check your best novels here

Wednesday 1 March 2017

KUKAN KURCIYA........ 1/10

[09/02 20:00] Abba Gana: KUKAN KURUCIYA...



                 NA
MUH'MD ABBA GANA
                 &
BILKISA IBRAHIM {Bily}
  (Mrs Abdus'salam)


Assalamu alaikum yaku 'yan uwa, muna farin cikin kasancewa daku a wannan d'an littafi namu, ALLAH yabar k'auna. 
    Idan kin karanta ko ka karanta wannan littafi namu kaga abinda yay kama da rayuwarka, ba haushi zakujiba bakuma marubutan littafin zaku zagaba, A'a,  kamata yayi ku bibiyi littafin domin magance taku matsalar ko gyara taku rayuwar, fatanmu masu kuskure irin wannan su daina, masu sha'awar yi karsu fara, shiyyasa muka kira littafin da suna  "KUKAN KURUCIYA, MAI HANKALI NE KAD'AI YAKE GANEWA, to ALLAH yaganar damu ayayinda b'ata ya riskemu.



Page 1⃣&2⃣

    Tafiya take tana had'a hanya, kai da kaganta kasan ba,a hankalinta take ba, dan kariyar ALLAH ce kad'ai ke tareda ita a bisa titin, takalmanta rik'e ahannunta, gata dai k'yak'yk'yawar mace dirarriya kuma fuskarta tana nuna alamun hak'uri, wani ihu datayi yasa muka maida kallonmu gareta, tacika hannu dak'asa ta watsa jikinta, tasake kwala ihu saini Ameeda,  d'iyar malam dauda da iya Abu, d'iya d'aya tilo agurin iyayenna, nice tafari nice auta,  yarinya mai farin jinin tallah.
   Bansan sanda hawaye suka zubo bisa kumatunaba, takuma kaikaicewa ta rabga ihu, na girgiza kai dan tabani tausayi matuk'a.
   Mai adaidaita sahu ta tare, cikin muryar 'yan maye ta ce, "gidanmu zaka kaini.
    Mai adaidaita ya yatsine fuska, toni nasan gidan kunne? kifad'i anguwar dazaki malama.
   Tayi shiru alamar tunani, can tađ'ago tana kallonsa da rinannun idanunta, ta ce, "kaga namanta sunan anguwarmu amma muje zan dinga nuna maka hanya.
   Mai adaidaita yaja dogon tsaki yana fad'in saboda nima makakkene irinki ko??, yaja adaidaitarsa yayi gaba.
   Ta tuntsure da dariya tana nuna babur d'in tasa, kaga mahaukacin mutum, amfad'a maka dan ina a bige kwakwalwata bata aiki ne?, jiri ya jata kamar  zata fad'i, tayi saurin dafe wata mota dake bayanta.
  Indai tak'aice muku ta tsaida adaidaita kusan uku amma basu d'auketaba dan jin tamance sunan anguwarsu, da k'yar wani yad'auketa, tako ringa nuna masa hanya dalla dalla har kofan gida, ta zaro d'ari biyu acikin d'ankwalin ta tamik'a masa, yakarb'a yana fad'in toga canjin malama.
   Ta juyo tana kallonsa dan harta fara tafiya, ta ce, " sunana ba malamaba, kuma canji kaje nabar maka duka, tafad'a dad'an k'arfi.
   Mai adaidaita ya jinjina kai yana godiya ya ce, "ya ALLAH yashiryeki kinji.
   Muda muka biyosu abaya mukace amin ya RABBI.
  Cikin gidan tashiga tana tangad'i, iya Abu dake a tsakar gida tana aiki tabita da kallo cikin bacin rai.
   Ameeda tazube agabanta tana fad'in iya taimaka mini da abinci wallahi cikina kamar b'arayin duniya sunmin sata.
    Iya abu ta balla mata harara ke  tsinanniya kada ki bata min rai in abinci kikeso ki koma ki ciwo daga inda kika fito , idan kuma kinje kibar tunawa dani, inkuma bahakaba wlhy yanzu jikinki zaya gaya miki.
   ameeda ta tuntsure da dariya harda bugun k'asa ta ce, "iya aii tsinannun nada yawa dankema tsinanniyarce, na tabbata kafin iyayenki su mutu saida suka tsitstsine miki albarka..
   Kafin ta k'arasa iya abu tashiga jibgar ta tamkar ALLAH ya aikota, itako sai ihu take da kururuwa harda zagi, makwafta suna jinsu, babu wanda ya leko balle a shigo ceto, dan idan da sabo sun saba, babu wayewan gari dabaza'a daki ameeda ba, saidai idan bata kwana a gidanba, dan wata sa'in bata kwana agida, 
         duka sosai iya abu tayi mata, saida taga  ko  yatsun hannunta baya motsi sannan tabarta tana cigaba da kalaman tsinuwa da d'ebe albarka ga d'iyar tata.
   Ahaka malam dauda yashigo yasamesu, azatonmu za'a samu rangwame daga garesa, amma saimukaji yana ambatar wannan shegiyar sai yanzu tadawo gida??.
   iya abu dake cin rai ta huro hanci ta ce, "yanzu tadawo zatamin iskanci nazane shegiya.
    Yayi dai dai,yasa k'afa ya shuri ameeda dake kwance A kasa matsiyaciya tashi kibawa mutane wuri, sai kaurin taba kikeyi asararriyan yarinya.
   Na rintse ido nabud'e danjin irin munanan kalami da iyaye ke yima d'iyarsu, lallai dole ameeda ta lalace indai har haka iyayenta suke mata tun tana karama.

   Itako ameeda tana kwance ko motsi batayiba bare ta amsa kalaman baban nata kota bi umarnin sa, ruwa ya d'ebo ya watsa mata, tabud'e idanunta dak'yar,  ya ce, "bacewa nayi kitashi anan ba me kika tsaya kina kallona, ameeda ta mika masa hannu tana fad'in taimaka ka kaini d'aki baba wlhy duk jikina yayi tsami, waccan tsohuwar ta dakeni sosai, kafa yasa ya shureta da karfi yana zagi da tsine mata, ta maida hannunta tana fad'in bakaso natashi kenan, dan nikam bazan iya tashiba, duk cikin yanayin maganar bugaggu take maganar.
   Banza sukai mata suka cigaba da harkokinsu, saida taji rana tafara dukanta taja jikinta da k'yar tashiga dakinta a kofar dakin ta kwanta abinta.................

Ku biyomu. 




Hikayarmu!!!
Abba gana
            &
     Bily


www.muhdabbagana.blogspot.com
[10/02 20:06] Abba Gana: KUKAN KURUCIYA.......




                 NA
MUH'D ABBA GANA 
                  &
BILKISA IBRAHIM {Bily}
    (Mrs Abdus'salam)



Page3⃣&4⃣



WACECE AMEEDA???.

     Ameeda diyace ga malam Dauda, iya Abu itace mahaifiyarta, ita kad'ai Allah ya mallaka musu, sun dade suna neman haifuwa a kwana a tashi Allah ya albarkacesu da Ameeda, sun nuna mata so da kauna da ya wuce misali wanda hakan ya jawo ta tashi a sangarce, tayi karatu har zuwa secondary kuma tanada kokari, ta samu tarbiyya dai dai gwargwado a wajen iyayen nata.
    Ameeda tun tana 'yar karama take talla, saboda tsantsan son kudi irin na mahaifiyarta tun mahaifinta malam dauda baya jin dadin tallar da ake d'oramata  har ya zamana baya iya cewa komai  dan iya abu ta mallakeshi sai abinda tace.
    AMEEDA k'yak'yk'yawace sosai, ga dogon hanci, tanada hak'uri sosai, dakuma tsoro.
   Duk da gatan da iyayenta suke mata wannan baihana mahaifiyarta duka da aibanta d'iyar ta taba, abu kadan ameeda zatayi sai mahaifiyarta ta hauta da duka da zagi, balle taje bata sayar mata da kayan sana'ar taba, aii ranar ta banu.
   K'yawun ameeda yasa takasance mai farin jini awajen samari, talakawa damasu kud'i, idan kaga motoci na layi a k'ofar gidansu saika d'auka wani taro akeyi, duk wanda yazo kuma dole taje balle idan yanada mota, inko tak'i zuwa mahaifiyarta  tafara tsinemata kenan dayi mata gori, wai babanta talaka itama taje ta auri talaka, saisu dawwama a talauci.
    Wannan maganganu suna k'ona zuciyar ameeda, amma babu yanda zatayi tunda mahaifiyarta ce.
   
Akwana a tashi wani saurayi mai suna Naseer yashigo rayuwar ameeda, Naseer d'an mai kud'ine sosai, gashi shima an sangartashi, dan shikadaine awajen  iyayensa, kwata-kwata bashida tarbiyya ko kad'an, ya kware a fagen shaye-shaye da neman mata, tunda ya k'yalla ido akan Ameeda yaji yana buk'atar yayi tarayya da ita, amma saidai ameeda tak'i bashi had'in kai, yaja ra'ayinta da kud'i, amma ta bijirewa buk'atarsa.
   wani abokinsa Badaru shiyya bashi shawarar yakama k'afa da mahaifiyarta mana, yasan dole tasa  ta kulashi , yakoji dad'in wannan shawarar tasa, dan haka sukayi shiga ta mutunci sukaje har gidansu ameeda, yanemi izinin zuwa wajenta zance, dafarko mahaifiyarta tak'i amincewa, dan ta ce, "baza'a kashewa d'iyarta kasuwaba tana tashenta, amma da Naseer ya ajiye mata d'aurin kud'i saita amince da sauri, harda alk'awarin mallaka masa ameeda.
   Tun daga nan Naseer yasamu damar zuwa wajen Ameeda, saidai tak'i bashi hadin kai, ganin wannan yasa yafara zuba mata benelyn acikin lemo, tun bata sha harta fara saboda tana ganin nan gaba shi zai kasance mijinta, 
    Ahankali lemon dayake kawomata yafara tasiri a rayuwarta, har takanji idan bata shaba bata jin dad'i.
   Da Naseer ya kula tazo hannu, saiya koma kawo mata zallar benelyn, da sauran kayan saka maye, akwana atashi harta fishi kwarewa wajen iya shaye-shaye, ya kuma koya mata zuwa club, takanje ta kwana acan, ba tare da wani fargaba ba, Ameeda tayi suna a club saboda iya rawa, da d'ibar kayan maye, idan tana rawa dolene abata fili a club.
    Saidai abin sha'awa ga rayuwar ameeda, duk iskancin nata bata tab'a aikata zina ba, babu lallab'ar da Naseer bai mataba amma tak'i, bayanshi wasu dayawa su kan sha kawo mata hari amma tak'i, duk buguwar datayi baka isa kaja ra'ayin taba, bare kace zaka nuna mata k'arfi.
    Wasu samarin kuma suna tsoron Naseer ne saboda zarransa,  yanzu Ameeda tazama cikakkiyar 'yar maye.
   Gashi iyayen nata sun tsaneta, suna kuma tofin ala tsine da k'addarar rayuwar data da baibaye d'iyar tasu.
    

        Yauma kamar yanda ta saba ta tashi tayi wankanta, tad'au kwalliya cikin wando da riga na fakistan, tayi matukar kyau, tafito tana goge takalmi, iya abu tafito daga kicin hannunta rikeda kwarya da gari, Ameeda ta ce, "iya yau babu abincine??.
   Iya abu ta watsa mata harara, tana fad'in tunda kin bani kud'in yi abinci basai ki danne ni ki kwataba.
   Ameeda tayi murmushi tareda jawo jakkarta, tazaro 'yan dubu dubu guda biyar ta mik"a mata, ga wannan kuyi cefane kafin nadawo.
   Jikin iya abu na rawa takarb'a tana washe baki, yauwa 'yar albarka, idan kina bada irin wannan mai zai sa muringa fada, kedai ALLAH yabaki miji nagari mai kud'i da mota.
    Ameeda tayi murmushi domin jin furucin mahaifiyar nata, tana mamakin kwadayi irin na mahaifiyarta, itadai indai kanada kud'i to komai mugun halinka zata zauna dakai, ahankali ta furta ya ALLAH ka shirye iyayena, kakawo mini canjin rayuwa mai albarka.......

Ku biyomu.



           ©2017



Hikayarmu!!!.
Abba gana
            &
     Bily
[10/02 20:09] Abba Gana: KUKAN  KURUCIYA..........





                  NA
MUH'MD ABBA GANA
                    &
BILKISA IBRAHIM {Bily}
      (Mrs Abdus'salam)




Page5⃣&6⃣




AMEEDA tamik'e tana fad'in iya bari naje saina dawo, iya tajuyo tana kallonta ta ce, "to Yau kuma sai ina??.
    AMEEDA tad'an gyara tsayuwarta ta ce, "iya zanje wajen falmata ne, amma zuwa yamma zan dawo, zanbawa hashimu sako yakawo muku yanzu idan nafita.
   Iya ta washe baki tana fad'in to madallah, Ameedan baba, amma dan ALLAH yau kar a dawo a buge d'innan.
    Ameeda ta fice tana fad'in to inna, a zaure ta tsaya tana share hawaye, da alamun tana cikin damuwa, tad'an dad'e tana zubar da hawaye, daga baya tagyara fuskarta sannan ta fice.
    Gidan wata k'awarta taje falmata, itama dai falmata irinta ce, dan a club suka had'u, saidai falmata tana zaman kantane, wannan halinne ya banbantata da Ameeda, a hankali suka shaku har suka zama k'awaye mafi kusanci.

    sallama tayi ta shige ciki, Suka rungume juna cikin farin ciki, falmata tace kai Ameeda wlhy yau kinyi k'yau, ga idanunki yau dai-dai suke.
    Ameeda tayi dariya ta ajiye jakar ta  a saman kujere, ta warware gyalen data nad'e akanta shima ta ajiye, ta kwanta.
     Falmata ta ce, "badai barciba Ameeda??, Ameeda tad'an yatsine fuska, ta ce, "barci tsiya nakeji, ga yunwa ya takurani yakamata abani abinci.
    Falmata ta ce, "to mizakici? Asiyo miki, kinsandai ni ba girki nakeyiba.
    Ameeda ta harari falmata tana fad'in ai ba abin kirki kikayiba.
    Falmata tayi dariya kawai, dan kullum Ameeda tana bata shawara akan tadage ta iya girki, saboda wataran dole subar shashancin nan suyi aure.
     Babu dad'ewa aka kawo musu  abinci, suka zauna sukaci suka k'oshi, Ameeda ta kalli falmata ta ce, "wai babu komai yau agidan ne??.
    Falmata ta harareta, dan tasan kayan maye take nufi, ta ce, "plz Ameeda karki sha komai, ke wai bakya zama sai abuge, yakamata yau d ki dan huta, gashima zanyi bak'i daga abuja, shi yasama na ce, "kizo da wuri, danki tayani gyaran gida.
      Ameeda ta ce, kice dai kawai kin maidani 'yar aiki, amma wane irin bak'ine maza ko mata, idan mazane kema kinsan bazan zau.......
     Falmata tayi saurin katseta sannu ustaziya, nibansan randa zaki wayeba Ameeda, kishigo harka sosai dan ki wuce wajen, kifita daga tarkon talauci, ki fidda iyayenki.
    Ameeda ta had'e fuska tareda d'agawa falmata hannu, "kinsan nasha gargadinki akan wannan maganar, wallahi dana tara dukiya da kudin banza gwara na mutu acikin talauci, tamik'e a fusace taja gyalenta da jakka.
     Da sauri falmata ta tareta tana bata hak'uri, akan bazata sakeba, dak'yar tashawo kan Ameeda ta hak'ura ta zauna.
     Ameeda taje ma'ajiyar kayan mayensu takwaso kwalabe uku  tadawo tazauna, dan sune kad'ai zasu gusar mata da b'acin ran da falmata tasakata, ta tsani kace mata tayi tarayya dana miji, haka tadinga korawa harsuka kare, tamik'e zata k'aro wasu, falmata tayi saurin tareta tana fad'in ya isa haka.
    Ameeda ta ce, "d'aya kawai zan k'ara, falmata ta ce, "A'a, bazaki k'araba wlhy uku fa kika sha, nan dai falmata tayita lallab'ar ta, harta hak'ura tashige bedroom ta kwanta.
    Falmata tabita da kallo tana girgiza kai, tana mamakin yanda Ameeda take caja kanta da kayan maye, amma bata yadda ta aikata wani fasikanci ba, zata iya cewa bata tab'a had'uwa da mutum irin Ameeda ba, dan sunsha yin fad'a akan hakan, koda yake tasan tunda Naseer ya gagara tursasa Ameeda  dole kowama ya kasa.
   Dan idan har Naseer yasaka ido a kan mace tofa dolene tashiga tarkonsa, amma Ameeda ta gagareshi, yayi dai nasarar koya mata shaye-shaye, da zuwa club, amma sauran bad'ala ya gagara.


WACECE FALMATA???

Falmata 'yar asalin barno ce,  ita cikakkiyar babarbariya ce.
    Falmata yarinyar kirkice mai ilimi da addini, mahaifiyarta ta rasu wajen haihuwarta, daganan kakarta ta reneta tsawon shekara bakwai daga baya Allah ya karbi abunsa.
    Bayan rasuwar kakarta sai aka dawo da ita gidan mahaifinta, daga nan falmata tashiga tsananin rayuwa, dan matar babanta tana gallaza mata, bata sonta ko kad'an, amma agaban mahaifinta ta kan nuna mata tsantsar so da tausayawa.
    Wannan yasa mahaifinta yakasa fahimtar halin da falmata take ciki, gallazawar tayi yawa, dan har takai abinci yana gagarar ta agidan, wannan yayi matuk'ar tasiri wajen lalace warta, daga baya  ta gudu zuwa garin kano, anan tahad'u da badaru abokin Naseer.
    Shiya siya mata gida, yake mata komai data buk'ata kamar matarsa.

  takaitaccen labarinta ....................

Ku biyomu.




©2017



Hikayarmu!!!.
Abba gana
            &
     Bily
[11/02 12:08] bilyn Abdul: KUKAN KURCIYA......






                NA
MUH'D ABBA GANA
                &
BILKISA IBRAHIM
   {☆bilyn Abdul☆}





Page9⃣&🔟


Ameeda ta juya ta sake juyawa akan 'yar yololiyar katifarta, gaba ďaya kanta akulle yake tama rasa irin tunanin dazatayi, da sauri ta mi'ke zaune tajawo jakarta ta hannu, kwalaben sirob taďakko guda uku taďan rintse ido tana mai ba'kin cikin yanda rayuwa da sakacin iyaye ya jefata, afusace tashiga 6alle marafan kwalaben kamar wadda ta tuna wani abu, jiki na rawa tashiga tuttula maganin abakinta kamar mai shan ruwa, kafin mu farga ta shanye kwalabenan ukku gaba ďaya,, abba ya girgiza kai yana jan numfashi da sauri,, tabbas yanajin tausayin halin da ameeda take ciki,, nikam kunsan mace da rauni saida nayi kuka.
    Tana gama sha ta 6ingire awajen tahau barci,, muma sai muka fito guywa a sanyaye.
   Ameeda bata farkaba sai bayan magriba, ta mi'ke zumbur tana kallon kanta kamar wadda aka sake, takai dubanta ga agogo, ido ta zaro dan ganin yanda lokaci yatafi idan zata iya tunawa tun 'karfe tara na safe take barcinnan, ta furta na shiga uku babu azahar bare la'asar, da hanzari tafice daga ďakin iya abu ce kawai atsakar gidan take tatar koko, ta shiga washe baki yauwa ameedan baba kin tashi??, kinga zoki 'karasa min tatar nan dama nagaji wlhy, ďan 'karamin tsaki ameeda taja ta wuce batarda tabi takan iya abu ba bareta  tanka mata, iya abu ta ta6e baki 'yar kwaya tanaji ina magana tamin shiru kai ALLAH yawadaranki Ameeda, kai kawai na girgiza ina faďin ohni abba wanan wace irin rayuwace akeyi agidanan???, naďanja tsaki domin babu mai bani amsa tunda bily yau bata nan nikaďai nazo ďaukar muku rahoto.
   Ina nan zaune saiga ameeda tafito daga bayi da'alama wanka tayi, ruwa ta ďiba abuta tayi alwala, ďaki tanufa batareda takula habaicin da iya abu take mataba,, sallolin da'ake binta tashiga ramawa, tadaďe tana addu'a da ro'kon ALLAH ya shiryata tadena mugayen halayen datake aikatawa, dakuma ro'kon ALLAH yabata miji nagari mai sonta da gsky, ta shafa sanan tafito waje.
    Zuwa sanan iya abu tagama tatar kokon tana zaune tana walfar tuwo abinta, ameeda taja kujera 'yar tsugunno ta zauna agefen iya abu,, tana kallonta amma ta share tacigaba da cin tuwonta, ameeda taďan murmusa dan tasan tana fushine akan abunda tayi mata ďazu, cikin taushin murya ta ce, "iya ina nawa tuwon??, saida iya abu ta haďiye laumar tuwonta jikake kutttttt sanan ta harari ameeda cikin masifa ta ce, "ban dafa dakeba,, murmushi ameeda tayi ta ce, "babu damuwa iya, taďanyi shiru zuwa wani lokaci saikuma taja numfashi tareda faďin iya dan ALLAH inada tambaya??, iya tai mata banza bata tankaba.
   Ameeda tacigaba da faďin iya wai ina 'yan uwanmu ne??, gaban iya abu yafaďi duuuuum arikice taďago tana kallon ameeda data tsura mata idanu, sai fidda numfashi take da'kyar ga gumi yafara bin sassan jikinta kamar wadda tahaďi kwaďo,, Ameeda ta ce, "iya yayadai ko tambayata ta 6ata miki raine??, da sauri iya abu take girgiza kai saikace 'kadangaruwa, tashiga kame2 A'a ameeda babu komai tambayarki bata 6atamin raiba, miye abin 6acin rai awanan tambayar kawaidai naji xancen nakine abazata shiyyasa......  ameeda tayi saurin 'katseta to iya kibani amasa mana ina danginmu suke?, kuma mu 'yan asalin wane garine??, inane tushenmu na asali??, cikin sar'kewar harshe ta ce, "kibari ba yanzuba watarana zan faďa miki, to waima miye dalilin wanan tambayar???.
   Ameeda tagyara zama tana faďin babu komai iya,, kawaidai ina son sanine, ina kuma mamakin tunda nataso bamu ta6a zuwa wani gari danufin ziyarar danginmuba, sai nan kano kawai nasani,, ahankali kuma nafara fahimtar bawata dagantaka mai 'karfi tsakaninmu da 'yan uwanmu nan kano, musamman idan nayi la'akari da irin halin danake ciki basu ta6a nuna damuwarsuba bare su tsawatar mini.
   Jikin iya abu sai rawa yakeyi kamar mai jin sanyi, Ameeda tana kula da'ita, tana mamakin yanda iya abu tashiga wani hali daga tambaya.
   Lalai akwai alamomin tambayoyi akan iyayen nata,, akwai wani 6oyayyan abu gameda tarihinta,, lokaci yayi dazatasan mi iyayenta suke 6oye mata, lokaci yayi dazatasan inda danginsu suke, lokaci yayi dazata nisanta kanta ga iyayennata, tasan duk tsiya bazata rasa wanda zai ri'keta acikin dangin nasuba harta samu mijin aure,, tayi al'kawarin koda a'kauye dangin iyayenta suke zata zauna dasu kuma tasamu miji acikinsu tayi aure,, tagaji da wanan tam6elen datakeyi, tasan kuma indai tana gaban iyayenta bazata ta6a daidaita rayuwartaba,, ta mi'ke batareda ta tanka irin lallashin da iya abu take mataba akan taci tuwon data zubo mata,, gyale taja akan igiya tafice abinta......................

Ku biyomu!!










©2017





Hikayarmu!!!!!!!
abba gana
             &
      bilyn Abdul
[11/02 20:11] Abba Gana: KUKAN KURUCIYA....





            NA 
MUH'D ABBA GANA
               &
BILKISA IBRAHIM {Bily}
   (Mrs Abdus'salam)




Page7⃣&8⃣


Sai yamma can Ameeda ta tashi daga nannauyan barcin daya d'auketa, takai dubanta ga agogon dake manne a d'akin falmata, 5:56pm ta zaro idanu tareda fad'in nashiga uku ni Ameeda ko sallar azahar banyiba, ta zabura daga gadon tana maida numfashi, bandaki tashige tayi wanka tareda yin alwala.
   D'akin tadawo tafara ramuwar sallah.
   Bata bar wajenba har saida tayi sallar isha'i, tun tana kabbaran farko  takeji ana buga k'ofa bayan ta kammala ta saka kayan falmata sannan ta bud'e d'akin tafito.
    Tayi turus dan ganin Naseer zaune, shima ayatsine yake kallonta yanata wani mazurai.
   Ta daure ta ce, "sannu da zuwa.
   Harara ya watsa mata taredajan tsaki, ya ce, " 'yar rainin hankali, shine kika wani kulle d'aki, anata bugawa kinyi banza da mutane.
    Ameeda tad'an tab'e baki kayi hakuri ina sallah ne.
   A'a d'awafi kikeyi, tun karfe 1 narana nake zarya agidannan falmata ta ce, "mini kina d'aki kwance, dan iskanci inata buga miki kinki ki bud'e.
   Lah wlhy barci nakeyi, kwata-kwata banjikaba, kaima kasan danaji zan bud'e aii.
   Harara ya zabga mata, yau kika fara shiga d'aki ki kulle ayita bugawa kiki bud'ewa, zaki kawomin wani tsarin banza.
   ka yi hak'uri, yanzu mike tafe dakai??
   Saida ya kurb'i giya sannan ya ce, "nazone dama nafad'a miki gobenefa zuwa abuja d'innan, dan haka ki kwana da shiri, dan kinada matuk'ar muhimmanci awajen faty d'inanan, kinsan dai yanda nake da ANAS, baikuma dace ace babu baby na awajen birthday d'insaba.
    Ameeda tad'an murgud'a baki, nidai tun ranar nagaya maka bazan jeba, dan haka kabar zancennan kawai, banaso yakawo mana b'acin rai, tafad'a tana mik'ewa, ni bari na wuce gida dare yanayi.

   ke k'aramar 'yar iska har kin isa nabaki umurni ki bijire? kodan kinga ina lallabakine??.
    Ameeda tayi masa kallon sama da k'asa ta ce, "To Nas kai ubanane dabazan bijirema umar ninkaba, kaima kasan idan har na ce, "bazanyi abu ba, to bazanyi d'inba", dan haka ka saurara mini, ina sauran 'yammatan naka kad'auki d'aya acikinsu mana ta rakaka.
   Nas ya finciko Ameeda cikin xafin nama ya had'eta da bango, cizo ta galla masa ahannu, da sauri ya saketa, ta nunashi da hannu kai Nas kasan nasha fad'a maka, duk iskancinka kadaina gigin tab'amin jiki, wlhy kashiga hankalinka, idan har bazaka iya fad'a min magana daga nesaba to ka saurara, niba 'yar iska bace kajiko!!.
    tana gama fad'a ta fice, atsakar gida ta tarar da falmata itada bad suna hira, kallo d'aya tamusu ta d'auke kai tana tsaki, daga nesa ta ce, "falmata nawuce gida saida safe.
   Falmata ta ce, "kai Ameeda bazaki kwanan anan bane??, ko yau bazakije club bane?.
   Ameeda ta yatsine fuska tana fad'in bazanjeba, inaso naje gida dan nafad'ama iya cewa zan dawo dawuri.
   To shikenan saida safe, falmata tafad'a.
   Bad ya ce, "Ameeda abin ko gaisuwa?,.
   "O, sorry ban kula dakai bane ykk?".
   Ya ce, "lfy lau, ya garin.
  Gaba tayi abinta ba tare da ta amsashiba.
   Bad yamaida kallonsa ga falmata, wai ita wannan k'awar taki miye damuwarta, kodai Nas ne ya b'ata mata rai??.
   Falmata ta ce, "k'ila hakane amma dama tun d'azu ranta ab'ace yake, shine dalilin dayasama ta d'au caji.
   Bad ya ce, "wlhy dani nakeson yarinyar can datuni na shak'ama shegiya koken, nayi abinda zanyi, narasa mike damun Nas da har yarinyarnan tafi k'arfinsa.
    Hummm kajika dawata magana, tunda bataso yazaiyi, wlhy nakula Ameeda bata buk'atar wannan harkar, dan ALLAH ku barta, indai dan ALLAH yakesonta to ya aureta kawai, amma indai ta wannan hanyarne bazai tab'a samun Ameeda yanda yakesoba.
   Habawa falmata bakisan Nas bane kawai, na tabbata wataran sai yakaiga samun nasara, kedai kisa idanu kisha kallo kawai.
   Dariya kawai falmata tayi dan tasan hakan bamai yuwuwa bane, tasan tasha cin kud'in Nas akan yanaso ta shawo masa kan Ameeda ta yarda dashi, amma takasa.

Aban garen Ameeda kuwa tana fita ta samu adaidaita ta hau, sai gida, sallama tayi tare da shiga cikin gidan babu kowa a tsakar gida, d'akin iya tanufa, amma babu kowa, saita wuce d'akinta kaiwai.
   Tacire kaya ta kwanta, babu dad'ewa ta fada duniyar tunani, tabbas indai tana tareda Nas bata tunanin zata shiryu, lokaci yayi dazata nisanta kanta dasu Nas, to amma iyayentama suna taka rawar gani wajen lalacewarta, kenan suma dolene ta nisancesu?, to inta bijire musu ta tafi ina zata?, a kano tatashi tayi wayo harta mallaki hankalin kanta, itadai batasan wasu 'yan uwansu dasuke nesaba, to miye mafita??.
   Zata cigaba da zama dasune?, kokuwa zata kama gabanta domin daidaita rayuwarta?, kullum shekarunta k'ara ja suke, tanaso tayi aure ta haifi yara, amma bata fata Nas yazama mijinta uban 'ya'yanta, wace hanya yakamata tabi domin gujewa auren Naseer??.
  Tajuya kwanciyarta zuwa rubda ciki, wayarta tad'anyi k'ara alamar shigowar sak'o, ahankali takai hannu ta d'auka, Nas ne yaturo mata sak'o.
    Ta ajiye wayar batareda sha'awar duba sak'onba, sai kuma ta d'auka ta duba.
     Ga abinda ke ciki....
   Hy babyna
Plz kiyi hak'uri da abinda nayi miki, nayi miki alk'awarin bazan sakeba, amma dan ALLAH kiyi hak'uri ki halarci birthday party  d'inan, dan wlhy duk cikin 'yammatan kece mai kala, kin fisu aji, kuma kece nake burin ki zama uwar 'ya'yana, dan nasan zasuyi alfahari dake a matsayin uwarsu.
   Saina jiki.
  I luv u my dear.
      Naki NAS!!!.

Tsaki tayi tana fad'in shasha sha ai wlhy duk dad'in bakinka babu inda zanje, kuma ni bana fatan kazama mijina, dan 'ya'yana bazasuyi alfahari dakaiba a matsayin ubansu.
  Taja tsaki tareda wurgar da wayar saman katifar ta.

Iya talek'o tana fad'in Ameeda sai yanzu??.
   Ameeda ta tashi zaune wlhy kuwa iya, amma nad'an dad'e da dawowa na lek'a d'akinki bak'ya nan.
  Eh naje  gidan malam D'anladi, matarsace ta haihu d'azu.
   Ayya ALLAH yaraya, mi'aka samu.
   Mace ta haifa tanana sarga d'ed'iya, iya tafad'a tana washe baki.
   Ameeda ta ce, "masha ALLAH.
  Kinci abinci ko, iya ta tambayi Ameeda??.
   Eh, kawai Ameeda ta ce, "mata.
  To aii shikenan, kinga bari naje nacinye wanda na ajiye miki dama wlhy bai isheniba.
    Ameeda ta girgiza kai kawai, danjin furicin iya abu, ta shafa cikinta tare da fadin  a cikin ranta wlhy yuwa nakeji ba k'aramaba, dan tun safe rabonta da abinci.
   Kud'i ta d'auka tafice, wajen wani mai shayi taje tasiyo soyayyar indome da kwai, da shayi, tazo taci takoshi, sannan tasamu sa'ida.
    
WASHE GARI
   tunda safe tashirya tabar gidan, dan tasan Nas zai iya zuwa yasa su iya su tursasata zuwa Abuja.
   Itako wlhy bazata jeba, gidan wata aunty ta tatafi, tawuni acan sai dare tadawo.
    
   ko hutawa batayiba iya abu ta shaida mata zuwan Nas, wai haryabasu kud'i, amma ransa ya b'aci daya tarar bata nan.
   Baki Ameeda ta tab'e ta ce, "matsalarsa ce kuma wannan, nidai tunda nace bazaniba ai dole a sauraramini.
   Tamik'e tashige d'aki tana mita...................

Ku biyomu!!.








©2017




Hikayarmu!!!.
abba gana
             & 
    Bilyn Abdul
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *