check your best novels here

Saturday 11 March 2017

SABON AL'AMAREE 27/30

[24/02 18:00] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》


®BILKEESA IBRAHEEM
         {♡Bilyn Abdul♡}


 Kuyi ha'kuri masoyana yanzu nazama lazy wlhy.
Luv u oll

27
......Da asuba tarigashi farkawa, wani haushi ya turni'keta dan ganin yanda ya wani kanainayeta ajikinsa, wannan ai iskancine tafaďa a zuciyarta tana hararar sa, shikam baimasan tanayiba dan barcinsa yakeyi, jikinta tayi 'kokarin zamewa daga nasa amma saiya farka, ya ce' "lafiya?, ko zazza6inne??, kai ta girgiza batareda tayi magana ba, ya ce, "to ina zakije??.
    Sallah zanyi".
Juyawa yayi yana kallon agogon dake manne a jikin bangon ďakin 5:11am mi'kewa yayi shima dan tuni Nurr ta tashi harma tashige bayi, shima tashi yayi yanufi ďakinsa domin yin alwalar.
    Koda tafito daga bayin saita sama 'kofarta key tana mita, nikamdai wlhy bazan sake yarda ka kwanarmin a ďakiba, wannan ma aii zubar da girmane, 'kato dakai kazo kana kwana aďakin 'kanwarka, aiko Saiff bazaiyi abinda kayiba wlhy mtsooowwww ta'kare maganar da tsaki mai 'karfi, (nace lallai yarinya zakiyi bayani, zakiga ainahin 'kato ađakinki nan gaba).
     Koda yadawo daga masallaci ďakinsa yawuce domin yin shirin office, dan yakoma aiki.
     Anty bily ce kawai da 'yan aiki suketa hada hadar haďa breakfast, itakam 'yargatan mai mijin tana gado tana sharar barcin safe, bayan sun gama komai 'yan aikin suka ida gyara gidan tsaf, 'karfe takwas dai2 ya mahmud yasakko anty bily ce kaďai afalon, taje ta tarbosa, jakkar hannunsa ta amso tareda gaisheshi, ya amsa yana 'kayataccen murmushinsa wanda har wushiryarsa ta bayyana, dinning suka 'karasa kamar yanda suka saba, ta haďa masa komai zuwa gabansa dukda bawani ci yakeba sosai, kofin shayi yaďauka yana juya cokali aciki, yaďago yana kallonta my bily wai ina Nurr ne??.
     Tayi ďan murmushi yaya aikai zan tanbaya Nurr tunda ďaki ďaya kuka kwana, amma inaga bata tashiba.
   Baice komaiba yacigaba dacin abincinsa, (azuciyarsa ya ce, "dolene na saitama Nurr zama agidannan, dan nakula har yanzu kanta yana rawa).
   Bayan ya kammala break yale'ka ďakin Nurr domin yay mata sallama, saiyaji ďakin akulle, dawowa yayi anty bily tarakashi har wajen motarsa saida taga fitarsa sannan tadawo, itama ďakinta takoma danta ďan runtsa.

Sai 'karfe goma Nurr ta tashi, bayan tayi wanka tashirya  tsaf sannan tafito, afalon ta iske anty bily itama ta tashi, ta 'karasa suka gaisa, anty bily ta ce, "kinga tashi kiyi break zama da yunwa babu 'kyau.
    To aunty na,  tafaďa tana mi'kewa.
Bayan ta kammala tadawo falon suka cigaba da hira da aunty bily, idan kagansu saika ďauka yaya da 'kanwane zuciyarsu fas babu irin ďan banzan kishinnan aransu, dan ita Nurr har yanzu tanama ďaukar kanta tamkar 'yar shekara gomane, bama takawoma kanta cewa zaman aure takeyi, itadai inbanda shirme babu abunda ta'iya, ALLAH dai ya shirya.
    Sai wajen 'karfe shabiyu aunty bily tashiga kicin tareda masu aiki, amma Nurr saima ta'kara gyara zama wajen kallon film ďin datakeyi.
   Anty bily tana kicin wayarta tashiga 'kara, Nurr dake kusada wayar ta ďauka ta duba, my handsome tagani an rubuta, baki ta ta6e tana faďin lallai anty bily bama kisan handsome ba, wannan mai 'katuwar fuskar kike cema handsome, (na ce kai Nurr akwai ita sheri dai), bata ďagaba saima tami'ke takai mata wayar, da sauri aunty bily ta ďaga dan ganin ya mahmud ne, ta ce, "my handaome yaya office??, Alhmdllh yafaďa, mikikeyine??, ina kichin mana domin 'ko'karin haďa maka abincin rana.
   Ajiyar zuciya yaja, sannan ya ce, "Nurr fa??, tana falo yaya yanzu nabarota tana kallo, baice komaiba yayi mata sallama, itama saita cigaba da aikinta batareda tunanin komaiba.
            Sai 'karfe biyar yadawo kamar yanda yasaba, zuwa sannan duk sun sake wanka, yaudai su Nurr anyi abinkai ansaka atanfa siket dariga sunyi ba'in kama jikinta saikace fenti, anty bily ce kawai tayi masa sannu da zuwa, amma Nurr ko kallo bai ishetaba, shima baibi takantaba ya haye samansa, anty bily ta ce, "Nurr tashi kikaima yaya ruwansha daganan ki haďa masa ruwan wanka.
     Nurr ta 6ata fuska kai anty ki 'kyaleshi kinsanfa shi ba ayimasa gwaninta, yanzu zaka masa abu ya kusheka nikam bazan iyaba, daka masa kuskure yace zai dakeka saikace wani ďan doka.
    Anty bily tari'ke kai, kai Nurr akwai gyara sosai a al'amuranki kinga tashi kije bazai kushekiba, nidai anty 'kyaleshi kawai indai wancan masifaffenne, garama na kalli film ďina wlhy, anty bily bata sake cemata komaiba tatashi tanufi ďakinsa, tana mai jinjina wautar Nurr azuciyarta.
  (Nace kaďanma kika gani indai 'yar mamace.
       
   Akwance ta iskeshi yacika yayi fam da haushi, ta ajiye tiren data ďoro ruwan a saman tebir ďin dake gaban gadon, ta ce, "sannu ya aiki?, banza yay da ita koma motsi baiyiba balle yabata amsa, batayi zuciyaba ta tsiyaya ruwa akofi taje bakin gadon tazauna kusadashi, yaya tashi ga ruwa kasha, ahankali yabuďe idanunsa cikin masifa ya ce, "saiyanzu kuka tuna dani??.
     A'a waya isa yamanta dakai yi ha'kuri dan ALLAH kar6i ruwan kasha, nakoshi yafaďa yana lumshe idanunsa dasuka nuna alamun gajiya, ruwan ta ajiye cikin sanyin murya ta ce, "kayi ha'kuri dan ALLAH my handsome, kasandai babu yanda za'ayi mu manta dakai.
    Zaki faďi haka kuwa, mintina nawa dashigowa gidan amma babu wanda yanemi inda nake, idan ita batada hankali "k saiki biye mata?, shiru tayi dantasan halin kayanta sarai, da'kyar ta lalla6ashi yasha ruwan sannan ta haďa masa ruwan wanka, itama ta taimaka masa wajen wankan, ta shafa masa mai ya shirya cikin farar jallabiyya suka sakko falon............




Luv u oll my fan's.
©2017
[24/02 18:11] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》



®BILKEESA IBRAHEEM 
     {♡Bilyn Abdul♡}


28

.....Sanda suka sakko tuni Nurr tabar falon, shima masallaci yatafi domin yin sallar magriba, dama sai anyi isha'i yake dawowa, har sannan Nurr bata fitoba, anty bily ta haďa masa abinci ta ce, "bismillah bari nakira Nurr.
    Hannu yaďaga mata yana faďin yi zamanki, ita dan iskanci kullum sai ankirata wajen cin abinci, karta fito tayita zama aii cikinta zatakai bana waniba.
   Badan aunty bily tasoba takoma ta zauna sukaci abincin, har suka gama Nurr bata fitoba, tana ďaki abinta kwance kuma ba barci takeyiba idonta biyu badai tayi niyyar fitowa bane.
    Bayan sun gama anty bily ta ce, "yaya dan ALLAH bari naje nayima abba sannu da zuwa, dan inaso muyi wata magana dashi kafin yasake barin 'kasar.
   Okey, amma kibari sai gobe mana.
    A'a yaya gara naje yanzu kasansa dai zai iya wata tafiyar gobe.
   Okey to kigaida manasu, ďazun nashiga ni mungaisa, mi'kewa tayi tana faďin zasuji, ya ce, "o, dama kice saida kika shirya sannan kika nemi izini, dariya tayi tana faďi afuwan my prince, shima dariyar yayi ya ce, nayi my dear.
   Mi'kewa yayi bayan tafiyarta yanufi ďakin Nurr, tana kwance a saman kujera idanunta suna kallon sama, da alama tana duniyar tunani, harya shigo yazauna bakin gadon bata saniba.
    Yasan tana tunanin iyayentane, yana ganin yakamata su dady sanar da'ita kodan tasamu nutsuwar zuciya, koba komai zata yima iyayenta addu, gyaran murya yayi sannan tasan da shigowarsa, ta tashi zaune amma bata kalli inda yakeba, shikam sai binta da kallo yakeyi dan ganin yanda taketa cin magani, ya girgiza kai tareda 'kara tsare gida dan soyake yakafa mata dokoki.
   Ya ce, "k".
   A 'kasan ma'koshi ta ce, "na'am.
Bai damu da yanda ta amsa masaba yacigaba da faďin waye sa'anki agidannan?.
      Saida ta kalleshi sannan ta ce, "babu.
   Mikike nufi dazaman ďaki kullum sai anzo ankiraki wajen cin abinci?.
   Baki ta zum6ura ta ce, "nifa bance dole idan zakuci abinci saikun kiraniba, le6ensa ya cije dan yalura saiya buďe mata wuta tunda lallami baya mata.
    Cikin tsawa ya ce, "kishiga hankalinki dan wlhy yanzu xan ďumamamiki jiki, dan rashin mutunci ina miki magana kina maidamin yanda kika gadama ko?, daga yau yazama nafarko na 'karshe dazan miki magana ki mayarmin, nakula duk aikin gidannan bilkeesu ce takeyi saboda "k bakida kunya, kullum kina kwance saidai a tasoki kici  ki koma gado, bakisan idan nadawo gidan nan kimin sannu dazuwaba, bakisan ki ďebo ruwa kibani nashaba, bakisan gari yawaye ranar girkin ki kije ki gyaramin ďakiba, a'a "k abinda kika sani shine kici ki kwanta kiyi barci kitashi kiyi kallo ko??.
    Haka kikaga su mama sunayi agida?, haka zakiyita rayuwa kina ďaukar kanki amatsayin 'karamar yarinya, duk wannan ayyukan babu wanda bakwayi agida, amma nan saboda kin samu maiyimiki shine zaki 'kiyi, ďazufa saboda raini kina kallo nadawo bily tayimini sannu amma "k ko kallo ban ishekiba saboda raini, daga 'karshema saikika baro falon kika dawo ďaki saboda ma'kiyinki yadawo gidan?, sai bily ce takawo min ruwansha ďaki.
   Tunda yafara maganar take kuka amma saboda tađan karkatar da fuskarta bai kulaba.
   Yacigaba da faďin kinsan halina sarai dan haka wlhy kishiga hankalinki niba sakaren miji bane da zan zauna mace tafi 'karfina, inhar kinaso mu zauna lafiya dolene kiyi abinda nake bu'kata, tunda na auri bily bata ta6a tsallake umar nina ba, duk abinda nakeso shitake so kafinma nace taimin tatashi tayinshi.
    Daga yau duk safiya kitashi aringa haďa break dake kafin natafi office, dolene idan ranar girkinkine ki haďa min ruwan wanka, kibani break naci, idan nagama kirakani har wajen mota, kidawo ki gyaramin ďaki, dolene ki girka abincin rana akaimini office, idan nadawo ki tarbeni kirakani har ďakina, kibani ruwan sha, ki haďa min ruwan wanka, "k wankanma idan takama kece zakimin, da sauri tajuyo tana kallonsa, yasake tsare gida.
    Daga yau karna sakejin sai ankiraki wajen cin abinci tunda ita ba sa'ar ki bace, inko hakan tasake faruwa ranki sai yayi matu'kar 6aci, kinsanni kinsan halina duk abinda na lissafo miki babu ba'konki aciki.
   Nurr ta ce, "har yimaka wankan?.
   Fuska ya'kara tamkewa ya ce, "eh, Nurr tafashe da kuka tana faďin ni wlhy ba 'yar iska bace,
Da sauri ya mi'ke yanufi inda take ubanwaye ďan iskan to??, filon kujera ta ďauka ta kare fuskarta dan gudun kartaji saukar mari, ga kuka tanayi, ya ce, "wlhy ki haďiye wannan kukan kafin nakashe fuskarki da mari, ubanmi aka yimiki dazaki tasa mutane gaba kina faman rusar kuka yafaďa yana fisgo filon data kare fuskarta dashi.
   'Kuuttt ta haďiye kukan dan tasan yanda ya fusata ďinnan ba 'karamin aikinsa bane ya saukema fuskarta marin.
   Ya ce, "maza tashi nabaki minti uku kishiga bayi ki wanke fuskarki.........kafin ya 'karasa harta kai hanyar bayi, dama hanyar guduwa take nema, yana nan tsaye tafito, amma saita dogare a 'kofar bayin, hanya yanuna mata batareda yayi maganaba, sum2 tafice falo shima yatake mata baya, ya ce, "wuce kici abinci.
   nifa na 'koshi tafaďa cikin rawar murya.
   inda take yanufo tako zura da gudu hanyar fita, a'kofa sukaci karo da anty bily da sauri tari'ke Nurr dasuke 'kokarin yin karo, Nurr lafiya dai??, hawaye suka zubo mata ta ce, "ya Mahmud ne, bily tamaida kallonta gareshi yayi kicin2 da fuska babu alamar wasa, taja hannunta suka 'karasa cikin falon, tsawa yadaka ma Nurr wanda tasakata dur'kushewa ita kantta anty bily ďin saida ta tsorata, ya mi'ka mata filet ďin abinci daya zuba, ya dangwarar agaban ta minti goma nabaki kicinyeshi tas, Nurr dake kusada anty bily ta fashe da kuka ni wlhy bazan iya cinye wannan avincin ba, karki iya yafaďa yana nifota da cajar fitila ahannusa, ta ko 'kadandane aunty bily tana kuka, aunty bily tashiga ro'konsa akan yayi ha'kuri ya 'kyaleta karya daketa.
    Ki bari bily gara na koyama yarinyar nan hankali iskancinta yafara isata, dukda hakadai kayi ha'kuri aizataci, tsaki yaja yakoma saman kujera yana kallon labarai.......................



Luv u oll my fan's
©2017
[26/02 11:21] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》



®BILKEESA IBRAHEEM 
       {♡Bilyn Abdul♡}



29

......itama anty bily taja hannunta suka zauna tabata tahau ci, data tsaya dacin abinci alamar ta 'koshi sai aunty bily ta nuna mata ya Mahmud da idanu, haka tayita tura abincin harta cinye, dama yunwa takeji kuma abincin daya zuba mata baifi 'karfin cikintaba, kawaidai 'yan rashin arzi'kinne akanta, bayan tagama takai filet ďin kichin tadawo zata wuce ďaki.
   Ya ce, "dawo nan ki zauna.
    Ta ce, "barcifa nakeji.
  Kidawo kizauna nace, duk maganar dayakeyi idonsa nakan tv, anty bily ta nuna mata da hannu tadawo ta tazauna, dawowa tayi tazauna tana kunkunai.
   Bayanda zatayi dole ta zauna harya gama kallon labairai yatashi sannan suma kowacce tanufi ďakinta.
    Tana shiga tasakama 'kofarta key tana faďin wlhy bazan sake kwana da 'katon gardi a ďakinaba gara tsoron yakasheni, koda yake dije mai aiki zan kira taringa tayani kwana naga tsiyarka masifaffe kawai, wanda idan ba bala'i yayiba baya jin daďi.
    Shikam koda yaje ďakinsa shirin barci yayi yanufo ďakin Nurr amma saiyajishi akulle, kai kawai ya girgiza yakoma đakinsa.
   Andaiyi sa'a yau tatashi ta haďa masa break da taimakon aunty bily, amma ko saving nasa bata tsaya tayiba takoma đaki tai kwanciyarta, sai anty bilyce tabashi abincin amma ita tuni ta tsufa aďaki, baice komaiba yazauna yaci abincinsa yatafi office, yasan dolene saiya 'kara ha'kuri da Nurr akwai sauran lokaci dazata bambance fari da 'ba"ki, shekara sha shidda aiko da sauran 'kuruciya.
  
 Haka rayuwar tacigaba da tafiya, balaifi Nurr tana rage wasu abubuwan na rashin hankali saboda tsoron ya mahmud datakeyi.
   Yauma takasance weekend ranar kuma girkin Nurr ne, amma ko kaďan bata farin ciki da hakan, tana shiga matu'kar damuwa duk ranar dayake ďakinta, bata iya barci ko kaďan saboda fargaba, har yanzu kuma takasa kiran dije mai aiki ta tayata kwana, amma yau taďauki aniyar kiranta komai tafanjama fanjam.
       Suna zaune afalo itada aunty bily suna hira, shikuma mai gidan yana đakinsa dan yanzu ya fahad yafita bayan sungama tattaunawa, mai wankinsu yay salkama suka amsa tareda bashi izinin shigowa,  yashigo hannunsa rungume da kayan wankin ya Mahmud dayayi yau, saida ya gaishesu sannan ya ce, "ga kayan oga hajiya, anty bily ta ce, "to ďanliti sannu da 'ko'kari, Nurr tashi ki kar6a ki kaimasa ďaki.
    Nurr jitayi kamar ta fasa ihu amma yazatayi tanajin kunyar aunty bily kodan hidimar datakeyi da'ita.
   Tashi tayi takar6a tana faďi ďanliti ai kayan da nauyi, dariya yayi eh hajiya akwai nauyi amma ai zaki iya, hakadai kace tanufi saman ya Mahmud tana faďi, tana mama kin irin turaren da ya Mahmud yake amfani dashi, dukda wankin da kayan suka sha amma sai zabga ďan karen kamshin turaren sukeyi, kamar yanzu aka saka, taja birki a 'kofar falon dan fargabar abinda zata tarar, tana tunanin ta kwan kwasa kota juya, to amma idan tajuya yazatayi da waďannan kayan??, tasan aunty bily tana falo a zaune.
    Ahankali ta kwankwasa 'kofar dan batayima zaton zaijiba, ta 'kara tabiyu, takai tsawon minti biyar agurin ba'a buďeba, harta đaga 'kafa zata juya aka buďe kofar, da sauri ta kalli wajen, gogan nakune tsaye dagashi sai guntun tawul ďaure a 'kugunsa da alama wanka zaishiga, tayi saurin yin 'kasa da kai, dan bata ta6a ganin namiji ahakaba tunda take, koda suna gida yayyen nasu basa zama haka, ko gajeren wando basa fitowa dashi garama jallabiya da wando iya gwuywa.
   Yalura da kunya takeji amma saiya basar ya matsa mata alamar ta shigo, kanta sunkuye ta shigo falon shikuma yamaida ďakin yakule.
   Saman kujera tayi yun'kurin ajiyewa, yay saurin faďin karki sake ki ajiye min kaya anan gurin.
    Cikin dauriya ta ce, "ina zankai to, yanda tayi maganar muryarta babu tsoro saida tabashi mamaki harya ďago yana kallonta, amma saiya danne mamakinsa ya ce, "a ina kike kai kayanki, ta ce, "bedroom acikin dirowa, baice da ita komai ba yay gaba zuwa cikin bedroom.
    Kular datayi bashida lokacinta yasa ta take masa baya, sanda tashiga ya cire tawul đin yana kokarin saka gajeren wando, da sauri ta watsa kayan saman gado zata gudu, yay saurin daka mata tsawa "k wanne irin shirmene wannan kobakiga yanda kika yimin da kayabane??, tsayawa tayi jiki narawa ta ce, "sorry kuskurene, tsaki yayi yace dawo ki gyarasu kuma adirowa nake son ganinsu yafaďa yana zura jallabiya, dan yakula ganinsa datayi ahaka yasakata tsorata,.
   Zuwa tayi tana tattara kayan, tabbas ya Mahmud yana burgeta awajen tsafta, mutumne mai tsafta da son gayu, ko 'kafarsa ka kallah kasan ya haďu wajen tsafta dajin daďi, saidai zuciyace babu 'kyau sai ba'kar mugunta dason girman tsiya, tagama gyarawa ta ďiba zuwa dirowa, ya ce, "ai nan zaki ajiyesu kiringa ďauka da ďai2.
     Saida ta murguďa baki sannan ta ajiye amma bai ganiba, dirowar tabuďe tana kallon ikon ALLAH, komai na dirowar atsare yake, shaddoji wajensu daban, sut wajensu daban, 'kananun kaya wajensu daban, jallabiyoyima haka, kai komaidai atsare kuma ajikin hanga, gawani 'kamshi na musamman mai daďi yana fita acikin dirowar, hankalinta nawajen kallon dirowa yashigo, dan da yafita, kamar daga sama taji yace aikin dana sakaki kenan?.
    Da sauri tajuyo tana kallonsa cikin rawar murya ta ce, "yi ha'kuri ina duba inda zansakane, ya ce, "kodai kina kallemin sirrin dirowane??, kai ta girgiza tana faďin a'a wlhy, yaďan ta6e baki to kiyi aikinki.
    Kayan ta ďauka zuwa dirowa amma tarasa yanda zatayi tasakasu, karasowa yayi wajen dirowar ya tsaya bayanta tamkar zai rungumeta, yami'ka hannu yaďau hanga ďaya ya nuna mata yanda zatayi, batace komaiba tacigaba dayi yanda ya nuna mata, saida tagama lodasu tas sannan.
   Tana cikin ďan gyara musu zama idonta yakai kan rigar daya kwace kwanaki ahannunta randa yatarar suna faďa ita da deena, rufewa tayi dan yana tsaye yana kallonta, amma tađau alwashin wataran saita sace rigarnan dan tana sonta sosai.
    Bayan ta kammala ya ce, "shiga bayi ki haďamin ruwan wanka, ido taďago tana kallonsa yaďan ďaure fuska, da sauri tawuce bayi shikuma yafara zame kayan jikinsa, ruwan tahaďa masa agurguje tafito a'kofar bayin taci karo dashi, dagashi sai guntun tawul iya cinya na ďazunnema ya mayar, 'kasa tayi da kanta tawuce sum2 tamkar mara gsky.
    Yabita da kallo kayan sunmata 'kyau amma sun matseta sosai, yarinyar akwai jikin mata. (kwalelenka ya Mahmud)..............





Luv u oll my fan's
©2017
[26/02 11:31] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》



®BILKEESA IBRAHEEM
       {♡bilyn Abdul♡}


30

........da daddare bayan sun gama kallon labarai kowa yanufi ďaki, dama ita Nurr ko hira suke bata saka musu baki, shimaďin bakomai yake faďa kai tsayeba saidai ata'kaice, wani sa'in har soyayya sukeyi agabanta amma ko kallo basu ishetaba, idan tagama suna abinda yafi 'karfin tunaninta tashi take tabar wajen, ita kallonma 'yan iska take musu.
   Tagama shirin barcinta tsaf, sannan taje kiran dije mai aiki danta tayata kwana, duk da dije mai aiki tana tsoron abinda zaije yadawo wannan bai hanata cika umarnin Nurr ba, katifa tasaka atsakar ďakin ta kwanta, itakuma Nurr ta haye gado, babu daďewa barci yay gaba dasu.
     Wajen 'karge goma nadare ya Mahmud yakammala duk abinda yazamana na al'adar rayuwarsa, yay shirin barci, yakashe komai yanufi ďakin Nurr, key yasa yabuďe, dan tunda tafara kulle masa 'kofa saiya nemi wani key ďin, dayazo saidai yabuďe yashige batareda ya kwankwasa ba, saidai tafarka taganshi kokuma da asubahi, turus yayi danganin mutum kwance atsakar ďaki, yaja numfashi tareda cije le6e, 'karasawa yayi jikin gadon yazauna gefen ta, yana mai mamakin mike damun yarinyar nanne??, Nurr! 'k Nurr!!, maimakon Nurr tafarka sai dije tafarka,  afirgice take kallon ya Mahmud.
    Cikin rawar murya ta ce, "sannu alhaji.
   Yauwa ya Mahmud yafaďa tareda faďin dije lafiya naganki anan?.
   Taďan sosa gefen wuyanta ta ce, "anty ce tace nazo natayata kwana wai tanajin tsoro........kafin tarufe baki Nurr ta tashi, dama indai ana magana akusa da ita komin nisan barcinta saita tashi, cikin mamaki take kallonsa, ta maida kallonta ga dije datake naďe kayan shimfiđarta, a'a dije ina zakije??.
    Anty zan koma ďakinmu dije tafaďa.. 
   Kamar ya xaki koma ďakinku?, bani na ce, "kizo kitayani kwana ba?.
   Harara ya Mahmud ya watsa mata......gum tayi dabakinta, ya maida kallonsa ga dije kinga yitafiyarki, to Alhaji saida safe dije tarissina sannan tafice, tashi yayi yarufe ďakin yadawo saman gadon yakwanta batareda yabi takan Nurr ďinba dake zaune tana binsa da kallo tamkar gunki, addu'a yayi tareda jan bargo ya lullu6e jikinsa, Nurr ta watsa masa harara amma bai ganiba, sakkowa tayi takoma saman kujera ta kwanta.
    Ya Mahmud ya ce, "k dawonan.
   Ta tashi daga kwanciyar datayi tana zum6ura baki nidai kabarni na kwanta anan, ya za'ayi muringa kwana waje ďaya.
   Tashi yayi zaune kinsan ALLAH idan baki tasoba nazonan saikin raina kanki, "k wai miki ďau kankine?, yafaďa cikin matu'kar masifa, tashi tayi takoma kangadon, ya fusgota jikinsa yafatse sosai, "k kina ganin idan kinyi hakan shine zaisa na 'kyaleki??, idan nayi niyyar kusantarki kota 'karfine zan aikata hakan, matata kike inada hakkin dazan kar6i hakkina najikinki kota halin 'ka'ka, bawai na 'kyaleki bane saboda wayonki, yaďan sassauta mata ri'kon dayayi mata, wlhy daga yau kika 'kara kawo mini wata daniyyar ta tayaki kwana saina kacaccalaki a wannan daren, idankuma kinji 'karya kisake aikatawa ya hankaďata saman filo yana faďin iskancin banza kawai!!!!!.
     Ya koma ya kwanta.
  Kifewa tayi tana garshe'kar kuka, juyowa yayi yana faďin wlhy kiyi maza ki haďiye wannan kukan kafin jikinki yayi tsami a wannan daren.
    Ai dawuri ta haďiye kukan tasan zai iya bubbugeta, ya ce, "oya kwanta, filo tajawo ta kwanta yaja bargo ya lillu6esu yana faďin ko shashsheka banasonji danhaka kiyi barci kokuma yanzu kisha mamaki, dama yara nakeso kinga adarennan da izinin ALLAH saina baki cikin ďana.
    Gabantane yafaďi rass plzzz yaya kayi ha'kuri zanyi wlhy, ya ce, "ato kidaiyi mai yuwwuwa, dole tabi abinda yakeso dan bata fatan abinda zai shiga tsakaninsu, jira take kawai daddy yadawo daga tafiya taje yaymata bayani akan iyayenta.
   Tana gama jin tushenta zata mi'ka bukatarta asa yasaketa, dan wlhy bata sonsa bakuma zata iya zama dashiba.
                          Tuni barci ya kwasheta, amma shi yakasa barcin tuni yafaďa duniyar tunani, shi yanzu wace hanya yakamata yabi wajen kwantarma da Nurr hankali, bai ta6a soyayyaba sai akan Nurr, tun tana 'yar 'karamarta yake 'kyaunarta, ita kaďai yabama dukkanin soyayyarsa, tuni zuciyarsa take mata 'kauna mai zafi yana dannewane saboda gudun tashin hankalinta, domin sannan tana masa kallon wanda suka fito ciki ďaya, yarinyar tana bashi matu'kar tausayi saboda hali irinna mahaifinta, yana burin nuna mata soyayya nagartacciya maikuma tsafta, saidai shirmen yarinyar yayi yawa, har yanzu 'kuruciya tana ďawainiya da ita, yasan yanason bilkeesu amma bakamar Nurr ba, yana yima yarinyar wata irin zazzafar soyayya, yana kwaďayin ďan ďana mata zumar irin son dayake mata, ya kalli yanda takoma can 'karshen gado tawani takure jinta, ya rungumota zuwa jikinsa, ajiyar zuciya yasaki danji lallausar fatarta ajikinkinsa, azuciyarsa ya ce, "ALLAH yakaimu randa zakiyi hankali my love! Burina nabaki cikin baby na ki haifa min, wannan shine cikon farincikina Nana maryam.
   Itadai batamasan yanayiba dan barcinta takeyi.
  Da asuba yarigata tashi saida yayi alwala sannan yatada ita yafice masallaci, bayan ta idar da sallah haka ta daure tafito taďora breakfast ďin safe, anty bily tafito ta tayata kamar yanda tasaba, bayan sun kammala kowa tanufi ďakinta, barci suka koma tunda weekend ne.
    Sai wajen 'karfe tara da rabi suka tashi, ya Mahmud yaďauki waya yana kiran Nurr wai tazo ta haďa masa ruwan wanka, saidai wayar bata shigaba, har yafarajin haushi saikuma yayi wani tunani, ai tunda aka kawota gidan baiga waya ahannuntaba ma, toko ta 6atarne?, yafaďa yana sakkowa, dakansa yahaďa ruwan wankan yayi sanan ya sakko 'kasa.
   Ďakin aunty bily yafara shiga ya rungumeta tsaf yana faďin i miss u my bily, murmushi tayi tareda faďin miss u too my handsome, janta yayi bakin gado suka zauna, ya manne bakinsa da nata yana nuna mata soyayyarsa mai tsafta da nagarta, adai dai wannan lokacin kuma Nurr tashigo ďakin daniyyar tada aunty bily daga barci idan bata tashiba, hazbinannahu wa'nimal wakil tafaďa kamar wadda taga wani abu, ya Mahmud yaďago idanunsa dasukayi jaa yana kallonta, dagudu tabuďe đakin tafice.
   Aunty bily ta ce, "my handsome kaga abinda nake gudu ko??, bai tanka mataba saima maida bakinsa dayayi kan nata yacigaba da abinda yakeyi, babu yanda zatayi mijintane dolene ta taimaka masa dan tasan yana matu'kar bu'katar hakan, tundashi mabu 'kacine, saida yagama lugiyguytata san ransa sannan ya'kyaleta.
      Nurr kam tuni taje ďakinta, saman gado ta haye ta rufe fuska wai yau taga iskanci, itakam wlhy yau gida zataje sai kuka takeyi, tana nan zaune ya Mahmud yashigo, ta'kara 'kudundune kanta acikin gyalen data yane kanta, gadon yahawo yana faďin "k suwaye 'yan iskan???.
    Bakinta bai mutuba ta ce, "kumana, wlhy ni gida zani bazan zauna aringa iskanci agabanaba.
   Janyota yayi jikinsa ya manneta sosai...............


Luv u oll my fan's
©2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *