AUREN K'ADDARA
ko BIYAYYA
Na billkisa ibrahim
37 «******» dady yakai tsawon awa biyu afalon yana sak'a da warwara, ya kalli agogon dake palon, yata shi zaune da sauri danganin lokaci yaja, ya mik'e ya nufi b'anga ren sa.
Wanka yayi yay shirin barci, ya dawo b'angaren Munneerah, ya kashe komai ya rufe ko ina, sannan ya shiga bedroom d'in ya kalleta tanata barcinta, ya kamata ya canza mata kayanta zuwa na barci, bayan ya canza mata, yay musu addu'a yay kwan ciyarsa.
Da Asuba ya tashi yay alwala ya wuce masallaci batare da ya tasheta ba, bai dad'e da tafiyaba tatashi, tabi jikinta da kallo cikin mamaki waye ya canza mata kaya, wakuma ya kawota kan gado, tunda tasan afalo ta kwanta, zuciyarta tace mata mijinki, ta zaro idanu waje ni Munneerah kice yagama kalleni abanza, taja bargo tarufe jikinta da sauri danjin an turo k'ofa.
Ya tsaya cak yana kallonta danganin tanata faman cikukuye jikinta cikin bargo, ita kam tai k'asa da kai ta kasa kallonsa, yay d'an murmushi ya k'arasa jikin gadon yana fad'in ya jikin naki??
"tad'an kalleshi kad'an taikasa da kai, dasauk'i ta fad'a asaman leb'enta"
"Yanzu dai ba inda yake miki ciwo ko??
Ta kad'a kai batare datayi maganaba.
Shima bai sake cewa komaiba ya juya ya fita abinsa.
"Ta mik'e ta shige bayi"
*************»«
Tunda labari yajema su husna akan zasu koma gidan mijinsu suketa farin ciki, dan suna son dady da gaskiya, iyayensune kawai suka k'ulla auren nasu da wata manufa.
Tun adaren suka had'a kayansu, karfe goma na safe agidan umma tai musu,
Umma ta rik'e baki oh ni yaran yanzu bakuda ta ido, yanzunan danza ku koma gidan mijinku shine kukayo irin wannan sammako haka.
Husna tace to umma bamuyi dai daiba kenan.
Ah bar tsohuwarnan kinji itama idan itace abinda zatayi kenan,ikilima tafad'a k'asa k'asa,
Umma ta cafe to mara kunya mikikace ??
Ikilima tace nifa umma bance komaiba, tafaki idonta tai mata murgud'e .
Husna tai mata gwalo fiti nanniyar tsohuwa kawai .......
billy
{mrs Abdus'salam}
0 comments:
Post a Comment