check your best novels here

Monday 20 March 2017

SABON AL'AMAREE 57/60

[18/03 12:19] bilyn Abdul: [17/03 21:36] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》









NA BILKEESA IBRAHEEM. 
      {♡bilyn Abdul♡}






HIQAYA ONLINE WRITER'S
https://mrsbilkisa.blogspot.com 



57

........Koda suka isa gida sai kowa yanufi ďakinsa, ko sallama basuyima aunty bily ba dake zaune afalon, tabisu da kallo cikin matu'kar mamaki, lalai akwai wani abu a'kasa kenan?, tomike faruwa??, tasan kotaje wajen ya Mahmud bazai sauraretaba tunda ransa a 6ace yake, tadafa kujera ta tashi da 'kyar saboda cikinta yafara tsufa, kofar Nurr tanufa amma koda ta ta6a saita jita gam akulle, tayi tunanin kwankwasawa saikuma ta sake tunani, falon takoma ta zauna cikin jimami da damuwa fes afuskarta.
      Itakam Nurr tana can hankalinta gaba ďaya yana kan buk ďin da dady yabata, ta haye gadonta tazauna tana buďewa.
  Da wani hoto ta fara karo, ta tsurama hoton idanu tabbas suna tsananin kama da matar dake jikin hoton, dabadan itace azaunaba, tasan kuma bata ďauki hotonba datuni tace itace, saidai matar jikin hoton babbace, ta karanta rubutun kasan hoton.
   "Asma'u Mutallaf sardauna".
 Shine taga an rubuta, gabanta yashiga harbawa da sauri da sauri, wato mahaifiyarta ce kenan, wasu siraran hawaye suka fara zirara akumatunta, takai bakinta ajikin hoton ta manna masa kiss tareda rungume book ďin a 'kirjinta, takai minti goma ahaka idanunta arintse amma hawaye nafita daga cikinsu, ta cire littafin daga 'kirjinta tacigaba da dubawa, a gaba kuma hoton wani namijine, hakan na nufin mahaifinta, jitayi batayi wani murna da ganinsaba, amma itama batasan dalilin hakanba, bata wani daďe tana kallonsaba tawuce.
    
                  ashafi na biyu tafara karo da cikakken bayani akan abinda ke cikin littafin.
      Sunana Asma'u Mutallaf sardauna,, ni ďiyace ta goma sha...... agidanmu, hakan yana nufin ni autace awajen iyayena, inada yayye maza da mata masu tarin yawa, wanda mahaifammu suka haifa.
     Muntaso a gidanmu cikin gata da ilimin addini dana boko, dukda iyayenmu masu haline(masu kuďi) matuka hakan bai saka mun lalaceba.
    Musbahu ya kasance ďa ga abokin mahaifina na kut da kut, yakasance maraya saboda rashin mahaifiyarsa data rasu bayan haihuwarsa, wannan yasa mahaifinsa ya ďakkoshi yadan'kama mahaifiyarmu akan ta raineshi.
   Ba'a ta6a banbanta Musbahu damuba, tundaga suttura ci sha, ilimi daduk wani abu da ďa yake samu acikin gidansu, idanma baka saniba saika ďauka shima agidanmu aka haifeshi.
    auren zuminci akeyi agidanmu tunkafin tasowarmu, dan haka muma akai mana, an haďani aure da Musbahu domin shima tamkar ďangidanmu muka ďaukeshi, banyi ba'kincikiba kasancewar dama can muna soyayya nidashi.
   Lokacin da akai aurenmu Musbahu yanuna min soyaya kamar gaske, har ALLAH ya azurtamu da samun ciki saidai kash cikina bai rufa wata uku ba yazube, mun ďauki hakan amatsayin kaddara wadda har Musbahu yanuna damuwarsa fiye dani, in ta'kaicemuku na samu ciki yakai sau 6 amma baya kaiwa labari saiya zube, ban ta6a yunkurin zuwa asibitiba kasancewar mijina likitane, dan haka idan yadubani saiyace babu wata matsala lokacin haihuwarne dai baiyiba.
    Ban ta6a kawo komai arainaba, hakama ban ta6a zargin kowaba, ahaka muka kai shekara biyar da aure nida musbahu.
      Rana tsaka yazomin dabatu akan komawa kano gidan mahaifinsa, hankalina yatashi harma naje gida na sanarda mahaifana, lallashina suka shigayi damin nasiha, sun nuna min abinda zaiyi shine daidai saboda kowa da gidansu yake ado, nayi ba'kincikin haka amma babu yanda zanyi dan kowa bai goyamin bayaba.
    Damuwar dana shiga yasa Ya Abdul'malik yabani mahmud akan natafi dashi wajena sun bani, hakan yayimin daďi dan kaf family ďinmu banida 'kawar data wuce majaifiyar Mahmud, ina kaunarta matuka itama tana kaunata, sanda aka bamu mahmud bai wuce shekara 6 ba aduniya.
    Haka muka tarkata mukatafi kano ina kukan rabuwa da dangina, dan kusan nice aka ware acikinsu, amma dayake inason ya Musbahu sai bakincikina ya ragu.
    Humm komawata kano tasani damuwa matuka domin kuwa tarbiyyar gidansu Musbahu bata minba, shikansa mahaifinsu yanda yake mu'amalla dasu babu tsari, nayi mamaki matuka yanda ada danake kallonsa daga nesa nake masa kallon mutumin kirki, kenan yanayin fuska biyu agaban mahaifinmu, tokomadai miye gamu a family ďin ya Musbahu.
    Munada babbancin tarbiyya gsky shiyyasa nashiga damuwa matuka zamana a cikinsu, rayuwa ake gudan tamkar ta yahudawa babu tsari bare birgewa, wanan yasa na tsame kaina acikinsu banida abokin hira sai mahmud, idan yatafi makaranta kuwa ina ďaki kulle amma wanan bai hana kannen musbahu biyoni suna bugamin kofaba saboda 'yan akuyanci.
   Abin yafara damuna sainayima ya Musbahu magana, amma abin mamaki bai nunamin wata damuwarsaba, saima cemin yayi k nanfa bakamar rayuwar gidanku bace ta takura, munan kanmu awaye yake, bamu ďauki a'kida mai zafi munsa aranmuba, dan haka idan zakiyi yanda kowa keyi kiyi, idan kuma bakida ra'ayi ki kama kanki, dan bazan ďauki salon kawo zugar 'yan uwanaba.
   Tab lallai wanan abu yasakani acikin maye da ruďani, amma saina danne kodan Mahmud dayake shiga damuwa idan na shiga, ko yaya yaga fuskata ta canja shima saiya fara kuka, dan haka nafara ke6e damuwata dan karya gani, ana haka nasamu ciki amma shima saiya zube, nanma ban kawo komaiba.
    Ahaka muka cigaba da tafiya, har wataran naga abin yafara sakani cikin ruďu akan addinina dan haka nasake yoma Musbahu magana,, humm awanan rana naci duka bana wasaba tamkar kurar wasa, bayan yagama dukana kuma yabar gidan, nikuka Mahmud kuka, dan kuwa yaron yanada hankali sosai dukda 'karancin shekarunsa, ahaka muka kwashe tsawon shekara goma a kano, ina cin ba'kar azaba agurin musbahu, amma nakasa faďama kowa saboda ina tunanin kona faďa baba bazai yardaba, ita kanta mahaifiyar Mahmud nakasa faďa mata, kowa yakawomini ziyara yaga yanda narame nayi baki idan yatanbayeni sainace babu komai.
   Babu wanda yata6a kawo musbahu zaimin haka danhakama basu kawo komai aransu gameda halin danake ciki.
    Wata safiya muka tashi da ba"kin cikin kama mahaifin musbahu da akayi a airport ďin kasar amurika (America) da hodar ibilis, ya ilahi hankalin duk wani masoyinsa ya tashi, wasu suce basu yarda zai iyaba sharri aka yimasa wasu kuma dama sun san yanayin harkar ta karkashin kasa.
   Mahaifina yana ďaya daga cikin waďanda basu yardaba, dan haka yashiga cuku2n fito dashi saboda kasancewarsa baban ďan kasuwa kuma sananne.
    Bamusan miya faruba saidai ganin musbahu akayi da sojoji sunje har gida sun kama baba, tashin hankali wanda ba'asa masa rana kenan, tun anan yayenmu suka fara tambayar ba'asi amma sai akace baza'a bama baba ikon yin magana ananba dan haka su biyosu.
    Koda akaje inda akakai baba sai suka sanar dasu ana tuhumarsa da saida miyagun kwayoyi kuma shinema yasakama mahaifin musbahu dan akamashi shikuma yayi basaja.
    Tabďijan inji mata, tunda musbahu yafara maganar yayena suke kallonsa dan basu ta6a tunanin fitowar wanan magana daga bakinsaba, nanfa suka tasammasa da faďin yafaďi gsky fa, humm musbahu ya kekashe kasa yace gskyar kenan.
    Bayan kwana biyu da faruwar haka aka tafi da babanmu kasar amuruka akan tuhumarsa da saida hodar ibilis, wai duk kuďinsama tana yasamesu, munyi bakinciki matuka danhaka musbahu yana dawowa nace yasakeni.
    Naci duka ranar saboda firicin danayi, aiko yaďaukemu cikin dare yakai wani gida nida Mahmud, bamusan inaneba bare mu kubtar da kanmu, awani ďaki akakaimu mu biyu, daganan bamusan halin da'ake cikiba gameda kes ďin su baba.
    Kulum ta ALLAH sai anzo ammana duka nida Mahmud, kuma abincima kaďan ake bamu, sauďaya arana, hakama ruwa, duk sanda musbahu kuma yaso zaisa aďaukeni akai wani ďaki danya kusanceni, wanan abu namin bakin ciki matuka, domin kuwa ko sallah bama samunyi tunda ni banida tsarki dan koya gama abinda zaiyi dani baya bani damar tsarkake jikina, ahaka nafara laulayin ciki.
    Humm musbahu yazo yabani magani da karfin tsiya nasha cikina yazube, a wannan lokacin nagane cewa dama shike zubarmin daciki, baima 6oyeminba yasanar dani haka, dan yace baya bukatar haihuwa ayanzu, nayi kuka sosai nida Mahmud, mahmud har zazza6i yayi saboda kuka, da'kyar naroki mai kula damu ya taimaka min da ruwa na gyara jikina dayake akwai bayi ađakin...............



              58

........duk wanan abun dayake faruwa anacan ana nemanmu agida, dan Musbahu ya ce, "baisan inda mukeba shima ya wayi garine kawai bai gammuba.
    Tashin hankali biyu yataso family ďinmu gaba, gana rashin baba gana 6atanmu.
   Ana haka aka yankema su baba hukunci ďaurin rai da rai, duk wani masoyinmu yashiga tashin hankali, anata kuma zagin mahaifin musbahu dan ansan shiyayi wanan zargen har aka saka mafita, saikuma hatsabibin ďansa dayaketa rantsuwa akan saboda koken da baba yake siyarwa yasa yabaro gidanmu.
    Anzo bincike har gida kuma sun samu hodar ibilis agidanmu, wanan duk yana cikin kullin musbahu saboda yasan sirrin gidanmu gaba ďaya, danhaka yayi yanda yayi yakawo koken cikin gidanmu, baikuma 6oye manaba yafaďa mana duk kullin dayakeyi akan mahaifina.
    Saidai kawai na rungume Mahmud musha kuka, ahaka nakara samun ciki amma awanan lokacin bai saniba, ALLAH ya makantar da jinsa da ganinsa akan cikin dake jikina, ALLAH sarki Mahmud haka yayta ďawainiya dani idan nayi amai, abincin da'ake bamu baya isarmu amma haka mahmud zaiki ci yabarmin naci, asana  mahmud yana shekara 18 danya gama secondary ďinsa, danaga Mahmud yafara fita hayyacinsa saboda yunwa saina daina yarda naci saidai muci tare, ganin haka yasa Mahmud yafara rokon mai kula damu akan ya ringa karamana abinci saboda baya isarmu gashi kuma bamuda ishashshar lafiya.
     Mai kula damu bai kiba saidai yace akwai sharaďi indai zai dinga bamu abinci fiye da yanda aka umarcesa tofa zai dinga yima Mahmud bulala ashirin kullum, da sauri mahmud ya amince amma ni nace ban yardaba.
    Bansan mahmud ya lla6a ya sake rokon mutuminba.
   Haka yakara mana abinci, amma kullum saiya yima mahmud bulala ashirin, jikin mahmud duk yafashe cikin sati ďaya danba dukan wasa yake masaba, hankalina yatashi matuka amma banida damar hanawa.
    A family namu kuwa andage da addu'oi aduk masallatai dake cikin kaduna harma da wajen kaduna dan baba mutumne na mutane.
    ALLAH gafurun rahimun sai gsky ta bayyana aka gane baba baya ta amulli da saida miyagun kwayoyi, aka sakkoshi, aka sake kama mahaifin musbahu, tofa awanan rana Musbahu yay niyyar kashemu saboda abin yay masa ciwo matuka.
     Bai 6oye manaba ya zayyane niyyarsa akanmu, amma wai ba rana ďaya zai kashemuba, dan haka muza6i wanda za'a fara kashewa, da sauri Mahmud ya ce, "afara takansa dan bazai iya ganin an kasheni agabansaba, nima kuma nace saidai afara ta kaina.
    Washe gari aka kulla igiya da shirin ratayemu, angama shirin komai dan har an ďora mahmud akan tebir inata kuka saboda tashin hankali, kamar daga sama aka bugo kofar ta buďe saiga sojoji da ya usman da Abdul'malik, atake anan aka damke su musbahu, mukuma aka kwashemu sai asibiti.
    An bamu taimakon gaggawa dan muna cikin halin ha'ula'i kam awanan lokacin, in ta'kaicemuku dai munsami taimakon gaggawa ga dangi.
   Cikin amincin ALLAH muka warke cikin wata biyu, lafiyalau mukadawo kamar yanda muke saidai rama, itama ahankali muka fara kiba.
    Dayawa dangi sunce azubar da cikin jikina amma mahmud yayta kuka shifa yanason abinda zan haifa, nima da nayarda azubar amma saboda tashin hankali da Mahmud yashiga yasa nace nima inaso abarmini.
    Haka nayita rainon ciki kusan tareda mahmud dan baya matsawa konan dacan, koda yaushe yana tareda ni har ALLAH yasa na haihu mace.
    Mahmud yayi farinciki dan har yafini farinciki nida na haifi 'yar, ina tausayin ďiyata dan ina tsoron kar abinda mahaifinta yay min yashafeta itama mijin dazata aura yaymata haka, dan ance duk abinda kayi kaima sai anmaka.
     Hakadai nayita rainon yarinya dataci suna nan mahaifiyarmu wato Maryam, amma muna kiranta da Nurr, babu wani taron suna da'akayi dan nace banaso, babu lalashi daba'a minba amma nace banaso, ahaka Nurr tacika shekara ďaya, sanan Mahmud yafara karatunsa a jami'a, amma dukda haka saida yayima Nurr bikin cika shekara ďaya, awannan ranane nayi al'kawarin mallaka masa Nurr har abada indai har yana sonta amatsayin mata, nayi hakane saboda Mahmud kawai nake ganin zai iya ri'ke Nurr tsakani da ALLAH, batareda ya kyaretaba bare cutarwa.
   Mahmud yayi matu'kar farinciki kuwa  hakama baba da ya Abdul'malik.
     Bayan kwana uku dafaruwar haka natashi da ciwo wanda yakasance mini ciwon ajali.........

BAYAN RASUWAR ASMA'U.
    Rainon Nurr yakoma hannun mama mahaifiyar Mahmud, alokacin tana goyon Saiff dan haka suka tashi tamkar tagwaye, ita kuma mami tana goyon madeena (deena) kenan, mama ta ďauki son duniya taďora akan Nurr fiyema da 'ya'yan da ta haifa.
    Babu mai ta6a Nurr ta yarda, Nurr ta tashi cikin gata batareda tasan wani abu shi maraiciba, harta shiga shekara ta takwas, alokacinne kuma Alh mutallaf yashiga ciwo, ganin kamar bazai tashiba yasa aka ďaura auren Mahmud da Nurr domin cikama Momy Asma'u burinta, bayan ďaura aure da kwana goma yace ga garinkunan.
    Sardauna family sunshiga ruďu da rashin mahaifinsu, hakama al'umma sunyi kukan rashinsa, dan mutumne mai taimakon al'umma, duk hanyar dazaibi dan nemawa matasa aiki yasani.
    Indai aka tauye maka hakkinka kaje gareshi tofa saiya kwato maka hakkinka koda shi zai cutu, Alh mutallaf yakasance babbar katanga ga 'yan arewa, amma yau ALLAH ya ďaukeshi.
    Bayan lafawar rasuwarsa Nurr tacigaba da zama wajen mama batareda tasan ala'kar dake tsakaninta da ya Mahmud ba, har kawo randa za'a akita gidan miji.
    Wanda zuwa sanan mahaifinta yarasu kuma an aiko har family ďin amma babu wanda ya damu da rasuwarsa.

Nurr tunda tafara karanta littafin take shashshekar kuka da tsinuwa akan azzazlumin mahaifinta mugu da kakanta, kuka take tamkar ranta zai fita, tabuďe wata takarda dake kunshe acikin ambulan, ga abinda ke ciki.

Assalamu alaiki ďiyata.
    ALLAH ya kaddara bazan rayu dakeba, amma inamai nasiha gareki idan har kin girma kin mallaki hankalinki har kika tsinci kanki agidan yayanki Mahmud.
   Kiyi masa biyayya, idan kika sa6ama mahmud kodana minti ďaya ban yafemikiba saidai akan kuskure.
    Kiyi masa biyya dan mutumne mai muhimmanci arayuwarki.
    Karki rabu dashi.
  Idan kikayi haka bazan yafe mikiba.
   Ban yafeba! 
      Ban yafeba.!!
          Ban yafeba.!!!

Kuka Nurr ta fashe dashi, tamike da sauri tafice kamar wadda hauka ya saukar mawa.................








Luv u oll my fan's
©2017
[19/03 10:34] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》
🔚
      🔚
            🔚





NA BILKEESA IBRAHEEM
    {♡Bilyn Abdul♡}





HIQAYA ONLINE WRITER'S 
https://mrsbilkisa.blogspot.com 
Wannan page ďin nakine amarya teema, ALLAH yasanya alkairi yabaku zaman lafiya keda angonki, ALLAH yasa baďi mudawo suna. 
     Kuyi hakuri darashin jina kwana biyu wlhy nayi busy ne,  ina muku fatan alkairi arayuwarku




59 & 60

........Dagudu tafice daga ďakin, aunty bily dake zaune afalo tun ďazu takasa tashi tabi Nurr da kallon mamaki, saman ya Mahmud tahaye tana rubzar kuka, yana falo kwance akan doguwar kujera idanunsa alumshe, da'alam yana duniyar tunani, yatashi zaune da sauri danjin shigowar Nurr tana kuka, jikinsa tafaďa yay mata 'kyakykyawan ru'ko, sai kawai jiyayi hawaye sun fara zirara daga idanunsa shima, Nurr ta tuna masa abinda ya wuce shekar 34 dasuka wuce, shima kuka yashiga rerawa tamkar wani mace, shida Nurr ďin aka rasa wanda zai lallashi wani, saidai aikin shafa kanta yakeyi ahankali, itakuma tana 'kara lafewa ajikinsa tamkar wata mage.
   Sunkai tsawon minti 30 ahaka suna abu ďaya daga baya ya Mahmud ya lallashi kansa, ahankali yaďago fuskar Nurr daga jikinsa yana mata murmushi, itama batadan sanda ta maida masa murtanin murmushinba, yasake rungumeta tsam ajikinsa, yana kara faďaďa murmushinsa wanda shima baisan dalilin yinsaba.
    Ahankali yaji dashashshiyar muryar Nurr tana furta I luv u my yaya.
    Yasake ďago kanta da sauri Nurrina da gsk kina sona???, taďaga masa kai tana rufe fuska alamar kunya.
   Yaci gaba da faďin maryam kin amince zaki cigaba da zama dani???, zaki sake haifamin abinda ke cikinki da 'kannensa??, bazaki rabudaniba har abada??, duk cikin rikicewar murna yake jero mata waďannan tanbayoyin??.
     Taďago matsakaitan idanunta dasuka jajur tana kallonsa, ahankali ta ce, "yaya na amince da dukkanin bu'katarka, zan zauna dakai, zan haifa maka yaran dakakeso insha ALLAHU, wlhy yayana inasonka ina 'kaunarka, bakuma zan daina sonka ba har 'karshen numfashina, tayi saurin sakkowa 'kasa ta durkusa agabansa, yaya dan ALLAH ka gafarceni akan abinda namaka abaya......takasa karasa abinda takeson faďa saboda kuka daya sarke muryarta.
   Shima sakkowa yayi kasa yay saurin rungumeta ajikinsa, nayafe miki Haskena dama ni ban ta6a fushi dakeba, akullum ina miki uzuri, kuma ina 'kaunarki bazan daina 'kaunarkiba har abada Haskeena, ya ALLAH na gode maka daka kawoni randa Nurrina ta amince da 'kaunar danake mata, ta fahimceni harta ďaukeni amatsayin miji kuma uban 'ya'yanta, matseta sosai yasakeyi tamkar zai maidata cikinsa, bayan wasu 'yan muntina yaďago fuskarta suna kallon juna sai murmushi sukeyi, Nurr takama hannunsa ta rumtse anata, taďan langa6e kai gefe tana kallonsa, yauce rana ta farko data tsaya tayi masa kallon tsaf, tabbas ya mahmud yanada 'kyau dukda kasancewarsa ba'ki sosai, abin alfaharin kowace macece inhar tasameshi amatsayin miji, yanada kwalitis masu yawa wanda sukaďai dasuka kasance matansa suka sani, saima yayi dariya fararen hakoransa sun bayyana da wushiryarsa matsakaiciya datakan kara masa armashi wajen kyawu, uwa uba kwarjini da ALLAH yayi masa na musamman.
   Ya bushe mata idanu takawo numfashi da da sauri, saikuma suka tuntsure da dariya, yaďan lumshe idanunsa tareda sumbatar hannunta, nayi miki 'kyaune??, yatambaya yanaďan zaro idanu kaďan, ta sakar masa murmushi har kumatunta suka lotsa, ahankali ta furta sosaima.
    Yajawota jikinsa yana 'yar dariya, cikin kunnenta ya ce, "kiyita kallona haskeena babu mai hanaki, niďin nakine, ina fata zaki shaidama su dady haka asafiyar gobe idan ALLAH yakaimu.
   Ta ce, "insha ALLAHU mijina, ayanzu bana shakka ko shayin faďar ina 'kaunarka agaban kowa, komin tarin ko dandazon jama'ar kuwa, ta raunana miryarta ya mahmud kai mutumin kirkine adalin namiji mai kuma matukar muhimmanci arayuwata, kataka matukar rawar gani acikin rayuwata tun ina ciki, ayayin dakuke fuskantar zalunci daga azzalumi musbah........da sauri ya Mahmud yarufe bakinta, Nurrina ki daina faďa har yanzu yanan amatsayin mahaifinki bakida kamarsa........ta zame hannunsa daga kan bakinta, ta ce, "niba 'yarsa bace domin kuwa baima san dazamana aduniyaba, ALLAH ya isa tsakanina dashi......haďe bakinsa da nata yayi, yashiga mantar da'ita 
duk wata damuwarta, tabbas yau ya Mahmud yashaida Nurr tana 'kaunarsa, dan tabada muhimmiyar gudummawa afagen soyayyar tasu mai daďďen tarihi, ta nuna masa itamafa ta kware afagen karatun nasa, takuma haddace duk abinda ya koyar da'ita harma tana 'ko'karin zarcesa, yaukam sababbin ango da amarya suka koma fil masu tsananin so da 'kaunar junansu, yaukam dabance acikin aurensu dan har sun sakata cikin tarihin rayuwar auren nasu.
   (Nima nayi matu'kar farinciki masu karatu, dama kullum burina naga Nurr ta 'kaunaci ya Mahmud, tokuwa saigashi ranar tazo).
     Washe gari har 'karfe takwas suna manne da juna, dan ya Mahmud ya hanata wani kwakwkwaran motsi, datace ihin!!, zaice miye damuwarki??, jikinta kam sai ciwo yake saboda murzar datasha ahanunsa, kwankwasa kofar da'akene yasa suka tashi, ya Mahmud ne yatashi yaje ya buďe saiyaga aunty bily, rungumeta yayi tareda mannawa cikinta kisses guda uku, ya ce, "kuna lafiya my bily??, ta ce, "dadai sauki kam, da sauri ya ce, "miye matsalarki??.
   Ta taka ahankali zuwa cikin falon shikuma yana tsaye yana binta da kallo, ta juyo suna fuskantar juna, yaya damuwata itace taku amma kun lilli6eni bakwason sanar dani, bansan miyasaba??, kokuwa ban cancanci na sani bane oho??.
     Yazo da sauri yasake rungumeta bama 6oye miki komai dan baki cancantaba, saidai dan kare lafiyarki bilyna, bawani abu bane dama kanwarkice tasamu ciki, saitace saita zubar, shine nakai kararta wajensu dady, kinji abinda yafaru, amma yanzu komai normal ta hakura.
   Nurr dake la6e tana jinsu tasaki ajiyar zuciya taji daďin abinda ya Mahmud yay mata, taji daďi daya rufe sirrinta dana mahaifanta.
   Fitowa tayi itama takama hannun aunty bily tana bata ha'kuri, akan damuwar dasuka sakata aciki, aunty bily ta ce, "karku damu yawuce babu komai, nayi muku uzuri, rungumeta sukayi suna sake bata hakuri, wlhy yawuce kunji, daga nan nasiha tashiga yima Nurr mai shiga jiki da ratsa zuciya, sanan suka sakko falon 'kasa domin yin breakfast, da aunty bily ta 'ko'krta wajen haďa musu.
     Bayan sun kammala sukayi shirin komawa gidan dady, sukacema aunty bily zasuje gidan dady dan yace su koma yau da safe.
   Aunty bily ta ce, "babu damuwa sai sun dawo.
     
GIDAN DADY.
       cikin 'yan mintuna suka isa gidan dady saboda babu nisa tsakaninsu, dady yana gida bai fitaba yana jiransu, tunda suka shigo yake binsu da kallon mamaki dan ganin fukokinsu cike da annuri, yabasu izinin zama bayan sun gaidashi, zamansu babu daďewa mama da mami suka shigo, Nurr da ya mahmud suka gaida iyayen nasu dan basuje ďakin kowaba, shiru ya gifta naďan wani lokaci, dady yay gyaran murya batareda 6ata lokaciba inason kusanar dani saka makon maganar jiya da'aka fara, Nurr da ya mahmud suka haďa ido tareda sakarma juna murmushi, dady dasu mami suka kalli juna suma.
    Dady ya ce, "ina saurarenku, ya mahmud yay 'kasa dakai yana murmushi, dady komai ya wuce mun daidaita kammu, babu sauran wata matsala yanzu.
   Dady ya jinjina kai inason jin hakan daga bakin Nurr ne.
  Nurr ta ce, "duk abinda ya mahmud yafaďa dady hakane, na amince zan zauna dashi har karshen rayuwata kuma cikin so da aminci.
   Dady ya washe baki kai amma naji daďi sosai, haka akeson mutum yakasance ALLAH yay muku albarka kunji, amin suka faďa suna kara yin kasa da kai saboda kunya.
  Nurr tafara shashshekar kuka dady dama haka azzalumi musbahu yay muku da momyna ALLAH ya isa ban yafe masaba, dady miyasa kuka 6oyemin, naso ace kunsanar dani tun ina karama nayita tsinemasa har karshen rayuwata...mama tajawota jikinta tana lallashi, saida ta tsagaita da kukan sanan suka shiga yimusu nasiha mai tsuma rai da zuciya, musamman ma Nurr anmata nasiha sosai akan muhimmancin iyaye komi suka maka, sun ďan daďe agidan daga baya dady ya sallamesu.
   Suna mi'kewa danufin tafiya saiga su waleeda, aiko ganin iyayensu suka manne musu, babu lalla6awar daba ayiba amma suka nani'ke akan sai sun bisu, dady ya ce, "shikenan kutafi dasu daga yau kuma yaye ya'kare, aii sunyima 'kokari, dama mamansu bilkeesu tanata mana zarya, wai anzo gaishemu nasan kuma dan 'ya'yanta take zuwa.
    Dariya suka saka gaba ďaya mami ta ce, "dama kawaici kawai ake mana, amma an kagara sukoma, to aii yau anbasu saisu gaida gida suda 'ya'yansu mama tafaďa tana ďan murmushi, daga yau kuma karna sake ganin kafafunku, dady da mami suka tuntsure da dariya.
   Ya mahmud dama haka yakeso, sukayi musu sallama suka taho.
   Ahanya Nurr ta ce, "Kai yaya ALLAH baka 'kyautaba, ya kalleta saboda mi kikace haka??, saboda amso su waleed daga gidan dady, yayi dariya haba 'yammata ainayi hakurima, wata biyu fa, kema dakiketa wani noke2 nasan kinyi missing nasu, nida bily munata kewarsu wlhy, aiko idan nice wlhy ko yini bazan sake ďaukarsuba, yayi dariya kawai batareda yayi maganaba, dahaka suka 'karasa gida, aunty bily tayi farincikin dawo war su waleeda, har ďan faty tahaďa na murnar dawowar yaranta  aunty bilynmu nakine ooh.
     
Haka rayuwa tacigaba da tafiya, Nurr da ya mahmud anata shan soyayya kamar su cinye juna, dama gashi yanzu mijin ahanunta yake, saboda aunty bily ciki ya tsufa, soyayya suke zabgawa kamar babu gobe, abin sai wanda yagani (na ce, "ALLAH ya cida 'yan baya haka irinsu Ayeesh da ikilee).
     Cikin amincin ALLAH aunty bily ta haihu, ta sambaďo ďanta namiji kyakykyawa sankon kowa kin wanda yarasa, kai zokaga murna gun Nurr da uban gayya ya mahmud, hakama dangi sunyi murna dan aunty bily tasha fama na asarar babys datayi tayi abaya, to gashi ALLAH yabata itama, dama ance mahakurci shine mawadaci.
    Komai Nurr tanayi, Duk abinda yadace tayima mai jego tanayi, tana bata kulawa yanda ya kamata, agefe kuma tana bawa ya mahmud tasa kulawar ta musamman, saikuma 'yan yaranta datakema aunty bily kara akansu.
    Bayan zagayowar sati yaro yaci suna habib sunan dadyn aunty bily, suna cemasa Arfat, to saimuce ALLAH yaraya Arfat gambon 'yan biyu waleed da waleeda.
      Bayan suna aunty bily da sati biyu deenama ta sauka ta haifi mace, masha ALLAH itama tasamu Aysha ALLAH yaraya Aysha humaira. Ameen.
    Sun cigaba da zuwa makaranta yayinda Nurr taketa rainon cikinta dayayimata ďas yasakata fari da jiki, dan har wani 'yan mazaunai ta ajiye na musamman, waďanda suke burkita kwanyar gwaskan nata ya mahmud.
   Ya Mahmud yana nunama matansa da 'ya'yansa soyayya ta musamman, yana 'kokarin nuna adalci atsakaninsu, koda yaushe yana manne da 'yayansa da matansa ababen tushen farincikinsa.

To ALLAH dai yasauki Nurr lafiya, ansamu mace AMEENATU, bayyana muku yanda shagalin suna yakasance 6ata lokacine, amma komai yabada ma'ana.
   Bayan kawana biyu Khairat da rabi'a suma suka haihu, zoga murna wajen ya mustapha da ya mubarak suma sunzama baba ooh.
    
BAYAN WANI LOKACI.
      ya mahmud yau yana gida kasancewar weekend ne, Nurr da aunty bily duk suna falonsa harma da yaran, zuwa yanzu meenal da Arfat babu inda basa zuwa ga surutu kamau akkuna, sunata wasansu iyayen nazaune suma suna hirarsu.
     Ya mahmud sai binsu da kallo yakeyi, wani daďi yakeji idan yakalli yaran, yanzufa nan duk mallakinsane shi kaďai yađan lumshe idanu yana sakin murmushi, Meenal da Arfat sukazo suka faďa jikinsa suna kiran Abba abba!!!, yakama hannunsu yana murmushi yaran abba ya akayine???.
   Abba ka kaimu gidan dady yau ko gidan uncle dady, ya mahmud yay dariya, wato yarannan kun maidama fahad suna uncle dady ko??,  waleed da waleeda dasuka girma sosai suma suka 'karaso suna faďen dady muma zamuje gidan dadyn.
   Ya mahmud yace watodai yau kowa yawo yakeji, suka haďa baki suna faďin ehh Abba ehh abba suna faďi suna tsallen murna.
   Ya maida kallonsa gasu aunty bily dasuke kallonsu suna dariya, ya ce, "to inaga harsu momy suma su shiya kawai mufita yawon buďa ido da shan askirim, yeeeee yaran suka ďau ihun murna danjin za'a shan askirim.
    Nurr ta ce, "kai abba ammafa mun gode dama zaman gidan duk ya ishemu, yaďaga musu gira tareda kanne ido ďaya, sukace yarankadai masu wayon tsiya suna kallonaka, dariya kawai yayi yamike..
   Dandanan suka gama shirinsu suka fice, ya mahmud da aunty bily suna gaba, Nurr tana baya tareda yara, data ďago saisu haďa ido da ya mahmud ta madubi yana kallonta, saidai su sakarma juna murmushi kawai, haka yayta yawo dasu wajajen sha'katawa da wasan yara na musamman, sai dare suka dawo gidan cikin farinciki da 'kaunar juna....

     Tonima inamai farincikin kammala wanan ďan littafi nawa masoyana.
      Ina godiya ga 'UBANGIJINA daya bani dama da basirar rubuta wanan littafi nawa daya kasance sadaukarwa ga masoyana, Abinda nafaďa dai2 ALLAH kabani lada, wanda nayi kuskure ALLAH ka yafemini.
     
     SADAUKARWA GA MASOYANA.
       karku manata masoyana wanan littafi sadaukarwane agareku, dan haka banida damar ware sunan wani, saidai ina alfahiri daku gaba ďaya, duk inda masoyina yake bana mantawa dashi ina alfahari daku da wanda nasani da wanda ban saniba, ina godiya ga group group da admin's nasu, ALLAH yabar 'kauna, nagode da ďumbin soyayyar dakuka nuna mini, nima ina 'kaunarku bakuma zan manta dakuba, muassaman ma 'yan group ďina ina alfahari daku, luv u oll my FAN'S.

    KUNA RAINA 'KAWAYEN KWARAi.
ummi sani tyw
Hadiza ďayyabu fama.
Fateema ďayyabu fama.
Sadiya sulaiman tyw
Zakiyya liti tyw
Ameera musawa.
Sadiya Abdulahi tyw
Bahijja musa tyw
Hauwa muh'md Nsrw
Umayya yuseef R/gado
Fa'iza zakari tyw
Nafisa ibrahim Gidan mutum 1
Bariya salisu yashe
Hadiza umar fama.
Zainab adam tyw
Ikileema muh'md kano
Zahariyya idiris R/gado.
Hadiza yakubu tyw
Rabi'a lawan tyw
Ru'kayya muh'md tyw
Nafisa kabir tuge
Shamsiyya kabir tuge
Halima lawan fama
Jamila Abdullahi bichi
Aysha safiyanu kabagiwa
Naja'atu Rabi'u R/gado
Zuwaira Abdullahi kabagiwa
Fateema musawa
Bilkisu musawa (nana)
Aysha musawa
Sa'adatu musawa
Amina Rabi'u na iya bichi
Zainab adam bichi
Sha'atu Nuhu bichi
Hauwa'u giďe Dutsamma
Maryam Tasu'u tyw (ALLAH yajikanki ya gafarta miki, yaraya abinda kika bari.
      Ina mi'ko gaisuwa gadukkan 'yan 2010 Graduation (Zolo) na D/zabuwa, ALLAH yajikan waďanda suka rasu, waďanda suka haihu kuma ALLAH yaraya mana yaranmu, waďanda basuyi aureba ALLAH yabasu miji nagari.
     Sako daga
   (Bil~Gur)'yar tsanyawa

   To masoyana saikunjini asabon buk ďina maisun BAN SAKETABA.
    shima zaizo muku danasa sabon salon, faďakarwa, nishaďantarwa, ilimantarwa, kardai nacikaku saikun gansa.
   Saidai kuyi hakuri dan zaiyi jinkiri wajen zuwa gareku, saka makon shirin bikin 'kanwata damukeyi, amma bayan biki zakugansa, banaso nafara kuma na tsaya.
   Kardai ku manta da sunan.
 BAN SAKETABA!
         BAN SAKETABA!!
                 BAN SAKETABA!!!
SAIKUNJINI!!!!!!

    TAku bilkeesa ibrahim (bilyn Abdul).
    Writer ďin
RASHIN SANI
AUREN 'KADDARA ko BIYAYYA
'KANWAR UWACE ko KISHIYAR UWA.
NI DA AMINIYATA
NAWAFF
KUKAN KURCIYA....
SABON AL'AMAREE.
     

Taku bilyn Abdul

bye bye.

LUV U OLL MY FAN'S
©2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *