check your best novels here

Saturday 11 March 2017

SABON AL'AMAREE 43/45

[09/03 16:01] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》







NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡bilyn Abdul♡}





44

.........ya Mahmud yasanarma Aunty bily cikin raďa, rungumeshi tayi tana hawayen farin ciki, shima ya rungumeta yana lallashinta.
    Ta ce, "yaya ALLAH ya inganta mana muma muga ďan kanmu aduniya, muma musamu abokan 'kiriniya agidan, ALLAH yabaki lafiya Nurr ďin mama kinji.
    Amin my bilyna, ya Mahmud yafaďa cikin wasu 'yan kwalla na farin ciki, haka sukaita murnarsu su biyu dan Nurr tayi barci batasan hidimar da akeyiba.
    Da 'kyar ya iya fita yayo sallar isha'i, itama aunty bily aďakin Nurr tayi tata, bayan yadawo suka tasata gaba suna kallo, sai wajen sha ďaya yaga aunty bily tana gyangayďi, ďaukarta yayi yakai ďaki, yana ajiyeta tana buďe idanu, yaďan kashe mata ido ďaya kin tashine?.
   Taďan murmusa badoleba my handsome, takamo hannunsa ta zaunar kusada ita, my handsome yau ba ranar barci bace, ranar mi'ka godiya ga ALLAH ce dakuma ro'kon ya inganta mana abin farincikin daya azurtamu dashi arana ta farko damuka kai azumin ramadana.
    Ya Mahmud ya sumbaci kumatunta tareda rungumeta hakane my bily, shiyyasa akulum nake 'kara sonki, insha ALLAHU zanyi yanda kikeso, amma ina fargaba wlhy, banason abinda yafaru abaya ya'kara faruwa yanzu.
    Ta shafo sajen dake kwance luf a fuskarsa, ka kwantar da hankalinka my luv insha ALLAHU a wannan karon zamuga ďan kammu inaji ajikina damuwarmu ta 'kare.
   Ya 'kara rungumeta sosai yana mai farinciki, daga nan aka zarce soyayya dama yana bu'kata tunda andaďe ba'a haďuba)
        
  Bayan lafawar komai yashiga bayinta yay wanka sanan yakoma ďakin Nurr, kusada ita yazauna tareda rungumeta tsam ajikinsa, sai kisses yake bata ako ina na sassan jikinta (nace malam da idonta biyu bazata yardaba, dan nasan hali) ya tsurama fuskarta ido yana ďan murmushi, Nurrina sarkin rigima, to yanzu koda rigimar wa zanji?, taki kota Babyna mai zuwa, yakuma bata kiss a ďan matsakaicin bakinta, taďan motsa kaďan....yari'ke hannun da aka saka mata 'karin ruwan, barcinta tacigaba dayi.
   Shikam yana kusada ita yanata sambatun farin ciki, saidaga baya yami'ke yay Alwala, sallah yashiga jerawa ta godiya ga sarkin sarakuna, "UBANGIJIN" talikai, mafificin sarki mai 'kyauta da 'kari.
   Ranardai ya Mahmud da aunty bily akan sallaya suka kwana, saida sukayi sallar asuba bayan sahur sanan suka kwanta damma weekend ne.
   Itama Nurr ta lalla6a tayi sallar dan tun dare ya Mahmud yacire mata 'karin ruwan bayan ya 'kare.

12:23pm 
     Jikin Nurr yarikice sosai, dole ya Mahmud ya sa6eta yakai mota asibiti suka nufa shida aunty bily, ita take tu'kin shikuma yana baya rungume da Nurr, har wani shiďewa take saboda amai data zazzaga saka makon shan wani shayi da ya Mahmud ya takura mata.
    Taimakon gaggawa aka shiga bawa Nurr, ya Mahmud sai safa da marwa yake yakasa zaune yakasa tsaye.
   Aunty bily ce ta sanar dasu mama, aiko cikin 'yan mintina suka iso, aunty bily ta gaishesu, suka amsa suna tambayar yamai jikin??.
   Da Sau'ki, amma tana tareda doctor.
   Ya Mahmud ya"karaso yana gaishesu, daka kalleshi kasan yana cikin damuwa, mami tari'ke hannunsa tana kwantar masa da zuciya, ka kwantar da hankalinka Mahmud insha ALLAHU babu abinda zai faru, amma miya sameta haka da zafi?.
    Yaďan cije le6e tareda faďa musu abinda yafaru jiya, mama taji daďi har cikin zuciyarta amma batace komai, saidai addu'ar samun lafiya datayima Nurr, mami kam ta nuna farincikinta afili, harma taďora da addu'ar ALLAH ya inganta, a la66ansa ya ce, "amin mami.
   Sai kallon mama yake dan yaji batace komaiba, ganin irin kallon dayake mata yasa ta ce, "ALLAH ya inganta ita, kuma yabata lafiya.
   Mami ta ce, "amin".
 Shima azuciyarsa ya ce, "amin mamana.

Bayan wasu 'yan mintuna Dr yafito yake sanar dasu tasamu barci, dan haka su kwantar da hankalinsu, tee ďin data shane yajawo aman.
    Ya Mahmud ya ce, "Dr zamu iya shiga muganta.
   Eh babu damuwa zaku iya shiga amma kada ayi mata hayaniyafa.
    Kafin yarufe baki mama takai cikin ďakin, tsaye tayi abakin gadon tana 'karema Nurr kallo, tayi wata fayau da ita sai wani uban haske data 'kara, amma ta rame sosai gsky.
   Ta ce, "tadaďema bata lafiya ko?....tafaďa tana kallon ya Mahmud.
    A'a mama jiyane abin yasameta bayan ansha ruwa, kuma Dr yaje yadubata, yanzunema jikin ya rikice.
    Mama tazauna kusada Nurr tana mai addu'ar ALLAH yaba autarta lafiya, mami ma da aunty bily suna mata addu'ar samun lafiya.
    Babu daďewa saiga deena ta zo itama da 'katon cikinta daga gani dai haihuwa na kusa da isowa, ya Mahmud ya ce, "deena daga ina haka?, taďanyi murmushi tana zama yaya naji usainata babu lafiya ina zan iya zama ban gantaba, mama tashafa kan deena autana aida kinyi zamanki yakamata kidaina yawo hakanan kinji.
   Ta gyaďa kai tana murmushi ta gaidasu da tambayar maijiki, suka amsa da faďin da sau'ki, nandai suka zauna kowa yana jimami, saida aka kira sallar la'asar sanan ya Mahmud ya ce, "yakamata aunty bily tatafi gida itada deena, suma sumama haka shi saiya zauna anan.
     Mama ta ce, "A'a kaje kai ni zan zauna, kata6a ganin namiji da jiyyar mace.......kafin yayi magana Nurr ta farka, taďan buďe idanu tana binsu da kallo ďaya bayan ďaya, sukuma suka shiga yimata sannu, kai kawai take jinjinawa.
   Mama ta ce, "zaki tashi zaune ko?, nanma kai ta jinjina, mama ta taimaka mata ta tashi tajingina da filon, ya Mahmud yace zakici wani abune?, taďan yatsina fuska dadai zan samu ďan sululu.
     miye kuma ďan suslulu??.
    Deena tayi murmushi wani abune da ake sayarwa amakaranta sanan muna D/Z.
    Mama ta ce, "to yanzu za'a samu anan?, deena ta ce, "kai dakamar wahala dan gsky saida mukaje can muma muka sanshu, kuma tunda muka baro ban sake ganiba, amma ai zan iya yi da alabo akeyi.
   Mami ta ce, "aida sau'ki saiki tashi kiyomata idan akwai alabo ďin awajenki.
   Ya Mahmud ya ce, "A'a mami atausaya mata, itama ai ba lafiyar take dashiba, ta kwatantama bilkeesu yanda akeyi saitayo mata, A'a yaya zan iya saidai kawai asiyo alabo ďin, kokuma nakira khairat tunda itama ta'iya.
   Yauwa to kira khaarat ďin nibari naje nasayo garin alabo ďin, yafaďa yana nufar 'kofar fita.
   Mama ta ce, "Nurr ahaďa miki shayi kisha kafin akawo miki abin ko?, ta girgiza kai ALLAH mama idan nasha amai nakeyi, đazuma da yaya ya tsareni nasha haka nayita amai.
       to yanzu babu abinda kike sha'awa kuma, dan kafin agama kinji yunwa kuma?, ta girgiza kai A'a mana bakinama ďaci yakemin  ko ruwa bana sha'awar sha, ďan sululun kawai nakeson ci.
    Shikenan mama ta faďa, ALLAH yasa yay saurin kawo alabo ďin, sukace amin, aunty bily da mami suka tafi gida saboda tanadar abin buďa baki, babu daďewa khairat tazo ta rissaina ta gaida mama, mama ta ce, "yauwa kunga kuzauna tareda ita bari naga likita, sukace to.
    Mama na fita khairat ta ce, "Nurr miye sirrin?, ko kema kin kamu?.
   Nurr ta harareta, nakamu da ubammi 'yar isaka??, suka shr'ke da dariya harda tafawa, ko kinkamu da babyn mu?, Deena tafaďa cikin dariya.
   Kwajidai da iskancinku, zazza6ine kawai yakamani fa, khairat ta ce, "to aidama da zazza6in ake farawa 'yammata, gaya mana gsky kodai ya Mahmud yabada tsarabane.......shigowar ya Mahmud ce ta katse ma khairat zancen, kuma yajisu sarai, khairat ta rissina tana gaisheshi, ya amsa yana faďin kedai ba'a ganinki ko?, khairat tayi dariya a'a yaya ina nan kawaidai......kawaidai mi?
   Nanma dariya kawai tayi, ya ce, "to ga alabo ďin, kije kiyo da sauri dan Nurri yunwa takeji, Deena da khairat suka kalli zuna suna murmushi, yaya ai wannan yayi yawa, a'a baiyi yawaba kije dashi duk sanda ta bu'kata sai kiringa yomata, to shikenan bari naje nayo, okey amma deena tashi kema ki tafi gida hakanan.
    Lah yaya kabarni bafana azumi kuma daga gidan momy ake kawoma ya Suraj abincin buďa baki , eh dukda haka jeki gida ki huta, ina mama??, taje wajen doctor yanzu.
    Kallonsa ya maida ga Nurr datayi shiru kamar bata ďakin, sannu Nurrina yafaďa yana lumshe idanu, kai ta jinjina masa, ya ce, "babu abinda zakici kafin akawo??, ta girgiza kai alama a'a.
    Su deena sukai musu sallama suka tafi.
   Nurr ta ce, "yaya mi likita ya ce, "yana damuna??, shiru yayi alamar tunani, saiyace malleriya ce take damunki.
   Batace komaiba ta zame jikinta zata kwanta, yari'ke ta yana faďin kwanciyar zakiyi kuma??, ta ce, "nagaji da zamanne ina ganin juwa, to sannu, ya taimaka mata ta kwanta, yana zaune kusada ita hannunsa ri'ke danata likita da mama suka shigo, Nurr tayi saurin zame hanunta.
    Likita yaďan duddubata iya gwargwado, ya Mahmud ya ce, "za'a iya bata abinci Dr?, eh inda tana sha'awar wani abu abata taci ga magunguna sai abata tasha, ALLAH ya 'kara sau'ki.
   Amin mama da ya Mahmud suka faďa, Dr yaja hannun ya mahmud suka fita..................








Luv u oll my fan's
©2017
[09/03 19:49] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》




NA BILKEESA IBRAHEEM 
     {♡bilyn Abdul♡}





45
.........Babu daďewa khairat takawoma Nurr ďan silulu wanda yaji haďin manja da yaji, mama tazuba mata jiki na rawa takar6a tafara ci, tabama ya Mahmud tausayi kwarai matu'ka, sanda aunty bily tana samun ciki ba haka takeyiba itakam, bata amai kuma komai citakeyi.
    Hannu baka hannu 'kwarya takeci, suduka sai kallonta suke fuskokinsu cike da tausayinta, dan danan tacinye ta ce, "mama a'karamin, lamarin yayima mama daďi ta kar6a ta'kara mata kuwa.
    Tana cikinci sai kuma taji amai na juya mata, ta mi'kama mama filet ďin da sauri, tuni tafara yun'kurin amai, da sauri ya Mahmud ya ďauketa yakai bayin dake ďakin, amai tashiga zazzagawa abin tausayi.
   Idanun ya Mahmud sunyi jajur saboda damuwa, mama ma tabiyosu tanama Nurr sannu, khairat kuma takira likita.
   Bayan tagama suka gyara mata jikinta sanan ya Mahmud yasake ďaukkota yadawo da ita saman gadon.
   Likita ya sake ďaura mata ruwa ta koma barci.
   Sardauna zomana, likita yafaďa yana fita.
    A office ďinsa suka zazzauna, ya kalli ya Mahmud da fuskarsa ta nuna matu'kar damuwa, Sardauna saifa ha'kuri kowace mace da irin kwai2n cikinta, shiyyasa mata abin tausayine gamai hankali da hangen nesa.
    Ya mahmud ya gyara zama, wlhy Dr rabon yarinyar nan dacin abinci tun shekaran jiya shiyyasa take 'kara bani tausayi.
   Hakane dama saidai addu'a, yanzuma inaga a tsahirta da bata abincin daga nan har zuwa gobe da yamma mugani, tunda naga kotaci baya zama saima wahala datakesha, zamu cigaba da saka mata ruwan dazai taimaketa kobataci abinciba  insha ALLAHU.
   TO shikenan doctor ALLAH ya taimaka.
  " Amin".
  Ya mahmud yabashi hannu sukayi musabaha sanan yafice.

Mama tace mi likitan yace maka?.
   Mama yace ne aďan tsagaita dabata abincin har zuwa gobe idan ALLAH yakaimu.
    Babu damuwa aisai adaina bata tunda ga ruwanan sun saka mata, dama ďazu yafara yimini bayani, ALLAH yabata lafiya dai.
   Amma dama inason nagaya maka, kada kasake ka sanar da ita tanada ciki sai nan gaba.
   Ya Mahmud ya jinjina kai yana faďin babu damuwa mama...dama ďazu ta tambayeni na ce, "mallariya ce ke damunta.
   Yauwa hakanma yayi dan nasan darun Nurr.
    da'kyar mama tasa ya Mahmud yatafi gida danya sha ruwa, ita kuma daga gida aka kawo mata nata, har zuwa sanan Nurr tanata barci.
    Yashiga gidan da sallama, aunty bily dake shirya kayan buďa baki a tsakkiyar falo ta ďago tana amsawa, ya 'karasa gareta yana faďin sannu da 'kokari bily.
    Yauwa yaya yamai jikin?.
  To da sau'ki za'a ace, dan wlhy taci wanan abun datace ayi mata amma saida ta amayar dashi tas.
   Ayya Nurr ALLAH yabaki lafiya.
   Amin dai.
 To yanzufa?.
    Nabarota tana barci dan doctor ya ce, "kar a'kara bata komai daga nan har zuwa gobe idan ALLAH yakaimu, aďan tsaya agani, yanzudai sun saka mata 'karin ruwa tana barci.
   Wayyo autar mama wlhy tausayi take bani, cikin kwana biyu dukta fige, wlhy kuwa dama ita ba aukiba, bily bari naďan watsa ruwa, to yaya amma dakasha koďan ruwane sanan, babu damuwa bari na watsa ruwan saina zauna gaba ďaya, to afito lafiya.
    
A asibiti kam bayan an gama shan ruwa 'yan uwa suka fara tururuwar zuwa duba Nurr, tsarin family ďin na burgeni, komai nasu atsare, 'ya'ya da iyaye da samari da 'yammata ba'abar kowa abayaba, har manyan iyayen family ďin irinsu dady zuwa suke, kowa yana mata addu'ar fatan samun lafiya.
   Ita tanatama barcinta batasan shigar kowaba balle fitarsa.
    Aunty bilyma bayan kammala shan ruwa tacewa ya Mahmud sukoma asibitin, ya ce, "to dama can nake shirin tafiya, amma bily dakin zauna kin huta.
   Haba yaya babu wani hutu normal nakejin jikina dan haka muje kawai.
   Okey yafaďa yana ďaukar makkullin mota.
   Sanda suka isa asibitin cike yake da dangi, suka shiga mi'kawa juna gaisuwa ana tambayarsu mai jiki.
   Har wajen sha ďaya 'kafafun 'yan uwa basu ďaukeba, zuwa sanan kuma Nurr bata farkaba.
   Mama ta kalli agogo 'karfe 11:48pm, bilkeesu yakamata kutafi gida hakanan kunga dare yayi ga gajiyar azumi.
   Aunty bily ta ce, "to mama amma baku bu'katar komai ko, mama tayi murmushi a'a bilkeesu babu abinda muke bu'kata, ya mahmud yana jinsu amma yayi shiru dan shifa soyake ya kwana anan, amma yana tunani tayanda zai furta ma mama, ta kalleshi tareda faďin kaikuma lafiya, ya girgiza kai babu komai mama dama canayi.......saikuma yayi shiru.
    Ta ce, "ina jinka.
  Ya ďan sosa kai mama dama canayi kozakije gida ki huta, ni saina kwana, da safe idan ALLAH yakaimu saiki dawo.
    A'a mama tafaďa tana girgiza kai, kayi tafiyarka gida nizan kwana, aibai kamata abar bilkeesu ita kaďai agidaba dan haka kutafi saida safe.
   Aunty bily ta ce, "indai dan tanine babu damuwa mama, mama ta ce, "kudai kuyi tafiyarku saida safe, barima natashi nayi isha'i saboda 'yan dubiya banyiba, ta tashi tashige bayi.
   Ya Mahmud ya kalli aunty bily to muje my bily, ta ce, "to, tafaďa tanayin gaba.
   Dawowa yayi ya sumbaci kumatun Nurr har sau biyu  hakan kuma yayi dai2 da fitowar mama, kuma tagansa dan har ido suka haďa, da sauri yafice yana sosa gefen wuya.
   Mama kuma tayi murmushi tana faďin yaran zamani sai a barsu sudai kunyarsu ragaggace.

Haka 'yan uwa sukacigaba da ziyarar Nurr har tsawon kwana uku data ďauka a asibitin, hakama ya Mahmud bai gajiyaba koda yaushe yana can, da rana mama takan koma gida taďan huta da yamma kuma saitazo, to Alhmdllh yau ansallamesu, saidai wani daru mama ta ce, "da Nurr zata tafi gidanta kuma dady yagoyi baya.
   Ran ya Mahmud baisoba amma babu yanda zaiyi tunda iyayensa sun yanke hukuncin hakan, Nurr kam sai murna take jitake kamar tatashi tayita rawa dan daďi, ya Mahmud yana kula da'ita dan haka dasun haďa ido saiya banka mata harara, sunbama mama dariya amma saita sharesu kamar bata lura da abinda sukeyiba.
   Bayan sun gama haďa kaya su ya Mahmud suka rankaya domin yimusu rakkiya har gidan dady.
   To yaudai anan sukasha ruwa, har bayan asham, saida dady ya ce, "suje gida su huta sannan, haka sukayi musu sallama suka tafi.
  Yaukam Nurr ana cikin farinciki za'a kwana agida agadon mama, to tarema suka kwana da mama, dan daddy ya ce, "tarin'ka kwana da ita kar wani abu yataso daddare babu kowa akusa da ita kuma, mama taji daďin haka dan dama hakan takeso, aiko sukayi kwanciyarau da autarta cikin farin ciki.

Washe gari misalin 'karfe tara Nurr tayi wankanta tana ďakin mama zaune tanacin wainar filawan datace amata, mami tayi mata mai daďi, tana zaune tanaďanci kaďan2 saiga ya mahmud, saida yashiga suka gaisa da dady da Mami acanma ya tarar da mama, bayan sun gaisane yanufo đakin mama.
    Yaturo 'kofar da sallama, ta ďago kai tana amsa masa, sannu tace masa tana saka laumar waina, yaji daďi dan yau bai ro'ki sannuba ammasa, ya 'karaso ya zauna kusada ita.
   Ta ce, "ina kwana.
  Lafiya law yafaďa yana murmushi, yaďora dafaďin ya jikinki??.
   Ta ce, "da sau'ki, ina aunty bily?.
   Tana gida ta ce, "na gaidaki kafin anjima tazo, ina amsawa kuwa.
  Ya kalli wainar filawan data dage tanaci, yaukuma abinda akesonci kenan?.
   Ta jinjina kai, akwai daďi wlhy yaya kozakacine??, yayi 'yar dariya a'a Nurri wanan saiku masu kwaďayi dage kici abinki.
   Batace komaiba saidai cin wainarta datakeyi, sukaďanyi shiru nawani lokaci.
   Ya mahmud yakatse shirun da faďin zan tafi office mikike bu'kata??, ta girgiza kai babu abinda nake bu'kata saidai kace aunty bily ta ďakko min kaya, dakuma chocolate ďina acikin wardrobe ďin gefen gado.
   To har kala nawa?, kamar goma haka.
   Maryam goma kuma? wannan lissafi haka kamar wadda zatayita zama anan, kenifa jibi nakeso ki koma tunda kin samu sau'ki.
   Ta turo baki idanunta cike da hawaye, nifa gsky anan zan zauna nafison zama awajen mama, ta'kare maganar da zubo da hawayen idanunta.
   Kinso kawai ki6atama kanki raine babu dalilin dazaisa nabarki anan tunda ga ďakin mijinki can, kinta6a ganin su suhaila sunzo gida sun zauna dan basuda lafiya?, kema dan mama ta matsane kuma babu yanda zanyi, ko deena dakeda ciki tana ďakinta tareda mijinta, dan haka kema nanda kwana uku zaki dawo ya mi'ke afusace yafice.
   Nurr ta rushe da kuka saikace wadda yayma dukan tsiya, babu daďewa mama tashigo ganin Nurr tana kuka saitayi turus Nurr miyafaru kuma kike kuka??.
    Tafaďa kan mama ba ya Mahmud bane ya ce, "wai nanda kwana uku zan koma can gidan, nikuma ALLAH mama nafison zama anan.
   Kinga yi shirunki babu inda zakije kinan, barsa kawai nizan masa magana da kaina, ta ďaga kai tana shashshekar kuka.

Haka akayi ta tafiya yauda gobe sai ALLAH, da dare yayi sai gari ya waye, yau ankai azumi na goma sha biyu, Nurr kuma kwananta takwas agidan dady, babu lafi taji sau'ki sosai dan tana iya yima kanta komai saidai abinda ba'a rasaba, kuma yanzu tanaďan cin abinci; saidai tana amai lokaci2, duk abinda ranta keso shi ake girka mata, aiko tsurfa iri2 saboda cikin nata maisa kwaďayine.
    Kullum dady idan zai fita saiya tanbayeta mitakeson ci, tafaďa masa kuwa, idan zai dawo saiya siyo mata fiyema da abinda takeso, hakama su ya Mustapha suna mata hidima, to bare Saiff abokin tagwaici, kullum sai sayo mata awara dayake tana bala'in so,  ba'a barinta shan 'kan'kara to shine ke sato mata idan yafaki idonsu mama, saikuwa mai gayya mai aiki baban baby ya Mahmud, dukda yana fushi da ita akan ta'ki komawa amma yana mata hidima, kuma kullum saiyazo sau biyu ko uku ya dubata, da safe kafin yatafi aiki zaizo, saikuma idan yataso aiki, dadaddare yakanzo yay mata saida safe.
   Mama tanajin daďin kulawar dayake bama autarta sosai, dan har 'yar fira takanyi dashi, shima hakan yayi masa daďi dan ganin mamar taďan saki jiki dashi a ďan lokaci 'kan'kani.
    Yaukuma akatashi da farincikin haihuwar deena Nurr harda rawar jin daďi, sanda mama zata tafi tadage akan saita bita asibitin, dakyar ta lalla6ata tazauna akan anjima zasu dawo.
    Cikin amincin ALLAH deena ta haihu namiji 'kato mai kama da ya Suraj, (kamar su bani yaron dan na 'kyasa) ALLAH yaraya ba'kon duniya.
    Sakamakon maijego lafiya hakama jariri aka sallamesu, gidanta aka maidata.............



Luv u oll my fan's
©2017
[10/03 10:18] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》







NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡bilyn Abdul♡}



 Assalamu alaikum
       OYOYO BABA BUHARI
Ina taya al'ummar Nageria farincikin dawo baba Buhari garemu, UBANGIJI ALLAH ya'kara masa lafiya da tsawon rai. 
       Mungodema ALLAH daya kunyata ma'kiya.
   Masu izgilin cewa baba Buhari bazai dawo 9ja ba, yau saiku mutu da ba'kincikin hakan, domin kuwa mai komai mai kowa ya 'kaddara masa dawowa 9ja, kuma cikin 'koshin lafiyarsa..
     Lallai yau ranar farincikice agaremu, ranar kuma ba'kinciki ga ma'kiya mahassada, saboda (DODON MUNAFUKAI) yadawo.
     ALLAH ka hana zaman lafiya gaduk wanda ya hanamu, ALLAH ka karya ma'kiyan baba Buhari aduk inda suke, komin girmansu komai girman mulkinsu.
    In sha ALLAH sai Baba Buhari yasauka daga mulki da kansa yabama ďan Arewa wanda zai kasance magajinsa na kwarai, (kuma kwankwaso muke fata, ko Al'Rufa'i dan sune dodannin nabiyu ga makiya arewacin 9ja.
     Bari nabarku haka karna cikaku da surutu((ALLAH ya'karama Buhari lafiya))ameeen(DODON MUNAFUKAI YADAWO).




43

.......Yau cikin amincin ALLAH aka tashi da azumin watan RAMADAN wata mai falala da ni'imomi, (ALLAH kadatar damu acikinsa, ameen).
    Zan iya cemuku har yanzu mai gidan yana fushi da matan nasa, amma da sau'ki tunda yana zama taredasu firace kawai baya saka musu baki, yanakuma cin abincinsu, yakan shiga ďakinsu suma suna zuwa nasa su kwana, koda yake aunty bily ce kawai mai 'ko'karin yin hakan, dama ita Nurr tsoronsama takeji, har yanzu bata kwana tare dashi, to shima ya watsar da al'amarinta, hummm ko ajikin mutuniyar taku, dan ita farincikima takeyi da hakan, har tsalle takeyi ranar dabaya ďakinta dan murna.
   Komai yana tafiya dai2 agidan, saidaifa Nurr daka kalleta kasan tanajin azuminnan, tana kwance atsakar ďakinta tayi ďai2  akasa babu abinda take bu'kata kamar sanyi, jikinta sanye da vest da wandon wanda yatsaya mata iya cinyarta.
    Ya mahmud ya turo 'kafar da sallama ciki2.
   batako motsaba illah dai ta amsa sallamar tasa, kallo ďaya yay mata ya kauda kai saboda kayan dake jikinta, abakin gadon yazauna yana faďin k kuma lfy?.
    Idanu taďago daga kwance tana kallonsa ta ce, "lfy lao, mika gani?, yaďanja numfashi babu yafaďa ata'kaice, saikuma yaďan kalleta k yanzu ba'kya tunanin sanyin kasannan ya cutar dake??, gashi kinyi wata shiga kamar 'karamar yarinya.
   Kallon kanta tayi, minene aibun shigata??, kuma ni wlhy zafi nakeji gashi ina ganin juwa dana mi'ke.
   Juwa kuma??, amma shine bazaki faďaba.
   Ai saina tashi take zuwa idan ina kwance banaji, hummm bakiyi sahur bane??, nayi mana, agabankafa nasha tee, yaďan rausayar dakai hefe tee aiba abinci bane?, kinga kuwa yunwace tasakaki ganin juwar.
   Batace komaiba illa gyara kwanciyarta datayi, shima zamewa yayi yakwanta akan gadon, Nurr tabishi da kallon mamaki miye kuma na kwanciya anan?, tafaďa aranta.
    Shikam baima san tanayiba dan tuni ya lumshe idanu barci yakesonyi, aiko mintuna kaďan barci yay awon gaba dashi.
   Nurr sai kunkuni takeyi wai zai takura mata (nace sarkin mita bansan ranar da ya Mahmud zai fara burgekiba Nurri?).
     Saida aka kira sallar la'asar yatashi yana mi'ka bakinsa cike da addu'ar tashi daga barci, Nurr tana zaune tayi shiru jitake tamkar ta karya azumin dan gsky batada lafiya dauriya kawai takeyi, ya tsura mata idanu danson gano matsalarta, ganin ta kauda kai saiya mi'ke ahankali yatako zuwa gareta, wani ďan tsugunno yayi na gayu agabanta yakai hannu gefen wuyanta saiyaji ďan zafi, Nurri bakida lafiya, bakison faďane kawai, ina ke miki ciwo??.
    Taďan cije le6enta na 'kasa cikin muryar tausayi ta ce, "ALLAH yaya azuminnanne jinake kamar bazan iya kaisaba, mi'kewa yayi tareda ďaukarta cak ya dire saman gadon, yazauna tareda jawo kanta saman cinyarsa, Nurrina faďamin ina ke miki ciwo??,     kaina saikuma juwa bakina kuma ďaci yakeyimin.
    Yaja yaďan lumshe idanunsa ya ce,  "daganan kumafa??, haushine yafara kama Nurr shiba likitaba amma zai isheta da tambaya, ta turo baki gaba ta ce, "shikenan.
   Baice komaiba illa xame kanta dayayi yatashi yashiga bayinta yay alwala yafice, itakuma tarakashi da harara, da kyar tatashi tayi sallar takoma ta kwanta, aunty bily ta le'ko dansu shiga kichin saita samu Nurr akwance, ta 'karaso cikin ďakin tana faďin autar mama yaya dai naganki kwance??.
    Nurr ta tashi zaune da 'kyar ta ce, "ALLAH aunty jinake kamar na karya azuminnan, tofa?, bakida lafiya ne?, a'a nidai ganinake azumine amma ina ganin juwa.
    Ayya sorry kinji, dama nazo danmu shiga kichin amma yanzu kiyi kwanciyarki bari naje 'yan aiki saisu taimaka mini, aunty muje zan iya taimaka miki dawani abun koda daga zaunane, a'a kiyi kwanciyarki, ALLAH zan iya aunty, tayun'kura da kyar ta tashi, aunty bily takama hannunta suka fito zuwa kichin.
   Aiko daga zaune taďan rin'ka taimakawa da aunty bily da aiki, koda ya Mahmud yadawo yashiga ďakin bata nana saiya le'ko kichin ďin, tabashi dariya yanda tawani baje 'kafafu akichin tana aiki, saikace mai tsohon ciki, yayi murmushi tareda faďin raguwa kenan, amma batajishiba, ya ce, "sannunku.
    Aunty bily ce kawai ta amsa sai 'yan aiki, Nurr kam kanta na 'kasa tana gyara kayan marmari, aunty bily ta ce, "harka dawo yaya?, nadawo my bily ya azumin??, taďan murmusa Alhmdllh yaya, to ALLAH yataimaka, bari nakoma masallaci dama nazo duba wananne ya nuna Nurr naga ďazu kamar batada lafiya?.
    Nurr ta turo baki nifa nace maka lafiyata 'kalao.
   To 'yar shagwa6a maida wu'kar idan tayi wari maji, ya fice abinsa, aunty bily sai dariya take musu.
  Da hakadai suka gama shirya abincin da'kyar Nurr tasamu tayi wanka, aiko ana kiran sallah tahau 6an6amar ruwan sanyi har saida ya Mahmud ya kar6e yana mata faďa, "k bakida hankali zakiyita ďurama cikinki ruwa, ta zube saman kujera tana maida Numfashi da 'kyar, masallaci yafice yabarta anan kwance.
     Tana nan kwance suka fito ya Mahmud yadawo daga masallaci, dama afalo 'kasan carpet suka shirya abincin, ya mahmud ya kalli Nurr dake kwance ya ce, "badai bakitashi kinyi sallah ba??, taďan yamutsa fuska ALLAH yaya bazan iya tsayuwaba juwa nake gani.
    Suduka sukai mata sannu, aunty bily ta haďa musu abincin a filet ďaya, ta haďama kowa kunun kus2, sakko kisha kunu ya mahmud yafaďa yana kallon Nurr, ya taimaka mata tasakko ta zauna, aunty bily ta mi'ka mata kofin kunun.
   Ta amsa tafara sha, saidai tana kur6a ta uku taji yafara juya mata, taďan tsaya da sha tana matse ido, ya Mahmud datun ďazu idanunsa na kanta ya ce, "yayadai??, tayi saurin toshe baki danjin amai yataho mata, ya mahmud ya ri'kota yana tambayar lafiya???......kafin yarufe baki tafara zazzaga amai ajikinsa, amai take tamkar zata amayar da 'yan cikinta, gaba ďaya ya mahmud ya ruďe sai sannu yake mata, itama aunty bily duk ta rikice.
   ALLAH sarki Nurrin ya mahmud tabani tausayi, saida tagama tas sanan ya mahmud ya ďauketa gaba ďaya zuwa ďakinta, bayi yawuce da ita kai tsaye, yay mata wanka shima yayi, yanaďota a tawul ya dire saman gado sai fidda numfashi take da 'kyar.
    Aunty bily tashigo bayan tagama gyara inda Nurr tayi amai, sannu Nurr tafaďa tareda zama kusada ita, kai kawai Nurr taďaga mata dan bazata iya maganaba, aunty bily ta ce, "yaya yakamata akira doctor ko?, to bily amma wayoyina suna falo ďakomin sai a kirashi.
  Kafin aunty bily tadawo yasamo riga maiďan kauri yasakama Nurr dan rawar sanyi takeyi, ya kar6i wayar da aunty bily takawo masa, bayan yakira doctor Ashir sun gaisa, sukaima juna barka da shanruwa sanan ya sanar dashi halinda Nurr take ciki.
   Ayya Sardauna karka damu insha ALLAH dana gama shan ruwa zan iso ALLAH yabata lfy.
   Amin ya mahmud yafaďa yana kashe wayar.
   Ya ajiye wayar abakin gado tareda faďin bily bari nasaka kaya, amma yakamata kitashi kije kiyi buďa baki tunda nakulama kamar barci takeyi.
    To aunty bily tafaďa jiki a sanyaye, yaja bargo ya lullu6ama Nurr dan ganin taďan takure jikinta waje ďaya, sanan suka fito shida aunty bily, ya haye samansa itakuma tadawo falon tazauna, babu daďewa ya sakko jikinsa sanye da 'kananun kaya, wando iya gwuywa da 'karamar riga tashan iska, yazauna kusada anty bily dake shan kunu amma damuwarta duk tana kan Nurr.
   Bily kinga yarinyarnan ko! dama nakula batada lafiya tun ďazu amma tayimini gardama.
    Wlhy nima yaya saida na ce, "mata kobatada lafiya amma ta ce, mini lafiyarta 'kalau azumine kawai.
    Hakadai sukacigaba da buďa baki suna jimami.
   Kamar yanda doctor Ashir yay al'kawari haka yazo, ana cikin kiraye2n sallar isha'i ya iso, bayan sun gaisa suka nufi ďakin Nurr da barcin wahala yay gaba dabita.
    Doctor Ashir ya kalli ya Mahmud Sardauna inagafa saika tadata dan zan yimata wasu 'yan tanbayoyi.
    Ya mahmud ya amsa da to, ya zauna abakin gadon tareda ďago kan Nurr zuwa cinyarsa, taďan buďe idanu tana kallonsa, ya ce, "sannu Nurrina  idanu ta lumshe batareda tayi maganaba, Doctor Ashir yay mata sannu, shima kai kawai ta ďaga masa.
   Ya ce, "zaki iya tashine?, taďaga kai alamar eh...., ya Mahmud yatadata ya jinginata da jikinsa, harta 'kara ramewa wuni ďaya, dama gata masha ALLAH akwai 'kiba ba'ace babuba.
   Tanbayoyi doctor yake masa tana amsa masa iya abinda tasani.
    Yaďan murmusa tareda mi'kama ya Muhmud hannu, mutumina sainace ALLAH yasanya alkairifa.
   Ya mahmud yabishi da kallo cikin mamaki, ya ce, "ban ganeba.
   Doctor yaďan kalli Nurr...ya ce, "inbazaka damuba naganka awaje mana.
  Okey ya mahmud yafaďa yana kwantar da Nurr akan filo, falo suka fito suna ri'ke da hannun juna, Doctor Ashir ya ce, "Sardauna Amarya tana ďauke da baby fa.
     Cikin matu'kar farinciki ya Mahmud yake kallonsa, ya ďaga hannu sama yana kwararo addu'oi na godiya ga ALLAH, tareda addu'ar ALLAH ya inganta masa wanan haryazo doron duniya, cikin tausayawa doctor Ashir yake amsa masa da amin.
    Doctor Ashir ya ce, "bai kamata abata maganiba yanzu  amma zamuje dakai musuyo ruwa asaka mata dantaji 'karfin jikinta.
   Babu damuwa ya Mahmud yafaďa cikin farin ciki.
   
Cikin 'yan mintuna suka dawo da ruwa da abinda yadace, aka sakama Nurr, babu daďewa barci yay awon gaba da ita................


Luv u oll my fan's
©2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *