check your best novels here

Monday 20 March 2017

SABON AL'AMAREE 54

《《SABON AL'AMAREE》》







NA BILKEESA IBRAHEEM
    {♡bilyn Abdul♡}




🏻HIQAYA ONLINE WRITER'S🏻
https://mrsbilkisa.blogspot.com 




5⃣4⃣.

........Cikin lokaci 'kankani gidan yacika da dangi, tuni su deena sun iso harda amarya khairat, su aunty suhaila aunty khadija duk suna gidan, an haďu anata barkwanci, jarirai kowa yagani saiya yaba, har zuwa dare mutane suna tururuwar zuwa ganin baby's.
     Sai bayan isha'i suka lafa, suma deena suka tafigida, yanzuma mamace tadawo tayima Nurr wanka dan tunda safe takoma gida, suma jarirai akayi musu, sanan mama tatafi gida bayan ta shirya yaran.
     Gidan shiru saisu kaďai, ya mahmud ma baya nan, aunty bily tana zaune aďakin Nurr ri'ke da jarirai, Nurr kuma tana kwance, aunty bily sai yabama yaran take dafaďin kyawun da ALLAH yabasu, Nurr dai bata tankaba saima ta6e baki datakeyi.
   Aunty bily taďago tana kallon Nurr autar mama wai bakijinane??, humm ina jinki aunty bily banida abin faďane kawai, dariya aunty bily tayi kai kodai kina kishine? yarana sun fiki kyau.
    Hhhhh aunty kenan, aiko makaho yashafa yasan nagaba yayi gaba, wlhy babu abinda yaranki zasu nuna mini.......kafin aunty bily tayi magana ya Mahmud yashigo, ohh ashe kuna nan inacan ina nemanki.
   Yaya ai yanzu babu inda zaka ringa samunmu sai gaban sanyin idaniyar mu, ya zauna yana dariya kumafa hakane my bily, Nurr tazame ta kwanta batareda ta tanka musu ba.
   Yauwa yaya dama gardama akeyi dan ALLAH da yarannan da autar mama wayafi 'kyau??, ya mahmud yakali Nurr yana dariya, ya nuna yaransa da hannu.....Nurr ta ta6e baki to aidama kai koba'a faďaba bakinku ďaya da aunty bily.
   Ya mahmud ya tuntsure da dariya, to bily kinji kin yarda kuwa??, inafa batun yarda itama tasan yarana sunfita 'kyau garama ta hakur kawai, ya mahmud yaďanja hancin ďaya acikinsu wow!!! Dan ALLAH my bily kalli hanci har baka masha ALLAH, Nurr ta ce, "kwadaiji dashi, haka sukaita tsokanarta ita kuma tana kare kanta.
    Washegari mama ta turo mai kula dasu saboda dare, tunda babu dama ya mahmud yaringa kwana dasu tana jego, yanzu kuma lokacin aunty bily ne (to kema ALLAH yabaki naki awanan lokacin auntynmu).

Haka suka cigaba da zaman bakwai, kullum dangi suna tururuwar ganin baby, gidan kullum wuni yake da mutane ana hidima, dahaka suna yazo.
    Yau daren suna daga gidan dady har gidan ya Mahmud suna cikin hidima, dady yayima yara huďuba da kansa, har gida yazo ya gansu yay musu huďuba, shima yayi farinciki da samun jikoki daga yaron kirki ya mahmud, kuma babban ďansa abin alfaharinsa.
    To yaudai suna amasallaci aka raďawa yara sunan dady da momy mamar Nurr, wato Asma'u da Abdul'malik kenan, za'a ringa kiransu waleeda da waleed, to saimuce ALLAH yaraya.
    Da yamma kuma akayi taron suna mai 'kayatarwa da burgewa shagali ake tamkar babu gobe, abin sai wanda yagani, naga masu karatu dayawa awajen taron sunan nan, lallai kunyima ya mahmud da Nurr halacci.
   Masha ALLAH taron suna ya kayatar yanda yakamata, sai makiyi zai kushe, kawo muku yanda shagalin sunan ya kasance 6ata lokacine amma nabama kowa dama ta kiyasta azuciyarta da irin farin cikin daya dace.
    amaryar jego Nurr sai shiga ďunkuna take tana fita itada aunty bily, duk sun 'kyayatar da kwalliyarsu masha ALLAH.
    to hakama angon jego ya Mahmud baki yakasa rufuwa sai tallar makilin yake😁dan farin ciki, jiyake kamar yau an masa rahama, ya haďa kayatacciyar walima shida abokansa da sauran 'yan family ďin, iya maza dai akayi walimar cin abincin dayima jarirai addu'oin fatan Alkairi.
   Iyayen yara su ya Fahad sun taka rawar gani suma saidai muce ALLAH yabar zuminci da 'kaunar juna, ameen.
    To zuwa 'karfe tara na dare kowa yakama gabansa akabar mai jego da aunty bily matar kwarai, saikuma ya mahmud angon jego da 'yan yaransu waleed da waleeda.
   'Yan aiki suka ďan rage abinda ba'a rasaba saboda gidan duk ya hargitse da tarkace.
   Yau Nurr duk agajiye take, hakadai tadage ta gaggasa jikinta dan tursasawar inna magajiya, tsohuwar dake zaune dasu, suma yaran akai musu wankan sanan akayi musu shirin barci.
   Aunty bily na kwantar dasu aďan gadonsu ya mahmud yashigo da sallama, sukai masa sannu ya amsa yana tambayarsu ya gajiyar suna??.
   Aunty bily ta ce, "Alhmdllh, amma Nurr tayi gum da bakinta, ya tsugunna ya sumbaci kumatun yaransa, yana faďin 'yan albarka yagajiyarku??.
   Aunty bily tayi dariya, yanzu gajiyarsu zatabi gado aii, shima dariyar yayi, ya ce, "hakane kam my bily, gashima harsunyi barcinsu hankali kwance, amma mu aii saimunyi jiyyar jikinmu.
   Aunty bily tayi dariya ta ce, "aii saima bawa yakwanta zaiji ajikinsa, Nurr dai tana jinsu tayi shiru, ya Mahmud yami'ke zuwa inda Nurr take tana cin abinci, zama yayi kusada ita, to 'yammata wanan wani salon rowane kuma??.
   Nurr taďan kalleshi batareda tayi maganaba, yaja hancinta kokin zama kurmane??, humm da bakina raďam.
   Maganarce ba'a ra'ayin yi damune??, no kawaidai bajin yin surutu saboda ciwon da kaina keyi, o, sorry hayaniya ce kawai, amma kinsha magani??, a'a tafaďa ata'kaice, okey kigama cin abincin kisha magani insha ALLAH zai daina, yagajiyar taro??, ni bana tareda gajiya, dan taron banawabane, saidai katanbayi aunty bily, itace uwar taro, o, hakanefa na manta sorry ashefa ke 'yar karoro ce.
    Aunty bily dake jinsu ta tuntsure da dariya, ALLAH idan kuna wani abu saikace yara......ya Mahmud ya katseta da faďin to kinsan halin gwamnati dai saida lallashi, Nurr ta kalleshi okey nice gwamnatin kenan??, yayi dariya a'a karkimin sharri nidai ban ambaci sunaba ko my bily??, Nurr ta ce, "aii basai ka ambaci sunaba kowa yay zagi akasuwa yasan da wanda yake........dariya sosai ya mahmud da bily sukeyi.
    Nurr dai tayi musu shiru danta sha'ka, itafa bakomai ya mahmud yakeyi ya burgetaba, abu kaďan zaiyi yabata haushi, tana ďan raga masane saboda kwarjini dayake mata kawai, dakuma darajar shi yayan tane.
    Haka sukaita hira har karfe goma, sanan aunty bily da ya mahmud suka mata saida safe suka fice, suna fita ta kwanta sai barci, ko sanda inna magajiya tashigo tayi barci.
    Aďakin ya Mahmud kuwa ya rungume bilynsa tareda bata 'kyawawan sumba, my bily kema lokaci yayi da za'a buďe mahaifarki ki haifomin yara kema, yau Dr yay mini wannan albishir ďin.
   Ta rungumeshi jiki a sanyaye yayana inajin tsoro wlhy, idan dantanine abarni kawai yaran da Nurr zata haifa mana sun ishemu wlhy, kara rungumeta yayi shima, no my bily kema ina bu'katar kihaifa mini naki 'ya'yan, duk saiki haďa sunzama naki, inason naga natara yara dayawa, dan inaso naga babban family kamar yanda Alhaji mutallaf ya haďamu gamunan cuke kamar karmu 'kare.
    Ta shafa kirjinsa karka damu yayana ALLAH yacika maka burinka.
    " amin my bily".

Kwana biyu da faruwar haka aka kwancema aunty bily mahaifarta.
    Nurr tayi murna sosai da hakan, hakama su mama da 'yan gidansu aunty bily.

Haka sukaci gaba da rainon 'yan2 iyalan baba, koda yaushe suna hannun aunty bily, shan nono kawai yake haďa Nurr dasu, saikuwa barci, itama har cikin ranta tanason yaranta, tana yima aunty bily kawaicine kawai da alkunya, Alhmdllh yara sunyi 6u6ul dasu masha ALLAH kamar abani aro, lol.

AKWAN ATASHI.
    Babu wuya gurin "UBANGIJI", su waleeda sun shiga wata na biyar, Alhmdllh harsun fara koyan zama, ya mahmud yayi farinciki sosai, ya ďaukesu ďai2 yana ďagawa sama sukuma suna 6angale masa baki, harsun fara gane dadynsu, aunty bily tayi dariya, yaya yaran nanfa sun fara ganeka wlhy.
   Ya zauna kusada ita ri'ke da waleeda ai saima nan gaba, da nakula 'kyuya sukaso fara yimin basafa yarda dakowa agidannan saike, mamarsuma idan ta ďaukesu sai kuka, saidai idan Nona zasusha, aunty bily tayi dariyar jin daďi, tabbas tanason yaran har cikin zuciyarta, tanaji tamkar itace ta haifesu, tana fata bazata ta6a ban bantasu da 'ya'yan dazata haifaba har abada, waleed yakama zaninta yami'ke, kai yaya kalla kagani, waleed badai tafiyaba kuma??.
    Dariya sosai ya mahmud yake mata, to momy idan banda abinki mutum yata6a fara tafiya wata biyar??, zumuďinku yayi yawafa??, dariya tayi to kanadai ganin yanda yakama xanina yami'ke??, eh yanaso ki ďaukeshine kawai.
    Duk wanan hidimar da akeyi Nurr tana zaune afalon, ita saima kallonsu takeyi kawai, yanda suka zauna suna koďa yara 'kanana haka?, ta ďauke kallonta daga kansu dan ganin sun haďa ido da ya mahmud, murmushi kawai yayi, Nurr ďinsa tana burgeshi akoda yaushe gsky.
    Haka sukaita abinsu batareda ta saka musu bakiba.

Yau tunda aunty bily ta tashi takejin jikinta babu kwari, yanzuma tana kwance kan gado ta kwantar da waleeda da waleed agenta sunata barcinsu, jitai amai yana taso mata, tun tana iya rikewa harta tashi zuwa bayi da sauri, acan tashiga shekashi babu arziki.
   Kamar daga sama saiga Nurr tashigo, dasauri tadoshi bayin danjin kakarin aman aunty bily, ri'keta tayi tana mata sannu, saida tagama tas sanan ta taimaka mata ta gyara jikinta, takamota suka fito, saman gado ta kwanta; Nurr kuma ta ďauki wayar aunty bily domin kiran ya mahmud.
    Bugu ďaya ya ďauka yana faďin assalamu alaiki my bily, Nurr ta ce, "ba ita bace, da sauri ya ce, "Nurrina yaya dai??, wlhy aunty bily ce taketa amai shine nace katuro mana doctor plzzz.
   Da sauri ya ce, "tofa ganinan zuwa gidan.
  To saikazo tafaďa tana kashe wayar, bayin takoma tagyara inda aunty bily tayi amai..................✍🏻







Luv u oll my fan's
©2017
Share:

1 comment:

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *