amma yakamata ku gane igiyar auren yasmeen ba'a hannuna takeba, bakuma yanda za'ayi nakira yaronnan na tsareshi akan yasaki yasmeen, kofa na aikata hakan tofa auren bai sakuba tunda ni ba mahaifinsa bane.
   Kuyi ha'kuri muci gaba da yima faisal addu'ar fatan alkairi....
    Afusace alhaji buba yami'ke yana masifa, kai malam yazaka zauna kana jamana rai akan abinda baifi 'karfinmuba, harzaka wanice bayanda zakayi kasaka yaron yasaki yasmeen, shin wai bakada tausayine, baka ganin halin da d'ana d'aya tilo yashigane??, kodan kuna ganin 'yarku tanada 'kyaune??....
   Abba ya 'katse Alhaji buba ta hanyar d'aga masa hannu🖐🏻, kaga karka gaya mini magana, ai bani na ce, "faisal ya saki yasmeen bako??, ko kai ka manta da wula'kantani dayayi acikin taron jama'a ba yasaki tawa d'iyar ba!, sannan wanda kake magana na saka yasaketa shine ya share mana hawayenmu!!, to kuma saboda son zuciya saina sakashi yasaki yasmeen saboda faisal ya aureta???..
   Hajiya jummai ta ce, "dan ALLAH kuyi ha'kuri, agaban yarafa muke, da'kyar suka lafa da hayaniyar dasukeyi.
   Alhaji buba ya ce, "kutashi mu tafi, kuma inaso kasaka a zuciyarka ka mallaki yasmeen ka gama, yana gama fad'a yaja hannun faisal da hajiya jummai sukayi waje.
   Kuka yasmeen tafasa ta zube afalo tana birgima, umma tasa hannu ta d'agota tana lallashi, abba ya ce, "mamana kiyi shurinki, babu abinda suka isa suyi miki, kuma nanda sati uku insha ALLAHU kina d'akin mijinki.
   Ni ban ta6a ganin jahilan mutane irinsu alhaji buba ba, in banda jahilci yazakuce wani yasaki matarsa d'anku ya aura, bayan kuma shine yafara tozartamu agaban mutane yasiki yarinyar atake agurin da'aka d'aura musu aure.
   Umma ta ce, "babu wani jahilci malam son cuciyane kawai yake damunsu, 'kila atunaninsu mu bamu san darajar 'yarba ko???.
   To aiko zanyi maganin son zuciyarsu kwananan.

Yaseer kuwa d'aki yashige yashiga kiran number d'in Nawaf, saidai yayi masa kira yakai biyar bai d'aukaba, dan haka ya ha'kura yay shirin makaranta yatafi.
________________________

   Alokacin da yaseer yake kiran Nawaf baya kusada wayoyinsa,   yana wajen motsa jiki dayake fita akowace safiyar duniya, inhar yana 9ja.
   Sai wajen 'karfe 8:00am yashigo gidan jikinsa sanye da farin JC, gajeren wando da 'karamar riga mara hannu, 'kabarsa sanye da takalmin 'yan kwallo, dad'an gudunsa yashigo gidan, yasaka robar ruwan dake hannunsa cikin bola, key yasa yabud'e d'akinsa ya shige.
   Saida yasha ruwa sosai sannan yazauna yana zufa ya fitar da huci mai zafi daga bakinsa, ya kwantar da kansa saman kujera ya lumshe idanu, yakai minti5 ahaka daga bisani ya cire takalman 'kafarsa ya ajiye.
    Bedroom d'insa yashiga, yacire kayan ya jefa cikin wani dogon kwando, ya bud'e wata 'yar durowa dake kusada bayi (bathroom) tawul ne aciki kala2, yad'akko kalar yellow ya d'aura daga 'kugu zuwa guywa.
   Wanka yashiga, ammafa ya dad'e, dan nikam harna fara gajiya ma da jira, ya kai tsawon minti50 sannan yafito, d'aure da tawul d'insa, hannunsa ri'ke da 'karami fari yana goge sumarsa.
   Zama yayi yashiga tsara ado, na ce, "kai gay d'inana d'an kwalisa ne gsky.
   Kwalliyarma yakai tsawon lokaci yana tsarata saikace mace lol,  daga 'karshe yafito sanye cikin 'kananun kaya ya d'ora tafkekiyar rigar sanyi jaa mai 'kyalli saboda yanayin sanyin garin, sai zabga 'kamshi yakeyi.
   Zama yayi yay break, sanan ya jawo phones d'insa, ya kira wad'anda suka kirashi baya nan, haryazo kan number d'in yaseer, kira yashiga yi amma ba'a d'agaba, yasake kira, harta kusa katsewa aka d'aga.
   Mai makon yaji muryar yaseer sai yajita yasmeen, cikin muryarta mai za'ki ta ce, "mai wayar baya nan!.
   Nawaf ya ce, "ina yaje??.
 Ita bata gane Nawaf bane, ta ce, "yaje school, amma idan yadawo za'a sanar masa.
   Daya kula bata ganeshiba saiyayi niyyar zolayarta, ya ce, "toke wacece?.
    Saida taja numfashi sanan ta ce, "yayarsace.
   Saida yad'an ta6e baki sanan ya ce, "hummm kodai 'kanwarsa, dan dagajin muryarki "k, yarinya 'karamace.
    Cikin 'kufula yasmeen ta ce, "kai malam sai anjima, kabi duk ishii mutane da surutu, d'if ta kashe wayar.
    Dariya sosai Nawaf yayi, ya ce, "kai yarinyarnan 'yar bala'ice wlhy, dawata muryarta kamar ta gyare.
   Yashiga kwaywayon muryarta yana dariya, tamkar mai kallon film ko wa'ka.
   
--------------''''''---------------------
   Da yamma abba ya kira papa awaya yay masa bayanin komai, game da abinda yafaru da safe, maganar ta bama papa mamaki saikace a wasan kwaikwayo, kasaki mace kadawo kana hauka wai kana sonta.
    Papa ya ce, "karya damu zuwa gobe zaizo suyi magana, yasmeen ta tare kawai agindasa, ta 'karasa karatun a d'akinta.
   Papa yaji dad'in hakan, yakuma yi farin ciki, koda yagayama umma itama murna taitayi dan wanan shine kawai maganin son zuciya irin na alhaji buba da d'ansu.
    Yasmeen kuwa batayi murna da hakanba, dan itafa har yanzu zuciyarta bata wani saisaita mata zama da Nawaf ba, tana masa kallon mugune mara mutunci, darashin girmama d'an adam.
   To yasmeen koma dai miye?, lokacine zai nuna wannan.

Da yamma ta saci jiki tashige gidansu Ameena, umma tana d'aki bata saniba, tazata yasmeen d'in tana d'akine, tunda tasaba yini a d'aki, bare yau ana sanyi a garin.
   Yasmeen kam tana can sunata hirarsu itada ameena da bello yayan Ameena.
   Saida taga ana kiran wayarta sannan ta mi'ke zaram, number yaseer tagani, tad'aga da sauri tana fad'in bro's yaya dai??.
   Ya ce, "kina ina?, anata nemanki.
   Yasmeen ta gwalalo idanu waje tana fad'in naga ta kaina ganinan zuwa.
   Ameena ta ce, "kije kisha fad'an umma, dan satar fita kikayi, kuma akwai zunubi
   Hararta yasmeen tayi tafice da sauri batareda tabama Ameena amasaba.
   A 'kofar gida tayi turus, dan ganin Nawaf jingine a jikin mota, kansa a 'kasa yana danna waya, yana sanye cikin shadda milk, d'inkin iya guywarsa, yayi 'kyau sosai sai 'kamshin tutare yakeyi, yaseer yana gefensa tsaye.
   Jiki a sanyaye ta 'karasa wajensu.
   Yaseer ya ce, "sisto wai dama kina nan gidan tund'azu??.
   Kai kawai ta d'aga batare da tayi magana ba, ta ce, "miyasa kuka tsaya nan??.
   Yaya ne ya ce, "mu tsaya muga inda zaki fito.
  Yasmeen ta kai dubanta ga Nawaf wanda tunda tazo ko d'ago kai baiyi ya kalletaba, yanata danna wayarsa kamarma baisan dawata yasmeen a wajenba.
  Saida tad'an turo baki sanan ta ce, "to kumuje mana, Nawaf ko motsi baiyiba dan haka yasmeen tayi gaba abinta.
   A falo ta iske umma, umma ta hauta da fad'a, itadai yasmeen fad'i take umma kiyi ja'kuri ALLAH gidan ne naji shiru shiyyasa na fita.
    Tsaki umma taja ta ce, "aii yayi miki 'kyau tun d'azu mijinki yazo yake jiranki, kinacan inda ba a aikekiba.
   Shiru yasmeen tayi dan tasan batada gsky.
   D'an abinda umma tahad'a yasmeen ta d'auka tanufi falon abba, azaune ta tadda Nawaf yana kallo, ita a zatontama har yanzu bai shigoba.
   Ta dire tiren a gabansa sanan ta koma nesa dashi ta zauna.
   Suduka kowa ya share kowa, dan Nawaf har yanzu ko kallonta baiyiba, itama saita shareshi taci gaba da harkarta.
   Sunkai tsawon minti30 ahaka, yasmeen ta daure ta ce, "nikan gsky inada abinyi dan haka zan 'kara gaba.
    Harara ya watsa mata batareda yayi maganaba, ya d'auki remote ya 'kara 'karan tv dan bayaso umma taji hayaniyarsu, tsam ya mi'ke yanufo inda take zaune.
   Atu naninta zama zaiyi, dan haka tashiga matsawa tana 'kan'kame jiki.
   Tsaki Nawaf yayi ya'karasa gabanta, gashinta ya dam'ko ya matse da 'karfi, gaba d'aya jijiyoyin kan yasmeen suka fito, tasaki wani walallen kuka tana 'ko'karin ri'ke hannunsa, gashi ya toshe mata baki da hankacif.
   Ya zare mata fararen ida nunsa masu girma, ya ce, "wayace kifita??
    Yasmeen babu damar yin rashin kunya, saidai hawaye dake fita daga idanunta, ya saki gashin yana fad'in gobe idan kin tashi ki kuma fita bada izininaba, kiga abinda zan miki, baki ta murgud'a masa ta ce, "mugu ALLAH saiya saka mini.
   Hannu yakai zai kama hannunta ta kauce da sauri, yaja gefe danya kamata saita fad'a jikinsa, mai makon ya ri'keta saiya kama d'an yatsanta, tako daddage ta galla masa cizo a d'ayan hannunsa.
   Da sauri ya saki hannunta yana yarfe nasa hannun, abinka da fari gurin har yayi jajur, ga shatin ha'koranta awajen rad'a2.
   Nawaf ya rintse ido yana murza wajen, dariya sosai yasmeen takeyi, ta ce, "kaji idan da dad'i kaima.
   Ya bud'e ido yana cije le6ensa na 'kasa, har yanzu wajen zafi yake yi masa, ya ce, "ni kika ciza ko??.
   Baki ta murgud'a masa, gobema idan ka 'kara gwada mini mugunta saina yimaka wanda yafi wanan, mugu kawai.
   Wani murmuahi Nawaf yasaki mai kamada ya'ke ya ce, "banza kuriya, wlhy idan na kamaki zaki gane kuranki.
   gwalo yasmeen tayi masa ta ce, "saidai mu gane kurenmu wlhy.
 Kwafa yayi ya ce, "yarodai baisan wutaba saiya taka.
  Nunata yayi yana fad'in kuma wlhy kifad'ama wannan jahilin daya sakeki aka 'ka'kaba mini, daga yau nasake jin yazo gidanna saina sa an 6atar dashi, dagashi har jahilin ubansa, idan kunne yaji jiki ya tsira.
   Kemad'in bance karki 'ki fitaba, saidai idan kika cigaba da karya dokata zaki cigaba da shan ba'kar wahala ne, danni ba sa'anki bane.
   Yana kaiwa nan ya fice dama har anfara kiraye2 sallar magriba.
   Dariya tasaka harda tafa hannaye, ta ce, aii dai kasha cizo azzalumi kawai, aii wlhy na daina 'kyaleka kana sakar min kwanjinka a banza, idan kafi karfina aibakafi karfin cizoba, zakayita shan cizone harsai hannunka yakoma da zanen ha'korana ko ina.

_______________________
   D'aki tanufa tayi sallar magriba, tana nan zaune tana karatun alkur'ani har akayi sallar isha'i.
   Bata fitoba dan tasan umma tana ciki da ita, saida tabari yaseer yadawo sanan tafito, ganin baya falo yasa tanufi d'akinsa.
   Saman gado ta tarar dashi ya bud'e waya 'katuwa akwalinta yanata kallo yana murna, NAWAF ne ya sayamasa.
   Yasmeen ta murtike fuska, cikin masifa ta ce, "yaseer yaushe kazama munafiki, kai har ka fifita bare akan ni 'yar uwarka??.
   Ubanwaye yasaka gayama wancan mugun faisal yazo gidanan da safe??.
   Yaseer ya had'e fuska, kai kaji sisto d'innan koda ban fad'aba ma aii abba ya fad'ama abbansa, kuma nasan zai gaya masa, zaki wanizo kina zagina, yafad'a yana turo baki gaba.
   Tsawa yasmeen ta daka masa dallah malam rufe min baki, munafiki kawai, wanda bai iya ri'ke sirrin gudansuba, saboda an kawo maka waya kazauna kasaki baki kana zuba gulma da tsigudidi.
   Wlhy daga yau nakuma jin maka manciyar wanan maganar saina daka ka agidanna, idan kaji 'karya ka 'kara, sakarai kawai, tayi waje.
   Yaseer yabita da kallo yana murgud'a baki, an fad'a d'in, kumani ba magulmaci bane.
   Kinason mutum kina wani kauce2, ai tuni na harbo jirginki ooooh, yafad'a yana dariya. 
   
    Nawaf kam cikin haushi yaje gida, koda yayi sallar magriba da isha'i bai nemi mas'ud ba, dan yanada aikin yamma shiyyasa basuje tareba.
    D'aki yadawo yay kwanciyarsa, kad'a2 saiya kalli inda yasmeen ta cijeshi, wajen yayi jajur.
   Yasaki murmushin mugunta, wlhy yarinya sakinyi dana sanin cizonan dakikamin, mara kunyar banza kawai, yay kwafa yana gyara kwanciya.
    Ahaka mas'ud yazo ya sameshi, ya zauna yana fad'in angon yasmeen kabarota lfy??.
   Banza Nawaf yay masa.
       Mas'ud yay murmuahi oh baza'a amsa miniba angon yasmeen??.
   Cikin masifa Nawaf ya ce, "kasan ALLAH mas'ud ka daina had'ani da wanan yarinyar inkuwa ba hakaba zamu sami matsalane.
   To miye dan munsami maysalar alhaji???, wata ran basai mu shiryaba.
    Nawaf yatashi zaune yana fad'in wlhy mas'ud saina koyama yarinyar nan hankali kwanannan.
   Hummm mitayi maka dazaka koya mata hankali.
  Hannunsa ya nuna masa ya ce, "kalla ka gani waini yarinyarnan ta ciza.
   Mas'ud yatuntsire da dariya, kai saikace wata kura??.
   Ai tafi kura Nawaf yafad'a yana gyara zama, nan yabama mas'ud labarin abinda ya had'asu.
   Mas'ud ya ce, "Ah wanan laifinkane alhaji, aiba haka ake hukunta mutumba idan yayi laifi.
    Tsaki Nawaf yaja ya ce, "wanan kuma matsalar kace.........................







©2016




Bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
         luv u oll my fan's
Share:

NAWAFF!!! 18 & 19

[14/12/2016 12:55] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM




Page 18

BAYAN KWANA BIYU 
       Najeria suka buga wasa da gini, sai dai wanan wasa baiyima Najiria dad'iba, dan antashi 1-1 amma yau ba Nawaf ya zura mana kwalloba.
   Dana kalli Nawaf d'inma sainaga baya cikin walwala, na ce, "yau miskilanci 'yan mazan ya motsa.
  
KANO
    faisal ma an sallamesa saidai har yanzu yana zuba sambatunsa, duk ya rame yayi ba'ki, sai ro'kon iyayensa yake akan subarshi yaje gidansu yasmeen, 'kila idan yabata ha'kuri ta ha'kura tadawo gareshi.
   Tun iyayen na d'aukar lamarin nasa wasa har suka koma tausayinsa, idan yana surutai hajiya jummai har kuka takeyi masa, gabad'aya sun rasa kansa, bayada wani zance saina yasmeen.
    Hajiya jummai ta ce, "Alhaji kodai zuwa zamuyi mu ro'ki iyayen yasmeen ne?, 'kila su tausayamana su warware wancan auren, subama faisal.
   Alhaji buba yay shiru yana nazarin maganarta, zuwa can ya ce, "kina ganin hakan zata faru?, kuma idan sun yarda shi wanda ya auri yasmeen d'in zai amince??.
   Hajiya jummai ta ce, "to Alhaji saimu gwada, kuma ko biyansa yakeso muyi ai sai mu biyasa ko nawane, indai zai saki yasmeen faisal ya aura, karmuzo d'anmu ya susuce akan abinda baifi 'karfin saba.
   Na ce, "hummm aikodai wannan tafi 'karfinsa, dan ba kowacce mace kud'i ke iya sayaba.
    
KIRA
    mu mata munada al'adar cewa sai mun auri mai kud'i, kuma hakan ba daidai bane, kedai amatsayinki na d'iya mace kamata yayi kiyi addu'a ALLAH yabaki miji nagari mai 'kaunarki da gsky.
    Wlhy masu kud'innan damuke hari ba kowane yadamu da fita ha'k'kin iyalinsaba.
   Musamman ma mazan hausawa, idan suna samun kud'i sunfi maida hankalinsu ga neman kud'in fiyeda 'ya'yansu da matansu.
   Wani saiya had'a wata uku zuwa hud'u baya 'kasar, yabar matar cikin damuwa da kewa, shikuma yanacan tareda karuwai a hotel, to dan ALLAH miye ribar auren irin wanan mai kud'in.
   Idan baki kai zuciya nesaba saiki fara bin mazan waje da aurenki, ALLAH ya kiyayemu.
   Idan kuwa kika auri talakannan daba kiso, duk inda yafita zuwa yamma yadawo, zai kula dake zai kula da 'ya'yanku, UBANGIJI ALLAH yasa mu gane amin.

   Yasmeen kuwa tana cikin damuwa, tanaso ta koma makaranta amma abba ya ce, "tabari mijinta yazo ta gaya masa, tayi kukan harta gaji dan tanaso takoma makaranta gashi anata wuceta a lectures.
   Yau suna zaune afalo harda umma da abba, sunata hirar gida, abba yana cewa lokaci kad'an yarage suje kwangwalan dansuga dangi dangi su gansu, yaseer yanata murna, amma yasmeen ko motsi batayiba.
   Abba ya ce, "mamana lafiya dai??, tai firgigit tana fad'in lafiya lao abba, ya ce, "inafa lafiya munata magana amma ba'kya tare damu, zonan mamana naji damuwarki kinji.
   Jiki a sanyaye yasmeen ta tashi taje kusada 'kafafun abba ta zauna, yadafa kanta yana fad'in mike damunki? fad'amin!.
   Saida ta matso hawaye sanan ta ce, "abba makaranta ta.
  Tofa, abba ya fad'a, yanzunan dama saboda bokonnan kika takuri kanki, to aii na ce, "ki bari mijinki yazo saikuyi magana.
   Babansa yakirani d'azu ya ce, "gobe zasuzo insha ALLAHU, dama baya nanane shiyyasa bai zoba.
   Cikin sigar lallashi ya ce, "kiyi ha'kuri kinji mamana, ki d'auki duk abinda ya sameki amtsayi 'kaddara.
   Yasmeen ta d'aga kai tana hawaye,. Abba ya ce, "yauwa mamana ALLAH yay muku albarka kunji, ya tsare mana ku.
   Umma da yaseer sukace amin.
 Daga nan yasmeen tad'an saki jikinta tana d'an saka baki a hirar tasu, amma ba sosaiba.

NAWAFF
   yau da yamma Nawaf ya iso kano, zaid'an kwana biyu ya koma abuja, kafin aci gaba da wasa.
   Sunyi murnan ganinsa, momcy ta shafa kansa cikin hausarta dabata gama nuna ba ta ce, "my dear duk ka rame wlhy, mike damunka haka??.
   Nawaf yad'an cije leb'ensa na 'kasa ya ce, "momcy wanan auren da papa yay min mana, ALLAH bazan 6oye mikiba bana son aurenan momcy, ya'karasa fad'a cikin raunin murya.
    Momcy ta kwanto dashi gefen kafad'arta ta ce, "kayi ha'kuri Abbuna ina ji ajikina wanan auren Alkairine a gareka, kuma yanda su Abdallah suke bani labarin matar taka da gidan data fito duk masu mutuncine, da tarbiyya.
   Banaso akan aurennan kabari sa6ani yashiga tsaka ninka da papan ku, ka danne zuciyarka ka koyi son matarka tunkafin tadawo hannunka.
   Zanta tayaku da addu'a insha ALLAHU, itama ALLAH yacusa mata sonka kaji, dukda nasa modeebbona abin sone ga kowacce mace, babu macen dazata gansa ta ce, "bataso, momcy ta 'karashe maganar da tsokana.
   hannu yasa ya rufe idanunsa don kunya.
   Momcy tayi dariya, ato idan kuma bakaso mutafi saudia kaza6a cikin dangi, gama ummuhabeba nan kullum damuwarta tana kanka, kaga sai kawai musha biki.
   Nawaf ya zaro idanu ya ce, "momcy yi shiru kar papa yaji, danni bana ra'ayin zama da mata biyu, kuma ma bana son ummuhabeeba tacika 'kyau dayawa nikuma bana son macen data cika 'kyau gsky.
    Tofa, momcy tafad'a, wanan kuma wani sabon idea ne na rashin son auren 'kya'ky'kyawar mace??.
   Nawaf yay murmushi har fararen ha'koransa suka fito, ya ce, "A'a my sweet mom ra'ayina ne nidai!!!....
   Abdallah ya shigo da sallama, Nawaf ya ce, "ka amso mini?, eh yaya na amso, na kaimaka d'akinka banyi zaton kana nanba aii.
  Okey babu damuwa, amma yau miya hanaka zuwa islamiyya ne??, Abdallah yad'an sosai gefen wuyansa yagyara zama zai shararo 'karya.......Nawaf ya dakatar dashi ta hanyar d'aga masa hannu kaga basai kafad'aba, dan nasa 'karya zakamin.
   Momcy ta ce, "aii dama jira nake kadawo na sanar maka kwata2 Abdallah baya son zuwa islamiyya, danshi bai biyo halinkaba, tun kana shekara sha biyar ka sauke ALKUR'ANI, amma Abdallah har yanzu baikai ko izufi 50 ba nakula Anwar ma yakusa kamosa.
    Harara Nawaf ya watsa masa, ya ce, "wato kai nakula kaine mara ji d'in gidanan ko?, wlhy ka maida hankalinka kajiko, ku a tunaninku karatun boko shine wayewa ko??, amma ai baka ta6a fashin makarantar bokoba ko??.
  Kun manta karatun bokon iyakarsa nan duniys, karatun islamiyyar dabaku basa muhimman cinba shine zai zame mana tudun dafawa awata rana mai cike da rud'ani.
   Wlhy daga yau nasake jin bakaje islamiyyaba sai ranka yayi matu'kar 6aci, tashi kabani waje sakarai kawai.
  sum sum Abdallah yatashi yashige d'akinsa yana zum6ura baki.

WASHE GARI
    Tunda wuri umma da ameena suke hidimar had'a abubuwan tarbar ba'ki amma banda yasmeen data shige d'aki wai batada lfy.
   Dan haka umma taje ta nemo Ameena 'kawar yasmeen d'in dan ta tayata.
   Yasmeen kuwa tana d'aki cikin fargaba da damuwa, wai yau zataga mijinta, ko zaizo mata da mutuncine?, kokuma sa6anin hakan??.
    Har zuwa azahar tana d'aki tana kullawa da kwancewa, dakuma fad'uwar gaba.

a wannan lokacin kuwa Nawaf yanacan anci kwalliya cikin 'kananun kaya, ya fito shida mas'ud sai zabga 'kamshi suke, 6an garen su momcy suka nufa, afalo suka iske momcy da papa dasu Anwar.
   Papa ya ce, "kunyi 'kyau sai dai modeebbo koma ka canjo kaya wad'anan basu yiba.
   Nawaf yabi jikinsa da kallo, papa miye aibun wad'anan kayan yafad'a cikin shagwa6a.
  Papa ya ce, "aibunsu dasuka kasance 'kananun kaya, kai bakaga shigar da d'an uwanka yayi ba mas'ud.
   Gidan surukai zakujefa, kuma yau zasu fara ganinka, sai kaiwai suganka da 'kananun kaya kamar d'an yahudawa, maza kaje ka canjo shadda ina nan ina jiranka, dan kuna 'kara 6ata lokaci.
   Badan Nawaf yasoba yakoma ya sako farar shadda 'kal d'inkin zamani, harda saka hula, kai yayi 'kau wlhy, saiya fito asalin balarabensa, dan dakaga Nawaf dole ka kirashi ci kakken balarabe.
   Nawaf dogone sosai yanafa jikin 'karfi sabida training dayakeyi, yana da suffa irinta kosashshen xaki, daga sama 'ka'k'karfane sosai cikinsa ad'ame tamkar baya cin abinci, farine amma ba tas ba, kalar fatarsa irinta larabawace jaa kenan zamuce, yanada suma mai yawan gske mai kuma laushi d 'kalli dukda tanashan gyara da mayuka masu tsada, yanada d'an saje wanda ya tsaya iya kumatinsa dai dai kunne, ida nunsa masu 'kyau da haske ga girar ido zara zara, kai komaidai yaji d'ammmmm.
     Papa yay murmushi yauwa ko kaifa modeebbo, yanzu kaga shine mutuntawa, sai kuje banaso naji wani abinda zai 6ata mini rai, kuma ku sayi wani abu akai mata kar aje hannu rabbana, ku gashe mana dasu.
   Mas'ud ne kawai ya amsa.
Abdallah ya  ce, "yaya dan ALLAH zanje.
   Harara Nawaf ya watsa masa wadda tasakashi saurin rufe baki.
   Sukuma suka fice.
Papa ya ce, "huum d'an yanzu saka barsa da halinsa kawai.

Amota mas'ud ya ce, "mutumina baka ta6a kwalliya irin ta yauba wlhy, gashi yau ranar shan mamakice.
   Nawaf ya ce, "wane irin mamaki kuma bro's??, wani murmushi mas'ud yayi, ya ce, "sai munje zaka gani!".
    Baki Nawaf yad'an ta6e yana fad'in ni babu wani abin mamaki dazan gani malam.
   Mas'ud ya tuntsure da dariya   , banza Nawaf yay masa.
       Sun isa 'kofar gidansu yasmeen, mas'ud ya ce, "ka kirata kace mun iso mana.
   Harara Nawaf ya sakar masa, ya ce, "lallai ashe zamu kwana anan kuwa, indai har saina kirata ne.
   Girgixa kai kawai mas'ud yayi yad'akko wayarsa ya kira yaseer ya ce, "yaseer gamu munzo.
   Yaseer ya ce, "to yaya ku shigo falon Abba.
  Mas'ud ya kalli Nawaf bayan ya gama wayar, ya ce, "to saika fito ance mu shiga, baki Nawaf ya ta6e ya bud'e motar yafito.
   Cikin gidan suka danna kai, har zuwa 'kofar falon abba dake harabar gidan ta baya, babu yanda za ayi kaga masu gidan dan 'kofar falonsu tana can cikin lungu, Tunda suka shigo 'kamshin turare falon da abinci yake dukan hancinsu, suka zazzauna.
    Babu dad'ewa yaseer ya shigo da sallam suka amsa, idanu ya zaro waje dan mamaki, ya 'kara murza idaninsa, yagadai kwarai dgsk modeebbo ne, ya ce, "yaya mas'ud dan ALLAH dgske ida nuna sukeyi??.
   Murmushi mas'ud yayi dan yagane me yaseer yake nufi, ya ce, "gsky suka nuna maka yaseer, modebbone dai daga kasani yana gara mana kwallo a afili.
   Nawaf yay murmushi shima ya ce, "zonan 'kanina!, jiki a sanyaye yaseer ya 'karasa wajensa, hannunsa yakama ya zaunar dashi kusadashi, kasannine??, yaseer yay dariya, aiko shekaran jiya saidanaga wasanka, wlhy narasa irin murnar dazanyi danna burge kaina, amma ALLAH ngd maka daka nuna min wanda nake 'kauna ido da ido.
   Nawaf yaji dad'i sosai, danhaka ya rungume yaseer shima.
   mas'ud ya ce, "yaseer sisto d'inkafa?.
  Yaseer yami'ke yana fad'in kuyi ha'kuri farinciki ne ya mantar dani bari na kirata!!.
  Mas'ud ya ce, "to karka gaya mata abinda kagani fa.
   Cikin dariya yaseer ya ce, "bazan fad'aba ALLAH.
       yasmeen zaune afalo tana jiran yaseer yazo yakirata, tayi 'kyau cikin les green ta d'ora farin mayafi dukda ba kwalliya tayiba amma tayi bala'in 'kyau.
   Muskarsa cike da fara'a ya ce, "sisto kije suna jiranki, bai jira amsartaba yashige d'akin umma domin kai mata rahoton farin ciki.
    Jiki a sanyaye ta tashi tanufi falon, tad'an dad'e a 'kofar falon 'kirjinta yana dukan tara2, daga 'karshe tayi kundun bala tashiga da sallama, cikin siririyar muryarta.
   Mas'ud ne kawai ya amsa, dan Nawaf yana wayane.
   Ta zauna suka gaisa da mas'ud yabata ha'kuri akan kwana biyu basu zoba, tayi d'an mumushi tana fad'in babu damuwa aii.
  Mas'ud sai dariyar mugunta ya ke k'asa2, ya'kagara yaga yanda za'a had'u.
    To nimadai 'yar rahoto abinda nake jira kenan.
   Bayan Nawaf yagama waya ya juwyo yana kallon mas'ud, mas'ud ya ce, "lafiya dai ko??.
   Harar sa Nawaf yayi ya ce, "ban saniba.
    Mas'ud ya tuntsure da dariya, cikin dariya ya ce, "Amarya ga angonki na kawo miki yau dai.
  Kan yasmeen a'kasa ta ce, "ina yini?, 
   Lafiya. kawai Nawaf yafad'a yana wani yatsine fuska.
   Yasmeen ta mi'ke domin ta basu ko ruwane dan takula ko bud'e abincin basu yiba.
   Ta 'karaso kanta a'kasa, shi Nawaf ma waya yake latsawa, gabansu ta dur'kusa ta tsiyaya lemon kwakwa ta mi'kawa mas'ud.
   Ta zuba wani ta mi'kawa Nawaf dake latsa waya abinsa.
  Mas'ud ya ce, "malam ana baka abufa, ayatsine Nawaf yad'ago zaiyi magana, saiya daskare a gurin.
   Cikin in ina ya ce, "kai ba dai ke ba ce.....
   Itama cikin tsoro take kallonsa, sudukansu 'kirjinsu yana bugawa da tsananin 'karfi, hannun yasmeen sai rawa yake, gashi takasa ajiye lemon.
   Shima Nawaf cikin rawar hannu da baki yake nuna yasmeenamma yakasa cigaba da furta komai.
    Shiko mas'ud sai dariya yakeyi yana tafa hannaye.....................








©2016


Bilyn Abdul
     Mrs Abdus'salam
         Luv u oll my fan's
[14/12/2016 20:02] bilyn Abdul: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page 19

....Lokaci d'aya suka mi'ke kowa yana kallon kowa, idan kagansu saika d'auka kallon soyayya sukema juna, yasmeen ce tafara janye idanunta tana zubar da hawaye, saikuma tad'ago da sauri tana kallonsa.
   Nawaf yagyara tsayuwarsa tareda 'kara d'aure fuska ya ce, "lallai yarinya dama kece papa ya 'ka'kaba mini, tofa ina mai baki shawara 'yammata tun wuri ki hanzarta fad'a musu su warware wanan auren ankuwa ba hakaba wlhy zaki gwammace kid'a da karatu, ya 'kare fad'a yana huci, kamar wanda yake afilin danbe.
    Cikin tsiwa yasmeen ta harareshi ga hawaye share2 a fuska, ta ce, "ai basai nasha wahalar sanar dasuba malam, wannan damar tana hannunka, idan kaso nanda minti d'aya saika datse igiyar da aka d'auramini ta 'kaddara dakai, tsowww... taja tsaki.
   Wani 'kududun ba'kin ciki ya tokare ma'koshin Nawaf, wlhy badan yanajin tsoron fushin mahaifansaba da agurinnan zai saki yarinyarnan, ya had'iye wani mugun yawu jikake 'kudddd.
  Idanunsa sun kad'a sunyi jajur,, yasmeen ta ce, "aikin banza ashema kai matsoracine??..........kafin tarufe baki ya dam'ki hannunta na dama ya murd'e tabaya, tako kware baki zatayi ihu dan azaba, da sauri yasa d'ayan hannunsa ya toshe mata baki, saida ya tabbatar hannun ya murd'u sanan ya saketa yana dariyar mugunta, ya ce, "nida ke za'a tantance matsoraci.
   Yasmeen ta durkushe tana zubar da hawaye, jitake kamar hannunta baya jikinta, kwatakwata takasa d'agashi.
   Mus'ud yale'ko dan yaga wainar da ake toyawa tunda yasan ba shiri sukeyiba.dan tund'azu yafita yabarsu su biyu kawai.
  Da sauri ya'karaso ganin yasmeen tsugunne tana rusar kuka, a hanxarce ya ce, "Nawaf!! mikayi matane??.
   Banza Nawaf yay masa ya koma saman kujera ya zauna yana shan lemon kwakwarsa wanda yayi masa dad'i.
   Ran mas'ud ya6aci sosai ya ce, "waikai Nawaf wane irin mugun mutumne yau kuma mizakace tayi maka??.
   Nawaf ya yatsine fuska, katanbayeta abinda taimin sai nikuma nagaya maka abinda nayi mata, kawani d'ora mini laifi ni kad'ai, tsowwww ya 'karashe maganar da tsaki.
    Mas'ud ya ce, "kiyi hakuri yasmeen ALLAH zai saka miki,, yasmeen tad'ago jajayen ida nunta ta ce, "karka damu mas'ud nima dakaina zan rama, dan wlhy bana barin bashi, karya d'auka dan yayi mini wanan muguntar zan barsa, shima ya saurari ranar ramuwa..
   Tana kaiwanan ta mi'ke zata tafi, mas'ud ya ce, "plz karki tafi ki dawo, kinga su umma bazasuji dad'iba.
   Batayi musuba tadawo ta zauna dan tana ganin darajar mas'ud.
   Nawaf kam ko kallo basu isheshiba, yanata danne2 awaya hankalinsa kwance, yana kora lemon kwakwa.
   Na ce, ji 'kafin hali azo gidanku a cuceka. 

Afalon umma kuwa faisal ne da hajiya jummai da alhaji buba, zuwansu kenan suma, umma bata nuna musu komaiba ta tarbesu da mutunci, harda ruwa ta zauna suka gaisa sanan ta ce, "gashi kunzo malam baya nan amma yana hanya, dama jiya yake magana akan akwatuna, ya ce, "azo akai muku kafin ku biyo.
   Hajiya jummai tayi dariya, A'a mu ba kar6ar akwatuna muka zoba, munzo mu baku ha'kuri akan abinda yafarune, wlhy makircin wani abokin faisal ne, shikuma babu bincike yaje ya aikata wanan aika aikar, amma wlhy tunda aka gane makircine hankalinsa ya tashi, nan dai hajiya jummai ta labartawa umma komai daya faru.
   Umma ta ce, "ALLAH sarki ai bamu saniba damunzo mun dubashi, ALLAH yasa kaffarane faisal.
  faisal ya ce, "amin umma, yafad'a yana wani sissinkuyar dakai 'kasa, adole shi mai kunya.
   Hajiya jummai ta ce, "nibanga 'yar tawaba.
   Umma ta ce, "tana nan wlhy, tayi ba'kine, ALLAH sarki d'iyar albarka.
   Alhaji buba yaga hajiya jummai tanata wani kewaye2 takasa furta komai, sai kawai ya wage baki yashiga bayanai.
   Maman yaseer dama abinda yakawomu shine dan ALLAH ayi ha'kuri da abinda yafaru baya, tunda faisal yayi nadama ayi ha'ku amayar masa matarsa, munyi muku al'kawari hakan bazai sake faruwaba.
   Cikin mamaki umma take kallonsu, ta ce, "alhaji ai yasmeen yanzu tanada aure, ko baku saniba??.
   Hajiya jummai ta kar6e, munsani mmn yaseer, abinda dama mukeso muce shine dan ALLAH abama wancan mijin ha'kuri sai a war ware adawoma da faisal matarsa.....

Da sauri yaseer ya shige falon abba, batareda yaji furicin ummaba, kai tsaye wajen Nawaf yanufa, yayinda mas'ud da yasmeen suke d'an ta6a hira.
  Akunne yaseer ya gwargwad'ama Nawaf abinda yajiyo.
   Idanu naga Nawaf yazaro ya ce 'kanina da gsk, yaseer ya kad'a kai tareda fad'in sunama falon umma,, kafad'ar yaseer Nawaf yadafa ya ce, "karka damu bazamu barima Mafita ba  ka kwantar da hankalinka, yaseer ya ce, "to bara naje naji yanzu mi ake tattaunawa.
   To Nawaf ya cema yaseer.
  Maganar ta girgiza Nawaff, amma shi atunaninsa yasmeen tana son failal ne, yazata makircinne da gsk.
   Dan haka yake ganin ai bama saiya saketaba yasamu hanyar yima yasmeen abinda yaso kenan.
     
Awajen su umma kuwa, umma ta ce, "musu to wanan ba maganarta bace sai abba yadawo zasuyi shawara.
   Alhaji buba ya ce, "to bari suje suna saurarensu idan sunyi shawarar.
   Umma ta ce, "to mungode ku gaida gida.
   Har ga ALLAH faisal yaso ganin yasmeen amma babu dama, danko mai kama da'ita bai ganiba,, jiki a sanyaye yatashi yabisu hajiya jummai yanata raba idanu dan son ganin yasmeen.

    Tafiyarsu babu dad'ewa abba yadawo, bayan ya huta yasha ruwa yashiga suka gaisa da su Nawaf, har 'kasa suka tsugunna suka gaidashi, Nawaf sai wani sisinkuyar dakai yakeyi.
   Yasmeen ta ce, "munafinci banza, wlhy indai nice zaka gane kurenka.
   Sun d'an dad'e suna hira da abba, daga nan umma tashigo suka gaisa, su duka sun yaba da hankalin surikin nasu, gashi 'kya'ky'kyawa laillai d'iyarsu ta more saidai subita da fatan alkairi, dan auren miji nagari bababar ribace.
    Sai gab da magriba suka tafi, abba yamatsa saita yimusu rakiya.
  A 'kofar gida mas'ud ya ce, "yasmeen yakamata nima ki samar min mata a anguwarnan gsky.
   Yasmeen tad'anyi murmushi, ai indai wannan ne takwana gidan sau'ki, nabaka ameena.
   Ya ce, "woow!! Kice harna samu?, yasmeen ta ce, insha ALLAH.
   to yakamata afara yimini kamfen daga yau.
   Nawaf yaja tsaki yana fad'in malam nifa kana 6ata mini lokaci kaji,  tsaki mas'ud yaja, ya ce, "matsalarka ce kuma wannan, d'an rainin wayo kodan kaga ka kama taka a hannu, to nima tawa nake nema.
   Baki Nawaf ya ta6e ya ce, "kaine mata ke gabanka aii.
     Maganar tayi mugun 6atawa yasmeen rai, dan haka taja wani dogon tsaki tana fad'in wandama ya ce, "basa gabansa munafinci ne kawai...
    Da sauri Nawaf ya ce, "ke waye munafikin??, saida ta murgud'a baki sanan ta ce, "damai aikatawa nake.
    Nawaf yay wata 'yar dariya, yarinya kin taimaki kanki dakika kauce, wlhy dasai na ida 6alla wananan hannun mai kamada sillen kara.
   Masha ALLAH yasmeen tafad'a tana murgud'a masa baki, ta ce, "basai kazo ka 6allaba, kuma dakai ake zaka kashe nine???.
    tana ganin Nawaf ya biyota ta tsillara da gudu cikin gida.
  Nawaf ya ce, "'karamar 'yar marakunya daki tsaya mana kiga hauka.
    Mas'ud ya ce, "wlhy tunda nake ban ta6a kallon film mai dad'in kamar nakuba, gsky kuna wuta alhaji.
   Harara Nawaf yasakar masa, ya ce, "kaifa d'an iskane wlhy    mas'ud ya ce, "iskan cin menayi maka malam??.
    Nawaf ya ce, "wai mas'ud ya akayi haka, kodai kaine kayi wanan had'in yama za'ayi wanan yarinyar tazama matata, aii da sake.
   Babu wani sake malam aii ka d'auka an wuce gurin kawai, domin wannan wata hikima ce daga cikin hikimomin ubangiji.
  Wai mikayi mata d'azu naga tana kuka??, ko har an fara soye wane??.
   Duka Nawaf ya d'akama mas'ud ya ce, "a 'konewa aka fara ba soyewa ba, rashin kunya tamin na hukuntata.
    Hhhhh kaidai wlhy mugune nakula.
  Koda yake wasan yana 'kyau dan nasan saita rama.
   Lallai kam kokuma ta rame ba, dan wlhy yanzu ta ce, "zatamin hauka wahala zatasha ba 'karamaba, garama ka bata shawara ta kiyayeni.
   Hhhhh kadaiji dashi malam, dahaka suka 'karasa wani masallaci domin yin sallahr magriba.

Yasmeen kuwa da gudi tashiga gida, a falo suka had'u da umma ta ce, "k irin wannan gudu haka lafiya?.
   Gefen wuyanta ta sosa ta ce, "babu komai umma.
   Girgiza kai kawai umma tayi tashige d'aki domin yin sallah.
   Itama yasmeen d'aki ta shige ta kwanta domin tana fashin sallah, dan danan tashiga duniyar tunani, lallai saita dage tunda har ALLAH ya 'kaddara mata zaman aure da wanan d'an haya'ki, saidai kuma tayi farin cikin rabuwada faisal d'an is......takumayi ba'kin cikin kasancewa da Nawaf d'an kwallo, wai itace matar d'an kwallo kai lamarin tamkar almara wlhy, gsky bata moreba dan ita kwallo bata burgeta bare mai yinta, amma gashi ALLAH ya jarabceta da auren d'an kwallon.
    Ta kalli hannunta da har yanzu ciwo yakemata ta ce, "mugu ALLAH yasaka mini, kuma wlhy ka rubuta ka ajiye saina rama, 'kilama yayi mani targad'e azzalumin.
   Haka tai ta tuna abinda yafaru d'azu tamkar a mafarki.

FAISAL
    faisal kuwa koda suka tafi saiya sakama iyayenasa kuka, hajiya jummai ta hau rarrashinsa haba faisal d'in dady kayi ha'kuri, kobakaga 'ko'karin da mukeyi akanka bane, ka d'auka yasmeen tama rigada tadawo hannunka nan bada dad'ewa ba.
   Alhaji buba ya ce, "bana son ganin kukanka my son dan ALLAH kabari indai yasmeen ce dan kai aka halicceta kaji.
   Kai kawai yad'aga yana share hawaye.
   Wlhy ni dariyama yabani.

BAYAN KWANA BIYU.
    yasmeen tasake yima abba maganar makarantar ta, abba ya ce, "banace ki fad'ama mijinki idan yazoba.
   Ta ce, "abba ai na manta ban fad'a masaba.
   Aii wanan mai sau'kine tashi kije ki fad'a masa ta waya yanzu, idan ya yarda saiki fara zuwa gobe idan ALLAH ya kaimu.
    Jiki asanyaye yasmeen ta mi'ke, ita yanzu idan ta kirashi mizatace masa, 'kilama yay mata wula 'kancin daya saba mata, itako wlhy ba 'kyaleshi zatayiba.
   Tadad'e tana kullawa da kwancewa, daga baya ta d'auki wayar tafara kiransa cikin fad'uwar gaba, har wayar ta tsinke bai d'aukaba.
   Ta kai dubanta akan agogo 'karfe 9:56pm, wata zuciya ta ce, "ki 'kara kira, maso d'an tsuntsu aishi ke binshi da jifa.
    Ta sake kira har sau biyu bai d'agaba, jiki asanyaye tazame ta kwanta tana hawaye, shike nan an hanata zuwa makaranta tanaji tana gani.
   
^^^^^^^^^^^^^^^^
    Alokacin da yasmeen take kiran Nawaf yana wanka, yanajin wayar tana wringing, gashi yana dad'ewa awajen wanka, saida yagama komai na al'adar rayuwarsa kamar shafa'i da wutiri, karatun alkur'ani, (dan duk dare saiya karanta littafi amai tsarki,) san shayi, sannan ya haye gado ya kwanta, wayoyinsa yajawo, yafara duba missed calls, ya kira wad'anda suke da muhimmanci sanan, wayar da yasmeen takira itace 'karshe, 3missed call yagani saidai kuma ba'kuwar number ce, shikuma baya kiran ba'kuwar number.
   Harya kwanta sai kuma zuciyarsa ta kwad'aita masa yakira, dan baisan dalilin dayasa mai number yay masa 3missedcall ba.
    Lokacin har yasmeen tagama kukanta tayi barci, dayake barcin baiyi nisaba saitaji phone d'inta na wringing, sanda ta d'auka harta kusa tsinkewama.
   Cikin muryar barci ta ce, "assalamu alaikum.
    saida yaja ajiyar zuciya wadda shi kansa basan yayiba, ya ce, "wa'alaikissalam wacece??.
    Tuni yasmeen ta watstsake domin jin muryar Nawaf, dan da farko bata duba number da aka kirata dashiba, ta tashi zaune, cikin rawar murya ta ce, "yasmeen ce!!.
    Yad'an ta b'e baki dan tunda tayi sallama yagane muryarta, ya ce, "ban ganekiba, kinga kimin bayani yanda zan gane banason inda2, inba hakaba zan kashe wayata.
    Saidata murgud'a baki tamkar tana gabansa, ta ce, "toni wane bayani zan maka tunda nafad'i sunana baka ganeba, ni dama sonake na koma makaranta kuma abba ya ce, "saina sanar maka shiyyasama nakiraka, inba hakaba mizaisa nakiraka, ta 'kare maganar cikin mugud'a baki.
    Tamkar yaganta ya ce, "mara kunyar banza, to ban aminceba inkuma kikaje ban saniba ALLAH ya isa, d'if ya yanke wayar.
   Wasu hawaye suka zubo mata masu zafi, zuciyarta taita zugata akan takirashi ta ro'keshi 'kila yabarta.
   Haka ta daure ta kirashi, yay buris da wayar, saida ta sake kira sanan ya d'auka, wani lallausan murmushi yasaki na mugunta kafin yad'aga, yana d'agawa ya ce, "k nifa kin dameni barci zanyi.
   Ta matse hawaye ta ce, "plz dan ALLAH kabarni, kaga zamu fara EXAM ne kwanan.
   Saida yagyara kwanciya sanan ya ce, "toni ina ruwana, nidai nace ALLAH ya isa ko, kuma zan kira abba na ce, "na hanaki, dan haka karki sake kirana zanyi barcine, bata ankaraba ya kashe wayar.
   Dariya yashiga tuntsurawa harda hawaye, yarinya baki sanni bane, inada hanyoyin maga ninki wlhy, yafad'a yana kwanciya.
   Itako yasmeen kuka tashiga rerawa kamar uwarta ta mutu, saida tayi mai isarta sanan tayi shiru, har barci ya kwasheta..
   Na ce, "yasmeen asuba tagari..................


Assalamu alaikum
  Ina mi'ko d'unbin gaisuwa ga masoyana, nagode kuna 'karamin 'karfin guywa gsky, ngd ALLAH yabar zuminci.
   Luv u oll!!!!!!.

Acigaba da gashi!!!!!!!!!!.






©2016

Bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        Luv u oll my fan's
Share:

Recent

Blog Archive

Contact Form

Name

Email *

Message *