check your best novels here

Wednesday 1 March 2017

KUKAN KURCIYA............11/20

[16/02 11:46] bilyn Abdul: KUKAN KURCIYA......




        NA
MUH'D ABBA GANA
                 &
BILKISA IBRAHIM





Page1⃣3⃣&1⃣4⃣

........har suka tsaida adai2ta sahu suka shiga yana kallonsu, da hanzari ya tsaida wata shima ya hau, ya ce, "mai adai2ta wancan matan zamubi, to mai babur yafaďa, haka sukaita binsu Ameeda lungu da sa'ko har 'kofar gidan falmata, daga ďan nesa dasu suka tsaya, saida yaga inda suka shiga sannan yace mu juya kawai, mai adai2ta ya juya kan babur ďinsa suka koma.
    Koda suka koma asibitin bai iya shigaba sai kawai ya shiga motarsa ya fice, wani ďan matsakaicin gida yaiso, fakin yayi, cikin hanzari yashiga gidan, agurguje ya haďa 'yan kayansa kala biyu aďan 'karamin  akwati,  ya ďakko zuwa mota, komawa yayi ya kulle gidan sannan yadawo yayma motar key yafice daga anguwar,, babban titi yahau yarin'ka sharara gudu(araina na ce, "waishi wanan mike damunsane????).
    Hanyar kaduna yanufa daga kaduna yaďau hanyar abuja, 'karfe uku a abuja tayi masa saboda uban gudun dayayta shararawa ahanya, wata haďaďďiyar anguwa yashiga woow!! Nafaďa azuciyata lallai anguwar tahaďu masu karatu, hon yayi a'kofar wani 'katon gate, dagudu mai gadi yabuďe masa ya danna hancin motar ciki yana ďagawa mai gadi hannu, a yalwatacciyar harabar gidan yayi fakin ya sakko daga motar yana mi'ka dafaďin Alhmdullh, ya lankwasa yatsunsa sukayi 'kara sannan ya shiga cikin ainhin gidan.
   Da sallama yashiga 'katon falon daya tsaru da kayan more rayu babu kowa sai ac daketa faman aikinsa, tv falon ma tanata 6a6atu, ya wuce abinsa zuwa ciki,, nanma wani falonne tsararre annan ya tarar da mutanen gidan, dagu wasu yara 'kyawawa kansu ďaya sukazo suna faďin uncle oyoyo,, yataresu cikin farinciki tareda ďagasu ďai2 yana sumbatar kumatunsu, suma yabasu nashi suka sumbata, gaban wata matsakaiciyar dattijuwa yaje ya tsugunna yana gaisheta, ta amsa fuskarta ďauke da murmushi Muzzaffar ďina lafiya kuwa naganka agida kuma yau ba weekend ba??.
    Kansa yashafa yana murmushi, wlhy kuwa momy hakanan naji ina marmarin ganinku shiyyasa nataho,, kumani wlhy zaman kano ďinnan ya isheni sonake adawo dani nan kusadaku.
    Murmushi dattijuwar tayi tana tashi zaune daga kishingiďar datayi karka damu Muzzaffar insha ALLAHU kwanannan zaka dawo abuja da aiki, dan har nayima kawunka maganama, yauwa momcyna yafaďa yana kwantar da kansa gefen kafaďarta,, momy ta shafa kansa to kaga tashi kaje ďakinka kayi wanka saikazo kaci abinci ko??, dama kamar nasani nasaka hama ta gyara maka ďakinka,, fuska yaďan yatsine kai momy banace 'kazamar yarinyarnan tadaina shigar mini ďaki bane??, da'kuwa momy tayi masa kaci gidanku muzaffar bana hanaka wanan halinbane??, yaďan shagwa6e fuska tareda hađe hannayensa biyu yana faďin sorry momy bazan sakeba.
    Yauwa ďan albarka jekayi wankan kaji.
   Ďakinsa yanufa wanda ya tsaru shima komai na ďakin farine tas, na ce, "lallai kanada tsafta malam,, dan 'kazami baya maida komai nasa fari haka, ďakin sai tashin 'kamshi yakeyi, ya cire kayan jikinsa ya ďaura farin tawul yanufi bayi,, komai na bayinma farine tas masha ALLAH, babu 6ata lokaci ya salla wankansa yafito ya shirya cikin wando fari iya gwuywa da pink ďin riga 'karama, ya gyara sumarsa tareda feshe jikinsa da turare sanan yadawo falon.
    Dinning yanufa wanda aka cika taf da kayan abinci saikace zasuci su goma, 'yan yaran ďazu sukazo suka haye saman kujerun dinning ďin suna faďin uncle muma zamuci, murmushi yayi musu tareda jan hancinsu to my dota's, dakansa yazuba musu sukaci suka 'koshi bayan sun kammala suka dawo falon kusada momy suka zauna, suna nan zaune suna 'yar hira har aka kira sallar la'asar, tashi yayi yanufi masallaci suma su momy suka nufi ďaki domin gabatar da tasu sallar.

Bayan yadawo kai 'tsaye ďakin momy yanufa tana zaune saman sallaya tana lazumi yawuce bakin gadonta ya kwanta saida ta idar sanan ya ce, "momy ina yini?, lafiya lao muzzaffar ya gajiyar tafiya??, to Alhamdllh momy,, masha ALLAH ai haka akesonji.
     Ya ce, "momy nifa wani abun mamaki nagano a kano yau, da sauri momy ta ce, "wane iri muzzaffar?, kasa yasakko ya zauna kusada ita, wlhy momy natafi zan shiga asibiti sainayi gamo dawata budurwa mai tsananin kama dake kamar antsaga kara an karya.
    Arazane momy ta ce, "muzzaffar da gsk kakeyi kokuwa wasa??, yaďan jinjina kai wlhy momy da gsk kinsandai ban ta6a kawo miki makamanciyar wanan maganarba, ta matso kusadashi cikin zumuďi ta ce,, "kasan daga ina take??, kai ya sake girgizawa A'a momy amma dai naga inda suka shiga itada 'kawarta,, masha ALLAHU yarona kayi "kyan kai,  gobe idan ALLAH yakaimu zamu juya kano.
    Da sauri ya ce, "A'a momy bama saikinjeba kibari nagama bibiyar yarinyar, idan naďan ga wani abu gameda sirrinta saimuje harda dady, kinga babu dađi kiyi tafiya yanzu dady bai saniba ko???, shikenan muzzaffar kaima kakawo hanzari maikyau momy tafaďa cikin raunin murya.
    Labarai masu daďi yayta kwakwaloma momy danta saki jikinta, yansan yanzu saita burkice musu, dama kwanan suka samo kanta da'kyar akan wannan matsalar, saida yaga tasaki jikinta sanan yatashi yafice daga ďakin, daga nan addu'oi mamy tacigaba dayi ALLAH yatabbar musu da farincikin dasuka rasa na shekar masu yawa,, ALLAH yakawo musu'karshen wannan damuwa tasu. (Muka ce, "amin momy, dukda bamusan wacce irin damuwace ta dabai bayekuba).

Itako Ameeda tunda suka koma gidan falmata tafaďa duniyar tunani kokađan fuskar saurayin dasukayi karo takasa 6ace mata, duk wani motsinta yana kan tuna fuskarshi,, har falmata saida talura da damuwarta, kusada ita tazo tazauna, cikin sigar lallashi ta ce, "haba Ameeda wai saiyaushe zakibar sakama kanki damuwa akan abinda bake kika ďorama kankiba???,, yakamatafa ki zubar dakomai agefe kiji daďin rayuwarki, dagafa duniya sai kaduna,, watarana bazamuyi abinda mukeyi yanzuba.
    Murmushi Ameeda tayi tana mai kallon fuskar falmata ta ce, "falmata ai bazamuyima ALLAH wayauba,, nida ke duk bamusan ranar da mala"ikan mutuwa zaizo kanmuba, wlhy ina matu'kar shiga cikin damuwa da halin danake ciki.
   Sai kuma wani SABON AL'AMAREE (littafin bilyn Abdul) dayake shirin faruwa agidanmu, amma bansan taya zan fassara shiba, ayau kuma na'kara gamo dawani abinda ya tsayamin zuciya acikin asibiti.
   Falmata ta gyara zamanta sosai,Ameeda miye yake shirin faruwa agidan naku?, miye kuma kikayi gamo dashi a asibitin??, shiru Ameeda tayi saikuma zuwa can ta nisa hannun falmata takama tana faďin karki damu zan sanar miki amma bayanzuba,, a asibiti kuwa mutumin damukayi karo da junane ďazu yaketa yimini gizo a idanu, bansan miyasaba nakasa mantawa da fuskarsa da kuma irin kallon kurillar dayake mini.
     Dariya sosai falmata tashigayi har Ameeda tafara jin haushi ta ce, "k kuma miya baki dariya daga cikin maganganuna???.
    Falmata ta tsagaita da dariyar tana bama Ameeda ha'kuri, wlhy 'kawata ganinayi kamar kin kamu da soyayyane?, tsaki Ameeda tayi ta ce, "kefa falmata watasa'in kanki a cunkushe yake wlhy,, wlhy abinda nakeji gameda mutumin ďazu yafi 'karfin soyayya, wani abu daban nakeji gameda shi, kinsan ban ta6a soyayyaba kuma har yanzu baga wanda zanyi soyayya dashiba.
    Falmata ta langa6e kai gefe kenan yaudarar Nas kikeyi??, tsakai sosai Ameeda tayi, "o, da ke atunaninki son Nas nakeyi?, to idanma kina tunanin haka kibari wlhy banta6a jin onason Nas azuciyataba,, k ahalin yanzuma jinake na 'kara tsanarsa da duk wasu halayensa.
    To shikenan Ameeda ALLAH yajishemu al'kairi, Ameeda ta ce, "amin 'yar uwa.
   Gaba ďaya yinin yau haka tayishi sukuku kuma cikin ikon ALLAH batasha komaiba har dare, agidan falmata takwana dan kwata2 bata sha'awar komawa gidan,, koda sukaje club  da daddare batasha komaiba, bakuma tayi rawaba, gefe tasamu ta zauna abinta, kowa yasan budurwar Nas ce dan haka babu wanda ya matsa mata, dan sunsan halinsa sarai, kuma yana dawowa labari zai kai masa, ba'karamin aikinsa bane yakashe mutum.
    
Haka rayuwar tacigaba da gudu da sauri,, babu abinda yacanja daga rayuwar ameeda saima kara ta6ar6arewa da yakeyi,, dan Nas yadawo mata dawani sabon salon na shaye2, gidansu kuwa ji ake da'ita yanzu su iya basa mata faďa bare duka, duk abinda takeso shi ake mata, ita lamarin nasu har mamaki yake bata matu'ka.
   Yauma haka taci kwalliya cikin doguwar riga ba'ka saidai daka ganta kasan abinda tasha bai gama sakintaba, haka tafito tana ďan dafe bango ayayin dataji zata faďi, cikin ikon ALLAH harta iso titi, tana tsaye domin jiran babur ko mota saiga wata dalleliyar mota tadawo da baya har zuwa gabanta dan da harya wuce.
    Ahankali aka zuge gilas ďin motar 'kya'ky'kywan saurayin ranarne ya bayyana, atsorace Ameeda taja baya tana tangaďi, yabuďe motar dasauri yafito, sorry yafaďa yana matsowa kusada ita, ta ce, "malam lafiya kuwa??, murmushi yasaki mai 'kayatarwa ya ce, "lafiya 'kalao 'yammata, ina zuwa haka??.
    Tai saurin dafe bangon wani shago danjin tana niyyar faďuwa, ina ruwanka da inda zani nikam banason yawan shishshigi gsky,, amamakinta saitaga yayi murmushi tareda haďe hannuwansa a waje guda yana faďin sorry madam, amin afuwa natsaya ne narage miki hanya naga kina bu'katar hakan,, harararsa tayi tana wani lumshe idanu irinna 'yan maye, to idan banasofa?, sai incigaba da ro'konki harki amince kishiga motata beauty.
   Murmushi tayi saboda jindaďin sunan daya kirata dashi, ta ce, "to muje ALLAH dai yasa karka sayar mini dakai,, buďe mata motar yay tashiga yana faďin ai ko sayar da kai nakeyi bazan saida na beauty ba irinki, dariya tayi tana faďin maza akwai daďin baki.
   Tada motar yay sukabar titin batareda yayi maganaba.
  Yajuyo yaďan kalleta yayinda sukayi nisa, beauty ina muka nufane??, taďan gyara zamanta ta ce, "muje zan rin'ka nuna maka hanya, okey yafaďa yana murmushi,, lafiya lau ta nuna masa hanya harzuwa gidan falmata yayi mamaki kwarai da gsk, azatonsa yanda take abigennan bazata iya komaiba, tafito tana masa godiya, ya ce, "yanzu nan haka zamu rabu ko number bazaki baniba??, taďan ta6e baki haba malam daga haďuwa yau saina ďauki no ďina nabaka??, ya murmusa A'a beauty kindai manta yauce haďuwarmu ta biyu fa, aikuwa na cancanta abani, kinga idan kinbani number ki duk sanda kika bu'kaci zuwa wani waje sainazo nakaiki, kinga kinsamu direba daga sama kenan.
    Dariya sosai tayi tareda mi'ka masa wayarta tana faďin sarkin wayo gashi kaďauka, yauwa ngd sosai yafaďa yana kar6ar wayar tata mai 'kyawun gsk, number sa yasaka sanan yakira tata yay save ďin tasa atata sanan yayitata atashi,, sallama sukayi yaja motar yatafi suna ďagama juna hannu, itama saita shige gidan falmata tana murmushi, jinta take cikin wani farinciki mara musaltuwa.............

Ku biyomu.









©2017



Hikayarmu!!!!!!.
abba gana
           &
     bilyn Abdul
[16/02 11:48] bilyn Abdul: KUKAN KIRCIYA........




          NA 
MUH'D ABBA GANA
                 &
BILKISA IBRAHIM
  {☆Bilyn Abdul☆}



Page1⃣1⃣&1⃣2⃣


Babu daďe tadawo hannunta ri'ke da ledar indome, sanda tadawo iya abu ta tashi dan haka tashige ďakinta itama, tana tunane2 yanda iya abu ta ruďe lallai awai wata magana a'kasa,, amma zatayi 'ko'kari tonota insha ALLAHU.
   Hakadai tacigaba da tura indomi ďin badan tana mata daďiba, bayan tagama ci tafita wanko hannunta,, harta kai gab da 'kofa zata shige saitayi saurin jan birki danjin ana magana 'kasa2 a ďakin iya abu, ta matsa ahankali gefen 'kofar baba taji yana magana cikin ruďewa.
   Abu!! data tanbayeki mikika cemata??.
   Why malam bance mata komaiba saboda matu'kar razana da maganar ta sakani, iya abuce ke magana cikin rawar murya.
  Baba ya ce, "lallai wannan magana takai arazana, to wai ya akayima wananan yariyar harta iya wanan magana??, kodai Nasuru ne ya kitsa mata hakan??.
   Kai malam kaima kasan nasuru bazai faďaba, dan yanama abuja, nasan Nasuru bazaiyi irin wannan kato6ararba.
                   Baba ya sauke numfashi tareda yarce gumin daya wanke masa fuska, ahankali ya furta lallai idan mukayi sakaki tofa allura zata tono garma..........da sauri iya abu ta katseshi haba malam daina yimana wanan fatan mana, ai har abada babu mai tono mana daďaďďen sirrinmu, wanda dagamu sai ALLAH saikuma hajiya.
   Baba ya jinjina kai, to ALLAH ya tabbatar mana zainabu.
     Tunda Ameeda ta'iso wajen tsaye take kamar gunki, zuface keta ambaliya adukkan sassan jikinta, maganganun su iya abu sun rikita mata kwakwalwa, tarasa yanda zata fassara zancen nasu dan ta fahimta.
    Da sauri tashige ďaki danjin motsin babanta zai fito, ta faďa saman katifarta tana fidda numfashi, afili ta furta wanne irin 6oyayyen sirrine su baba basa son nasani, minene ma'anar allura zata tono garma idan sukayi sakaki???, miyasa suke zargin kuma Nas shiyya sakata wanana tambayar???? Shin wai miya haďa Nas ma da sirrinsu??, kodai Nas yasan wani abu gameda family ďinsu ne???,, tadafekai tana jijjigashi kamar mai shirin hawa bori, hawaye suka fara silalowa akumatunta, itakam tana kallon rayuwa a baibai, lallai akwai mayan 'kalubale dake bibiyar rayuwarta ta baďini data zahiri,, yanzu tawace hanya yakamata tabi domin binciko boyayyen sirrin iyayen natane dasuke 6oye mata akan aslinsu da tushensu???, da sauri kanta yake sarawa kamar zai faďo 'kasa.
    Jakkarta ta raruma tafara zazzagewa amma bataga abinda take nemaba, ta koma cikin kayanta, cikin sa'a tayi tozali da kwalbar sirob guda uku, da hanzari take 6alle murafan  ta juye maganin abakinta, ta yarda kwalaben gefe dan bai ishetaba, kwalaben ďazu ta đauka tana 'kara kalacewa anan barci yay gaba da ita.

WASHE GARI.
      Da'kyar taiya tashi tayi sallah tayi wanka tana cikin shafa mai kiran falmata yashigo ta ďauka murya aďashe tana faďin falmata ykk??.
   Lfy lao Ameeda kema ykk?, ina lfya, dama sonake kizo kirakani wani waje dan ALLAH, okey babu damuwa dama shirin zuwa gidanki nakeyi,, to shikenan ina saurarenki.
          Bayan wani ďan lokaci tafito saye cikin atanfa zani da riga ta yafa mayafi, atsakar gida taga iya ta gaisheta sanan ta ce, "zanje gidan falmata saina dawo.
    Cikin rawar jiki iya tace to saikin dawo Ameedan baba, batabi takantaba tafice daga gidan.
     Koda taje sai suka nufi inda zasu, gidan wata 'kawarsu sukaje sukai mata  ALLAH yasanya Alkairi, dan tayi aurene itamadai irinsu ce ALLAH ne yay mata gyaďar dogo tasamu miji tayi aure.
     Daga nan asibiti suka nufa domin yin dubiya, bayan sungama dubiya suka fito, arikice Ameeda taďago domin ji tayi karo da mutum lokaci ďaya suka ďago suna kallon juna, ahankali tafurta yi ha'kuri dan ALLAH.
    Ko motsi baiyiba saboda shiga wani matsanancin ruďani, kallonta yakeyi ko 'kyafta ido bayayi, falmata taja hannunta suka bar gurin................


Ku biyomu. 





©2017



Hikayarmu!!!!!!.
abba gana
           &
       bilyn Abdul
[19/02 13:21] bilyn Abdul: KUKAN KURCIYA.......







            NA
MUH'D ABBA GANA
                  &
BILKISA IBRAHIM
   (☆bilyn Abdul☆)


Assalamu alaikum.
muna mi'ko gaisuwa da fatan alkairi gareku masoyanmu aduk inda kuke,, kuyi ha'kuri dabaku pages ďai2 damukeyi kullum, littafin namu gajeren labarine,, insha ALLAHU muna gab da kammalashi,, mungode da 'kaunarku garemu,,, luv u oll.  

Page1⃣7⃣&1⃣8⃣


..........jikinta sai rawa yakeyi cikin kuka take bashi ha'kuri dan bataji daďin yanda tayi masa 'karyaba, kayi ha'kuri yayana wlhy badan banida gskya yasa na 6oyemaka sirrinaba akwai wasu dalilai masu yawa,, amma ina ro'konka da ka gafar ceni, insha ALLAHU wanan shine nafarko na 'karshe dazan yimaka 'karya akan abinda yashafi rayuwata, ta ďago tana kallonsa sai taga shikuma hankalinsa yana kan babanta dake tsaye a'kofar gida yana cin goro.
       yayana!! tafaďa cikin sanyin murya, ahankali yajuyo yana kallonta cikin in ina ya ce, "beauty waye wancan??, babanane tafaďa cikin 'kwarin gwuywa.
    Tafďijan yafaďa azuciyarsa, Ameeda ta ce, "koshima kasanshi ne??, A'a yafaďa a ta'kaice amma idanunsa nacigaba da kallon malam dauda.
   Ameeda tabuďe motar tafice tana faďin to sai mun haďu gobe ko?, okey karki damu kijirani agida insha ALLAHU 'kar fe biyu zanzo miki da abu uwan mamaki, kinsan masu iya magana sunacewa KUKAN KURCIYA JAWABINE.......Ameeda ta'karasa da faďin "mai hankaline yake ganewa yayana, murmushi yayi tareda mi'ka mata dubu biyar ya ce, "sai kinjini, okey bye tafaďa tana ďaga masa hannu.
     Koda tashige gida yadaďe zaune amota yana karema malam dauda kallo, daga baya yafice yabar anguwar, gida yaje yay wanka yanufi filin jirgi sai abuja.
    Da wuri ya isa yauma mutanen gidan sunyi farincikin zuwansa, bayan yaci abinci ya huta, suka haďu afalon daddy, daddy ya ce, "Muzzaffar kace mana a kwai magana amma munjika shiru.
     Muzzaffar ya murmusa, tabbas daddy akwai magana, dan yau na'kara gano abin mamaki kamar yanda na faďa maka awaya, inaso ka shirya mana tafiya kano muduka harda hajiya babba.
    Bangane mikake faďaba Muzzaffar???, daddy zaka gane amma sai goben.........momy ta katse musu zancen da faďin a'a muje mu kaďai idan komai ya bayyana sai azo har inda take, kasan halinta sarai, kuma batason zuwa kano da kowa.
    Gsky ne daddy yafaďa, yanzu saimu kwana cikin shirin zuwa kano insha ALLAH.

Washegari sukai 'kaura zuwa kano, dayake jirgi sukabi har saida suka huta agidan muzzaffar, kamar yanda yay mata al'kawari 'karfe biyu suka iso anguwar dan masallataima sunata sallar karfe biyu, amotar suka zauna babu wanda yafita sai muzzaffar, kansa tsaye yashiga cikin gidan saboda anyi masa iso, tunda yashigo iya abu tayi mutuwar tsaye, cikin in ina take nuna Muzzaffar Ameeda ina kika san wanan??.
    Ameeda dake tsaye tana kallonsu ta ce, "iya Shinefa Muzzaffar ďin danake gaya miki, kumafa kece kikace ya shugo, ganin ta rikice da ganinsa sai Muzzaffar ya basar ya tsugunna har 'kasa yana faďin mama ina yini?, cikin rawar baki ta ammsa, baibi takantaba ya haye tabarmar da'aka shinfiďa masa ya zauna.
    Ana cikin haka baba ya shigo gidan shima yarikitu da ganin Muzzaffar amma sai muzzaffar ya fuske ya'ki bada kofa koďaya ta alamun yasansu, nanma rissinawa yayi ya gaida baba, atsorace ya amsa tareda faďin yaro mike tafe dakai ne???.
    Murmushi Muzzaffar yayi ya ce, "baba nidai sunana Muzzaffar nafito ne daga 'kasar kamaru, ALLAH ne ya haďani da Ameeda naji kuma inasonta, wani ďan aikine yakawoni Najeria saidai bansan ko inaba bankuma san kowaba akasar sai Ameeda dana fara karo da ita.
     Ajiyar zuciya baba da iya abu suja lokaci ďaya itadai Ameeda duk kanta a ďaure yake, tana mamakin miyasa yayi 'karya??, bayan ita yafaďa mata iyayensa suna abuja.
   baba ya ce, "yaro kana nufin kaiba ďan kasarnan bane??, eh hakane baba, niba ďan nan bane, domin a kamaru ďinma ba anan na girmaba a london na girma, lokaci ďaya suka washe baki iya abu ta ce, "masha ALLAH aimu wlhy sai kayi mana kama dawani damuka ta6a sani.
    Ayya aidama haka rayuwa tagada mama, saikiga baka haďa komai da mutumba amma kuna kama da juna, nima haka mutane sukecewa ina kama da Ameeda sosai tamkar jini ďaya muka fito????.
     Idanu suka zazzaro tareda haďa baki wajen faďi  kuma???.
    Ya ce, "ai ikon ALLAH kenan kawaidai kamace, ya za'ayi muzama jini ďaya bayan tana Najeria ina kamaru koma nace london, wanan shine karo na farko dana ta6a zuwa 9ja.
    Ajiyar zuciya suka 'kara saukewa sukace eh gskyar ka kuma.
    Ya ce, "to nazo neman aurenta ne indai zaku bani, amma inaso asadani da ainahin iyayenta.
    Iyayenta kuma???? suka haďa baki wajen faďa suna kallon juna.
    Muzzaffar ya ce, "eh ina nufin kanin baba ko yayansa tunda sune masu ďaura aurenta.
    Eh kayi gaskiya yaro suka faďa suna sauke ajiyar zuciya.
    Muzzaffar yasake faďin saidai abinda yabani mamaki ko kaďan bakwa kama da ita anya kuwa ba sato................da sauri sukace satowa kuma yaro??????, nanama suka faďa suna dafe 'kirji.
   A'a bahaka nake nufiba, ina nufin kota sato kamannin wanine a danginku???.
   Ohhhhhh yaro kace wani abu, tana kamane da kanwar kakar baban babana ce.
   Ayya ammadai tayi 'ko'kari data ďakko gida, dan ance duk wanda yabar gida gidafa ta barsa, saidai inane asalin 'kauyen naku, dan can yakamata akai kuďin aurena.
    Kallon juna sukayi Yaro kauye kuma???,,, suka faďa suna haďa baki.
     Eh baba wai ina nufin asalinku, dan inaso na auri 'yar dangi mai asali kuma.
   To to to wannan magana da girma take yaro.
     Miye girmanta baba???, kodai dangin kune a abuja dan naga kamarsu da Ameeda, tayi kama sosai dasu.
    Abuja kuma yaro???? suka faďa kamar zasuyi kuka.
   A'a kukwantar da hankalinku nifa nayi muku hannunka mai sandane, yanzu ina tareda iyayena zasu shigo idan kun basu izini dan sunaso ku gana kamar yanda al'adar kasarmu kamaru take kenan, dan gobe idan ALLAH yakaimu zamu juya kamaru.
    To sushigo mana bari asaka musu tabarma.
    Duk abinnan da akeyi Ameeda tana zaune kamar gunki tana kallon alamomin rashin gsky kuru kuru a idanun iyayennata, lallai yau akwai abubuwan mamaki masu kamada almara agidannan, ita harma tarasa yanda zata fassarasu.
     Shin kodai ya Muzzaffar yasan wani abu gamedasune??, miyasa yakema iyayenta wanana tambayoyin ma wai??, miyasa sukan rikice aduk lokacin da yay musu tambayar ne???, gaba ďaya takula sun fita hayyacinsu..
       Amota ya tarar dasu momy, ya kallesu yana murmushi, dady ina fatan kunajin duk yanda mukayi ta waya???, kwarai kuwa ďan kirki muna jinku, inagadai dukkan hasashenmu yazama gasky kuma ALLAH yakawo mana 'karshen damuwa ta shekara ashin da biyu dasuka wuce.
    Murmuahi yayi To ALLAH ya tabbatar iyayena, yanzu kamar yanda kukaji sunce ku shigo.
  To suka faďa suna fitowa.
 Duk wanan tanbayoyi da Muzzaffar yakema su iya abu wayarsa a kunne take, dankuwa kiran daddy yayi ya ajiye wayar komai sunaji har aka gama.
      Da sallama suka shiga gidan, iya abu da baba suna zaune yayinda Ameeda take zaune a inda suka barta kamar dutse.
    Tunda suka rangaďa sallama suka shigo kallo ya koma sama, dominkuwa tuni su iya abu sunyi mutuwar zaune, ko yatsun hannunsu sun kasa motsawa, Ameeda ta mi'ke zummbur dan tun shigowar muta nen biyu gabanta yake dukan uku2 tamkar zai fito waje, jinta take tamkar ba'a duniyaba, sai kawai ta yanke jiki tafaďi awajen batareda daliliba.
    Da gudu Muzzaffar yayi kanta yana kiran beauty! Beauty!!!. Ina beauty ta suma, jiki na rawa momy ta 'karaso wajen tana jijjiga Muzzaffar da Ameeda dake jikinsa.
    Acan kuwa tuni fitsari ya ji'ke wandunansu iya abu da malam dauda, tuni sunshiga cikin kogin kwadamin ruďani da kiďima, lallai yau kashinsu ya bushe, lallai yau itace ranar tonan asiri, lallai yau itace rana dubu ta 6arawo ďaya kuma tak tamai kaya, lallai yau itace rana mai firgitarwa, lalai yau itace rana ta cizon yatsa da ambatar dana sani.
   Lallai yau itace ake kira da 'karshen tuka tuki tikkk.
      Adai dai wanan lokacinne kuma Naseer yashigo gidan ko sallama babu, tofa shimafa mun lura 'kamewa yayi atsaye tamkar bishiyar da aka dasa awaje ďaya, gaba ďaya zufa ta gama wanke masa dukkan sassan jikinsa, jiyake tamkar ya saki kashi atsaye, lalaikam idan zomo na yawo tofa kerema yana yawo tabbas wata rana za'a haďu, yau itace ranar zadata girgiza mutane masu ďunbin yawa, wasu zasu rasa daula, wasu zasu rasa aure, wasu zasu rasa aiki, wasu zasu rasa mutunci, wasu zasu rasa girma, wasu zasu bakunci gidan yarinema, tofa tabbasa Nas yana ganin kila yana cikin masu ziyartar gidan yari, dan yau ranace mai kamada ranar hisabi amma na duniyyyyyyyya.
      Tofa wai miye sirrin wanan rikita2ne???, wai miye abinda ake tsoron yafarune??, wai miye dalilin shigar mutane masu yawa cikin ruďani haka?????, miye tsakanin su muzzaffar da Ameeda ne???, miye tsakanin Nas dasu muzzaffar ne???, waishin ma waye muzzaffar???, waye Naseer???, suwaye su iya abu?????, wacece Ameeda??????, miye matsayin momy & daddy awanana bada 'kala???, miye kuma ya haďa wanana ahali akarkashin runfar rikici ďayane??????????...
    Mukaďaine masu baku wanana amsar, dan haka ku kasance damu........................

Ku biyomu. 











©2017


Hikayarmu!!!!!!.
         abba gana
                 &
 bilyn Abdul
[19/02 13:31] bilyn Abdul: KUKAN KURCIYA........






       NA
MUH'D ABBA GANA
                 &
BILKISA IBRAHIM
    (☆bilyn Abdul☆)



Page1⃣5⃣&1⃣6⃣

.......Tunda tashiga falmata ke binta da kallo dan ganin wata fara'a mara kangado datakeyi, ta zube saman kujera tana lumshe idanu dan barcin bai gama isartaba, falmata data kasa ha'kuri ta ce, "Ameeda wai miye sirrin farin cikinki ne???.
    Murmushi Ameeda tayi tana kallonta hummm 'yar uwa yaumafa sake haďuwa da guy ďinnan nayi, shimane ya kawoni har 'kofar gidanan.
    Falmata ta saki baki tana kallonta, kai haba??, ALLAH kuwa, zama falmata tayi kusada ita tana faďin to ya akayi yasan gidanku??, k ahanya ya ďakkoni yayin zuwana nan gidan, kai kawai falmata ta jinjina ta na faďin to ALLAH ya jishemu alkairi.

Haka rayuwar tacigaba da gungurawa yayinda da Muzzaffar yashiga rayuwar Ameeda sosai, koda yaushe suna ma'kale da waya, ko kuma su haďu awani wajen dan bata so Nas yagane tana tare da wani, cikin hikima yake janye ra'ayinta daga barin shaye2, idanma tasan zasu haďu bata shan komai kwata2, yauma tana zaune aďakinta sai wayarta tafara ruri, takai hannu ta ďauka dan ganin sunan Muzzaffar, cikin muryarsa mai daďi ya ce, "assalamu alaiki beauty, saida tayi murmushi sannan ta ce, "wa'alaikassalam yayana, ykk?, ya aiki??.
    Alhmdllh wlhy, yanzuma gani ina shiri tashi daga aikin, kefa kina inane??, gabanta ne yafaďin dan batasan yazata cemasaba, tunda suka haďu baisan inane gidansuba kullum a hanya suke haďuwa ko gidan falmata, shi azatonsama nanne gidansu, yaďan yi gyaran murya yana faďin yadai beauty??? koba'kya gidane??.
    Ajiyar zuciya taja ta ce, "ina gida zakazo ne??, eh indai kina bu'katar ganina sainazo??, sassanyar dariya tayi aini kozaka kasance dani koda yaushe zanso haka, amma yanzu kaga kayi aiki kagaji dan haka kaje gida kayi wanka kaci abinci ka kwanta ka huta.
    Murmushi yayi tamkar yana gabanta, murya 'kasa2 ya ce, "ina gwauro yaga duk wanan gatan beauty!!?, dariya Ameeda tayi sosai, wlhy kanada abin dariya, yanzu dakanka kake kiran kakanka gwauro??.
     Shima dariyar yayi, to aii gsky ce beauty, kinga da inada mata da yanzu kafin na isa gida an haďamin ruwan wanka, idan nayi kuma ga abinci yana jirana, kilama saboda gata abani abaki, to amma yanzufa?, dole duk abinda nalissafo nizanma kaina.
          Ameeda ta gyara kwanciyarta to yayana kadage kayi auren mana musha biki, kaga idan kayi aure to koda yaushefa ina gidanka ina taya aunty na aiki da hira kafinkadawo.
     Tofa yafaďa yana murmushi, beauty to idan kuma kece kika zama matar tawafa???, ido tazaro da sauri kamar tana gabansa, tabďija yayana bar wananan zance kaji yanzu dai bari nabarka sai anjima,, kafin ya farga ta kashe wayar gaba ďaya, yayita kira amma akashe, daga baya saiya ha'kura yanufo gidan falmata kawai.
        A 'kofar gidan falmata yay fakin yasamu yaro ya ayka dan akira masa Ameeda, shigar yaron babu daďewa suka fito da falmata, saida ta gaisheshi sanan ta ce, "ai tana gida yauma batazo nan gidanba kwata2, cikin mamaki yake kallonta ya ce, "dama tanada wani gida bayan wannan??.
    Lah bata ta6a gaya makabane, ainan gidanane nikuma 'kawartace, kai ya girgiza to shikenan, dan ALLAH kozaki iya yimin kwatacen gidanne??, babu damuwa ai bawani nesa baneba, kwatance tashiga yimasa, ta ce, "damma inada ba'ko dana rakaka kawai.
   Babu damuwa yafaďa yana tada motar, bankwana yay mata yatafi.
    Yazo gaf dazai fita layin ya haďu da motar Nas, bin motar yayi da kallo harta shige wanan ai Naseer ne mikuma yakeyi anan anguwar??, kardai ďan isakan yaronnan yazo yayta 6ata 'ya'yan jama'a a garinnan??.
     Da yayi tunanin yabi bayansa saikuma yafasa ya hau babban titi yanufi gida, yama fasa zuwa gidansu Ameedan kenan.

  Bayan kamar kwana biyu da faruwar hakan saisuka sake haďuwa da Naseer a anguwar, amma shi Nas baiga Muzzaffar ba, Muzzaffar ya ce, "Beauty dan ALLAH kinsan wancan guy ďinne??, cikin damuwa ta kalleshi ta ce, "miyasa kamini wanan tambayar ne??, saboda naga kina ganin shigowar motarsa kika kwantar da kujerar baya, kuma kin matu'kar shiga ruďani.
     Ajiyar zuciya taja tareda zubo da hawaye daga idanunta, ta ce, "karka damu dashi, a'a beauty dolene nadamu dashi dominkuwa nasansa nasan koshi waye, irikice take kallonsa cikin tsoro kuma, a ina kasansa dan ALLAH????.
    kansa ya maida ga titi yana faďin kifara sanar dani ala'karku sanan saina sanar dake nima,, cikin rawar baki tace shinefa saurayina danake gaya maka ďinnan, hazbinallahu wani'imar wakil yashiga ambata, arikice ya ce, "Ameeda yau inaso ki kaini ainahin gidanku.
     Nanma cikin tsoro take kallonsa ta ce, "badaga gidan namu mukeba yanzu,, kansa ya girgiza tareda yin fakin agefen titi, juyowa yayi sosai yana kallonta, Ameeda banan bane ainahin gidanku, nan gidan 'kawarkine falmata, amma idan kin bani dama yanzunnan zan kaiki ainahin gidanku inda mom & dad naki suke, yana gama faďa yatada motar.
     Gaba ďaya zufa ta wanke jikin Ameeda, tanajin kunyar 'karyar datayi masa gsky,, amma ba laifinta bane rayuwace tamaida ita haka.
    Tiryan2 yaringa bin hanya kamar yata6a zuwa babu indà ya tsaya sai'a 'kofar gidansu Ameeda, yajuyo yana kallonta beauty ga gidanku nan.................

Ku biyomu.









©2017



Hikayarmu!!!!!.
     abba gana
                 &
           bilyn Abdul.
[24/02 17:32] bilyn Abdul: KUKAN KURCIYA..........





NA
MUH'D ABBA GANA
        &
BILKISA IBRAHIM
  (☆bilyn Abdul☆)





Page1⃣9⃣&2⃣0⃣

.........Bayan an yayyafama Ameeda ruwa ta farfaďo, ya Muzzaffar ya zaunar da ita, ruwa dady ya mi'ka mata tasha tana hawaye, cikin kuka ta ce, "ya suwaye waďannan dan ALLAH???.
     karki damu 'kanwata ashirye muke damu sanar dake komai, dan haka ki kwantar da hakalinki.
    Dubanta ta maida gasu iya abu dake durkushe sunata rawar jiki harda kuka, ahankali ta matsa kusadasu tana faďi iya miyake faruwane agidabnan??, shin kunsansu ne?? Idan kun sansu suwaye su??.
    Babu wanda yabata amsa acikinsu saima rawar jikinsu dake 'karuwa, ta ďauke kai daga garesu ta maida kan Nas dake tsaye shima tamkar gunki daka gansa kasan arikice yake, jira kawai yake yasami hanyar dazai arce amma babu dama, dan tuni polis sun dunkare 'kofar gidan.
    Waya daddy yayi tareda faďin kushigo ku kwashesu dan yanzu zamu koma abuja acan zamuyi komai daya dace.
   Okey sir suka faďa suna ďirarowa cikin gidan tamkar tururuwa, tamau aka dam'ke iya abu da malam dauda da Naseer aka yayibesu sai mota, 'kofar gidan cike yake da al'ummar annabi sai kallo da dariya akema su iya abu, su mutane azatonsu wajen kwaďayin 'yarsu ta auri mai kuďi suka kwaso wanda yafi 'karfinsu, mota aka cimimiyasu suna kuka da ro'kon ayi hakuri babu wanda ya sauraresu saima wani ďansanda daya kwalama iya abu bakin bindiga a 'kafa, tako daddage ta kwala ihu.
      Acikin gidan kuwa tuni Ameeda ta ruďe tana kwasar kuka dakyar suka lalla6ata tayi shiru, momy ta ce, "idan kinada wani abin bu'kata ki ďauka dan daga nan har abada bazaki sake zuwa gidanan ba, cikin mamaki Ameeda take kallonta amma babu damar tambaya dan tana tsoron kar itama asaka 'yan sanda cimimiyar ta yanzunan.
    Kayanta ta haďo dady yakama hannunta haba baby indai sutturace abinda kike bukata kawai to kibarta mu tafi komai kike bu'kata zamu yimiki da izinin ALLAH kinji.
     Kai ta jinjina tareda ajiye jakkar kayan ta ďauki ďan abinda ba'a rasaba suka fice, har yanzu mutane suna tsaytsaye a kofar gidan dan su iya abu ana motar 'yan sanda, suna shiga motar polis suka take musu baya sai abuja garin naira.
        Koda suka iso 'yan sanda wucewa sukayi dasu iya abu polistion sukuma suka wuce gida.
     Aljannar duniya ameeda tafaďa azuciyarta, gaba ďaya tazama 'yar 'kyauye, taga gida tamkar baza'a mutuba, saida momy takamata ta zaunar sannan, mizzaffar sai dariya yake mata, tana kallonsa amma tayi burus dashi tanabin ko ina da kallo, ruwa 'yan aikingidan suka kawo musu tareda kayan motsa baki, ďaya acikin 'yan aikin ta rissina tana faďin momy akawo abincine??.
   Momy ta girgiza mata kai, a'a magajiya abarsa saimunyi wanka sanan, to hajiya afito lafiya.
   Muzzaffar yami'ke yana faďin kunga nayi nana.
   Momy ta ce, "to saura kuma ka kwanta barci, kanayin wanka kazo kaci abinci, karki damu momyna kibani minti talatin.
   Kai ta ďaga masa tana dariya, saida ya haye samansa sanan ta kama hannun Ameeda tana murmushi babyna zomuje kiyi wanka kinji, itadai ameeda tamkar makaho da ďan jagora haka takebin momy har zuwa ďakinta.
    Yasalam ameeda tafaďa azuciyarta, bedroom ďin yatafi da imaninta wani abin kallo sai a bathroom tamkar wajen cin abinci, bayin ya haďu, itadai haka tayi wanka tafito, saimada momy tanuna mata yanda zatayi sanan.
    Bayan futowarta momy ma tashiga wankan, bayan ta nuna mata kanayan kwaliya dakuma kayan sawa data ajiye mata akan gado.
   Tashirya tsaf cikin jar doguwar rigar mai adon fararen duwatsu abinka ga fara tayi mata ďas kamar dan ita akayi.
    Momy ma tafito tashirya, sukayi sallar la'asar dan tama ďan shige lokacinta.
    Afalo suka tarar da ya Muzzaffar da dady suna jiransu a dinning.
     Momy tazauna kusada dady, itama ya Muzzaffar ya nuna mata kusadashi, babu musu taje tazauna, aka haďama kowa abinci agabansa sanan sukai bismillah suka hau ci.
    Itadai ameeda akunyace takecin abincin har saida daddy yay mata magana, babyna kodai dakaina zan baki abincinnan dai?, hannu tasa tarufe fuska tana dariya a'a dady zanci da kaina.
     To yakamata kam, kisaki jikinki baby nan gidankune, bakida inda yafinan kinji, dummm taji kanta yayi, wai ita wane irin ruďani ake shirin sakatane??, tagaza gane wanan rikitaccen al'amarin??, ya Muzzaffar ya ta6ata, taďago tana kallonsa da ido yay mata alamar taci, ďan murmushin ya'ke tayi tacigaba dacin abincin.
   Su momy suna kallonsu.

Dahaka dai suka gama cin abincin suka tashi, dady ya haye samansa sukuma suka zauna suna 'yar hira, wadda duk anayine dan ameeda tasaki jikinta.
     Momy taje ďakin daddy, ta ce, "Alhaji nifa yau tareda baby zan kwana nayimaka yaji, yay murmushi a'a hajiya ainima ban yardaba saidai tazonan mukwana tare, murmushi momy tayi ta ce, "to inaga hakan zaifi sau'ki kam.
    Ranar agado ďaya ta kwana da momy da dady, sukasakata tsakkiya, (araina nace kai 'yan boko sai abarsu, wananan gandamemiyar budurwar za'a kwana gado ďaya da ita in bandadai.........baridai nayi shiru, ALLAH yashiryemu).............


Ku biyomu. 









©2017






Hikayarmu!!!!!.
 abba gana
           &
       bilyn Abdul
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *