check your best novels here

Wednesday 1 March 2017

NAWAFF!!! 51/54

[26/02 15:14] Abba Gana: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page53 & 54

....Su momcy sunyi farincikin ganin yanda ďannasu da matarsa suka daidaita kansu,  ga abinci mairai da lafiya an shirya musu, papa sai saka musu albarka sukeyi, dayi musu fatan alkairi arayuwa.
   Bayan anci an'koshi anďan gaggaisa sukace bari su barsu su huta,, momcy ta ce, "aikuma yakamata kuje ku huta musammam ma ďiyata datasha girki, sannu kinji ďiyar albarka, yasmeen ta amsa da ameen cikin jin kunya, sukai musu sallama sannan suka nufi 6angarensu.
    Suna fita Nawaf ya harareta, "k fancy face ALLAH ya shiryamin ke wlhy.
   Ameen habibina, amma minayi???, yaďan buga kutunta da yatsansa ďaya, shine ko kice tare mukayi girkinnan momcy sai tausayinki takeji bandani.
   Dariya sosai yasmeen takeyi dan yanda yay maganar yabata dariya, cikin dariya ta ce, "o, my man kafara kishi dani kenan??,  okey hakama zakice ko??, karki damu zan rama, yafaďa yana shigewa cikin falon.
   Itama shiga tayi tana dariya, ta faďa saman jikinsa tana cigaba da dariyarta, ya tsura mata fararen idanunsa, idan tana dariya 'kyau take 'karawa, yakanji kamar ya hađiyeta, yasumbaci goshinta my xarah dariya tana miki 'kyau, ALLAH yasa ki haifa mana 'ya'ya masu fara'ar nan taki.
    Yasmeen ta tura kanta cikin 'kirjinsa wai ita kunya, yashafa kanta yana murmushi my xarah aii kunya adon mace, ALLAH yayi miki albarka, tana kwance a'kirjinsa tana sha'kar daddaďan 'kamshinsa ta ce, "ameen yayana.
   Yay dariya tareda ďago kanta suna kallon juna, ya ce, "kinsan mikika tuna mini dakikace yayan nan??, yasmeen ta ce, "A'a, ya murmusa, ranar dana ritsaki aďakin can mana, randa kika 6uya  nafaďo akanki kuma, kai fance face kekam matsoraciya ce wlhy,, ranarfa saidakikayi kamar zaki suma ya 'kare maganar da dariya, da tsokana yayana dan ALLAH kayi ha'kuri wlhy ina fashin sallah....
   Filo yasmeen taďauka tana ďan dukansa da masa kukan shagwa6a, shikuma yana dariya yana karewa da hannu.
    Ta tashi tashige bedroom tana turo baki gaba, shima binta yayi yana dariya, saman gado tafaďa tana kukan shagwa6a, yaja filo yaďan daki bayanta dashi, aisaita mi'ke itama taďauki nata, sukayitama juna duka da filo, shi yana dariya ita tana shagwa6a, duk sunbi sun hargitse gadon, sun baje fililukan wasuma sun faďa 'kasa, yajawota yarungume tsam ajikinsa, sorry teema na nabari bazan sakeba.
    Ta ce, "ai saina faďaka da momcy eh, ya kwanta tareda kwantar da'ita saman 'kirjinsa, kinga 'yar gidana yi ha'kuri bazan 'karaba, yanzu kina faďawa momcy ai cazatayi kikoma ďakinta nikuma aii naga banu kenan ko?.
   Taďago ido tana kallonsa ta ce, "basai kazama gwauroba, tafaďa tana murmushi.
   Ummyimm 1/1 kenan 'yammata kin rama ko?, ta ďaga gira tana dariya, ya ce, "yayi 'kyau, yafaďa yana mirginata, danaga za'a fara soyewa sainayo waje, dannaga wanga gay sai ahankali shi kullum..........um babu ruwana.

Ina nan zaune afalo suka fito, sun sake wanka kowa yaďauki gayu, namaga alamar fita zasuyi, nima sainayo waje, Nawaf ya kulle 'kofar sannan suka nufi 6angarensu momcy, suka sanar musu zasuje gidansu mas'ud ne,, to adawo lafiya momcy tafaďa.
    Saida suka fara gaisheda mami sannan abbansu mas'ud ma yana gida, shima suka gaisheshi yay musu nasiha da wa'azi, sun ďan daďe awajen kafin su nufi 6angaren mas'ud.
    Duk suna falo zaune ameena tana 'kasa ta baje 'kafafu dan cikinta yayi girma ankusa juyo mana baby, mas'ud kuma yana zaune kusada ita yana matsa mata 'kafafunta dasukaďanyi fushi,, cikin tsokana yasmeen tashigo tana faďin mai ciki uhum ganinan tafe, Nawaf da mas'ud suka tuntutsure da dariya yayinda ameena take hararar yasmeen,, habawa yarinya kema aigashinan ajikinki kwana nawane maye yaci amarya.
    Yasmeen tazauna tana faďin sannu mayya, inba mayyaba wazai hango kanada ciki??, Ameena ta ce, "ai alamomi sun fallasaki, yasmeen tabi jikinta da kallo tana ta6e baki ke 'yar fata 'kyayi ki barni, mudai kiyi maza ki juyo mana babynmu ko ya ya habibina?, Nawaf ya ce, "gsky ki fancy face.
     Mas'ud da Ameena suka kalli juna suna murmushi, harsuna haďa baki wajen faďin tofa haka akayi??, Nawaf ya ce, "haka akayi mi??, A'a basai mun faďaba Alhaji abar kaza cikin gashinta.
   Nawaf yay dariya kajidashi dai magulmaci, A'a bro's aikaine babban magulmacin kaida kace..........koda yakedai bari nayi shiru kawai,, A'a kafaďa karta kasheka mana,, A'a arufe rufau kawai.
    Sukai dariya gaba ďaya sannan suka gaisa da tambayar Ameena ya jiki??, ta ce, "Alhmdllh, ai nakusa barwa matarka, Nawaf yakalli yasmeen to ALLAH yakaimu lokacin, sukace ameen.
   Ameena ta ce, "dan ALLAH yasmeen ki ďakko muku abinsha mana,, yasmeen ta ce, "oni kazo ba'kunta asaka aiki, mas'ud ya ce, "ba babyn ku bane yaja mana, duk yabi yahanamu mu shana ko my honey??, Ameena ta ce, "wlhy kuwa gsky ka.
    Nawaf yay dariya toku juyo mana abinmu mana, basaikuje kuyita shanawarkuba, aii muna gab kuwa mas'ud yafaďa yana kunna tv.
    Yasmeen tadawo da abinsha, nan suka zauna sunata hira da tsokanar juna, daga baya ameena taja yasmeen ďaki, Nawaf ya ce, "o, mata kun iya gulma, kudai baza'a ta6a zama daku waje ďayaba.
   Yasmeen tajuyo tayi masa gwalo, ya ce, "niko?, tashige tana faďin eh,, okey zan kamaki aii yarinya, zaki banbantamin.
   Mas'ud yay dariya wai mutumina yaushe aka koma haka?, Nawaf ya ce, "kamar yaya??, harararsa mas'ud yayi kaifa ka iya waskewa wlhy, Nawaf yay dariya yana shafa kai, yashiga bama mas'ud labari, sunayi suna dariya da tafawa.
    Aďakima aminai biyu sun 'kulle sunata hira akan abinda yashafesu, yasmeen ta ce, "yauwa ameena yamaganar kayan dakikai min kwanaki??.
    Ameena ta tuntsure da dariya 'yammata keda kikace bazaki nemaba??, yasmeen ta ce, "hum kibari kawai fitinar Nawaf dole saina shirya mata, plz kidaina mini dariya mana, ameena ta tsagaita da dariya, to nabari sistona yanzu abinda za'ayi littafin zan baki kawai kiringa haďawa da kanki, danni nafi gane nahaďa abu dakaina, bawai da ankawo nahau shaba alhalin bansan daga inda yakeba.
   Hakane amma suna cutarwane??, kai, eh mana, akwai masu cutarwa, wasufa bakasan inda aka haďasuba, kinga kuwa ai za'a iya samun matsala.
   Gskyar ki, to amma aina zan samu kayan haďin idan kin bani littafin?, babu damuwa yawanci kayan itatuwane, barema ALLAH yabaki miji mayen kayan marmari, zakiringa samu koda yaushe, sukansu kayan marmarin idan kinasha komai zai zama dai2 kuma zam2, okey to shikenan kibama hanan takawomin littafin dan yanzu babu damar nace zan tafi dashi.
    Ameena tayi dariya kina tsoron boss yagani kenan???, hhhh babu wani tsoro ina kare martabatane kawai, suka tafa suna dariya.
   Sai bayan isha'i suka koma gidansu, a 6angarensu momcy suka yada zango, saida akasha hira sannan suka wuce 6angarensu, Nawaf yafaďa saman gado yana faďin wash ALLAH na nagaji my xarah.
   Yasmeen ta ce, "to yakakeso ayine??, ya ce, "amin wanka dan ALLAH yafaďa cikin shagwa6a, yasmeen ta zauna kusadashi tajawo kansa taďora saman cinyarta, ta ce, "kafa girma habibina amma kake shagwa6a,, ya kamo hannunta yasumbata yana murmushi, fancy face gara nayi kafin yara su zo su kwace mini fadata.
   Yasmeen ta du'ko ta sumbaci goshinsa, suka tsurama juna idanu cikin murya mai cikeda so da 'kauna ta ce, "bazasu kwace maka fadaba, dan kaina fara sani kafinsu,, yarungumeta kansa yacusa jikin cikinta, to shikenan fancy face ALLAH yakawo masu albarka, ina addu'ar kafin mu tafi Spain kin kamu.
    Yasmeen ta zaro ido waje, kai habibina nifa bazan bikaba ina nan tareda su momcy.
   da sauri yatashi zaune yana kallonta, yakamo hannunta, kina nufin zaki barni natafi ni kaďai, xarah??, danayi ha'kurin rashinki akusa dani amma fa yanzu bazan iyaba wlhy, ina kikeson naringa kai matsalolina, ko kinaso mijinki yafara aikata abinda baiyiba yana saurayi??, plz & plz karki bari su momcy suji wannan maganar, wlhy zasu goya miki bayane.
   Ya jawota jikinsa cikin taushin murya yafirta ina sonki dayawa fateema, amma ke naga kamar har yanzu baki amintaba, kokuwa ba'kya sona.............da sauri yasmeen ta rufe masa baki, plzzzzz karka faďa wlhy nima inasonka fiyema da yanda kake sona, nima bazan iya rayuwa babu kaiba kaji na rantse maka, da sauri ya rungumeta tsam suna fidda numfashi ahankali, saida zuciyoyinsu sukai sanyi sannan suka ďago suna kallon juna suna murmushi, tafara cire masa ma6allin rigarsa tana faďin tashi muje muyi wankan nafara jin barci.
    Tare sukayi wankan sukai shirin barci sai gado, nima na tattaro inawa2 nayo gida.

Haka rayuwa taci gaba da gudu da sauri, komai yana tafiya yanda akeso, su Nawaf suna shan soyayya, koda yaushe suna manne da juna idonsu yarufe gaban kowa soyewa sukeyi, suna 'kyautatawa juna, kowa burinsa yafarantawa ďan uwansa rai.
    Yasmeen takan shirya musu girki mai daďi da gamsarwa, suci susha abinsu, tana ma mijinta biyayya duk abinda ya bu'kata tana masa cikin hanzari babu nuna fushi bare ta ce, "tagaji,, aduk lokacin dayazo mata da bu'katarsa takanyi 'ko'karin taimaka masa dan yasamu nutsuwa, kullum sukan kasance cikin farinciki da 'kaunar juna.
   Shima Nawaf baya ba'kin cikin 'kyautata mata da 'karfinsa da lokacinsa aljihunsa dakuma farincikinsa,, nakula aurene mai cike da farinciki da 'kaunar juna.
     A yaune kuma Ameena ta haihu ďiyarta mace, su yasmeen ana cikin farinciki, kamar su suka haihu, kullum tana gidan suna kar6ar barka sune amarori 'kirjin biki.
    Kullum a can take wuni, sai dare take dawowa gida, yau kam agajiye tadawo gida Nawaf yana kichin yana haďa shayi, tashigo da sallama ta faďa saman kujera tana kiran wash ALLAH na, Nawaf yafito daga kichin hannunsa ďauke da kofin shayi ya ce, oyoyo my xarah kin dawo??, taďago ido agajiye tana kallonsa ta ce, "eh ammafa yau nagaji dayawa, ya'karaso ya zauna kusada ita, kofin shayin ya ajiye saman tabir ďin gabansu, ya rungumota zuwa jikinsa ayya sorry my dear karki damu ai hidimar babyn muce, ta shafa kirjinsa tana murmushi hakane my handsome.
   Shima yay murmushi, nima kwana biyunnan duk an barni cikin kaďaici, ga bu'katun sunyi mini yawa, kullum aka dawo sai ace angaji, yasmeen tayi dariya haba habibi yanzufa kagama faďar cewa hidimar babyn muce.
    Ya marairaice murya hakane fancy face, amma itama babynmu tana bu'katar sabon 'kani, atausaya mini plzzzzzz, yasmeen ta murmusa tana masa gwalo, ya ce, "niko??.
   Ta ce, "eh tareda 'kokarin tashi, yay saurin matseta ajikinsa yana bata 'kayatattun sumba ako ina na sassan jikinta...................




Kuyi hakuri yanzu ina typing kaďan, inada uzurine.
  ;luv u oll  kuna 'karamin karfin guywa ngd sosai.







©2017


bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
          luv u oll my fan's
[26/02 15:14] Abba Gana: ☆☆☆☆☆☆☆
 NAWAFF 
☆☆☆☆☆☆☆






NA BILKISA IBRAHIM



Page51 & 52

.......Daga sumba aka koma soyayya, na ce, "wannan lamari bana kallo bane, bari nayi nanan.
   Saida komai yay dai2 nadawo falon, yasmeen sai 6oye fuska take wai ita kunya, yayinda Nawaf yake ri'ke da hannunta yana mata dariya, cikin shagwa6a ta ce, "ALLAH idan baka bariba zan haďaka da momcy, yarufe baki yana faďin nabari, "k yanzu kina faďama momcy aizata 'kara baki mafakane, sorry na daina,, yasmeen tayi murmushi mafaka kuma kamar wata 'yar gudun hijira??.
    Nawaf ya ďora kansa saman cinyarta yana dariya, eh mana gudun hijira kikayi harna kwana shidda,, amma ALLAH ya koromini ke.
   Hhhh malam aii yanzu zan koma inda nafito, tab zance kenan, ai yarinya kinzo kenan, keda ďakin momcy saidai gaisuwa, ta waro ido habadai daga zuwa tambayar anguwa.
   Eh mana itama momcy zataji daďin hakan, dama tayi miki wayone ta turoki kawai.
   Yasmeen tayi murmushi, toya maganar tafiyar zanje?, saida ya sumbaci tafin hannunta sannan ya ce, "kibarsu suyi tafiyarsu mukuma musha soyayyarmu ko??, taďan zum6uro baki gaba kai dan ALLAH kabarni ALLAH inason zuwa fa.
   Yatashi zaune, kinga kibarsu su tafi, mukuma dasun dawo saimu lula saudia muyo hutunmu acan ko babyna, yafaďa yana jan hancinta.
   Ta ce, "ALLAH kaima ka iya wayo, babu wani wayo fancy face gasky nafaďa, kinga tashi muje muyu wanka.
   Tare sukayi wankan, sannan sukayi sallar isha'i, bayan sun idar ta ce, "bari natafi saida safe, da sauri ya ri'keta "k 'yammata babufa inda zaki, ina bu'katar jin ďumin matata, da lallausar fatarta haďeda sha'kar kamshin jikinta mai daďi, ta ce, "ALLAH inajin kunyar momcy, ďaukarta yayi cak ya ďora kan gado, babu wata kunya xarah na, zoki bama mijinki ďumin jikinki, babu yanda zatayi dole ta ha'kura ta kwana anan, yaudai Nawaf ya zazzage mata sirrin zuciyarsa, harsukayi barci bai daina fidda sirrikan sonta dake kwance a zuciyarsaba, dan haka barci yay gaba dasu cikin farin ciki, irin wanda basu ta6a gamo dashiba.lol

Da asuba ma suna idar da sallah suka koma gado, Nawaf yafara al'amura, cikin shagwa6a yasmeen ta ce, "plz kabarmu muyi barci, ya hura mata iska akunne, babu wani barci 'yammata, ta ce, "to mikakeso ayine?, ya ce, "kinfini sani, taďan lankwashe murya ALLAH saboda barci kaina har wani ďan ciwo yake, da sauri ya rungumeta ayya sorry fancy face to muyi barci ki huta, ALLAH yay miki albarka kinji, yasmeen tayi murmushi tana faďin ameen, bayanta yayta shafawa da hura mata iska a kunnenta, babu daďewa barci yay gaba da ita, Nawaf ya tsura ma face nata idanu, komai na yasmeen mai 'kyaune, dukda yafita fari amma tanada haske mai 'kayatarwa, yasa ďan yatsansa yana zagayawa akan la66anta masu kalar pink, ya ALLAH kabarni da abar 'kyaunata ya firta ahankali, tareda rungumeta tsam shima barcin yay gaba dashi.
   Basu farkaba saida momcy ta kira wayar Nawaf, kusan atare suka tashi, jallabiya kawai yasaka, itakuma tasaka hijjab suka fito, a harabar gidan suka iskesu tsaytsaye, Nawaf ya ce, "momcy kuce harkun shiryama??.
    Momcy ta ce, "ehmana gashima zamu wuce tunda ka hana matarka zuwa, yaďan sosa gefen wuyansa yana faďin ba haka bane momcy muma zamuje insha ALLAHU koba yauba.
   Momcy tayi murmushi to shikenan, mu bari muyi harama, sai jibi zamu dawo tareda papanku tunda yana can, gasu talatunan, lokaci2 yasmeen kiringa le'kowa kiga halin dasuke ciki kinji ko??, yasmeen ta ce, "to momy, ALLAH yatsare mana ku, yadawo mana daku lafiya.
   Amin momcy tafaďa tana shiga mota, su Anwar suka ďaga musu hannu, suma suna đaga musu harsuka fice daga get ďin.
   Nawaf yajuyo wajen yasmeen yana murmushi, fancy face kozaki bisune?, yasmeen ta harareshi kafaďi haka tunda sun tafi, cak yaďauketa suka nufi wajensu yana mata dariya, to bari na goge laifina, itama dariyar takeyi ta ce, "saidai ka goyani, ya direta 'kasa yana faďin wannan mai sau'kine, ya tsugunna ta haye, yami'ke yana dariya, amma kisani wannan goyon yanada tukuycifa.
    Ta ďora kanta gefen kafaďarsa, kai haba wane tukuyci kuma?, karka manta kayine dan lallashifa.
   Nawaf yay dariya yana tura 'kofar falonsu da 'kafa hakane kuma my xarah, saman gado ya sauketa yana wani faďin wash, kai ammafa kincika nauyi, a ido gaki siririya amma fa sai nauyin tsiya.
   Yasmeen ta zuro 'kafafunta tana dariya, haba my man abumma harda tsiya kuma, yari'ko hannunta babu wata tsiya sai gsky, ina zuwa haka??, tayi far da idanu zanje kichin nemawa habibina abinci ko.
   Ya kanne mata ido ďaya tareda mata, ta sauka tana dariya.
    Tare suka haďa break ďin suka gyara ďakinsu, su talatu suka gyara musu sauran guraren tsaf, dan danan gidan ya gauraye da 'kamshin turare gana daddaďan abincin dasuka girka,, yaukam babu kunya tare sukai wanka kowa yay ma ďan uwansa, suka fito kowa ya shirya, cikin 'kananun kaya,, Nawaf yabama yasmeen wasu fitunanun kaya cikin tsarabar dayay mata, daga Spain, ta ce, "woow!! Ammafa sun haďu my man, ya ce, "da gsk??, ta kanne masa ido ďaya tana faďin wlhy kuwa, ya ce, "ashe na iya za6e?, ta ce, "sosaima, aina kasiyo kayannan??, A Spain mana lokacin dakukaje jinyata, ta ce, "humm kace lokacin anajin haushina, amma harda tsaraba.
    Yay dariya kema aii sannan kinamin tashen rashin kunya, saidai ina ma'kale da sonki ko a sannan, yaja hannunta zomuje muyi break inajin yunwa.
   Ta ce, "wai yaushe kafara sonane??.
   Karki damu idan mungama zan baki labari.
    Suna cin abinci yana mata santi, itako tana 'kyal'kyata masa dariya da saka masa waugi, ya ce, "wai miki ďaukeni?, kina zaton santi nake??, cikin dariya ta ce, "faďi da wai ka 'kara da wayyo, kaima kasan santi kakeyi Alhaji, yay dariya, to idanma santin nakeyi toga akan abu biyu nakeyi.
   Yasmeen ta tsaya da dariyar datakeyi, to dami2 kenan??.
   Ya nunata fancy face ďina mana da abincin fancy face, tayi dariya tana wani far da idanu to nagode abin 'kaunata.
   Ya lumshe idanu yana faďin i luv u fancy face,, ta ce, "luv u too my habibi.
   Hakadai sukaci abincin yana bata tana bashi harsuka 'koshi, suka dawo falo suka baje.
    Yasmeen ta ce, "to faďa mini yaushe ka fara sona, saida ya kwanto da kansa saman cinyarta suna kallon idanun juna, tasa hannu cikin yalwatacciyar sumarsa tana masa susa, yafara lumshe idanu yana gyara kwanciya, cikin murya mai cike da shau'kin so ya ce, "idan na ce, "miki tun randa muka fara haďuwa harna jefa miki kwalin yogot đin holladia zakisha mamaki.
   Ta ce, haba dai ban yardaba, ya murmusa, wato sanda muka iso cikin gosulo ďin saina fara yima mas'ud Masifa akan miyasa ya ce, "mu biyo wannan titin bayan yasan yana haďa gosulo.
   Shuru yay min saboda yana amsa waya, haushin hakan yasa na ďauki yogot ďin inasha, ďagowar dazanyi sainayi tozali da 'kya'ky'kyawar yarinya tsaye tana hange2, wani shokin ne yaja kwakwalwata, kinyi bala'in tafiya da imanina saidai bansan yanda zan nuna miki hakanba banason kuma na faďama mas'ud nayi tsuntuwa, dan munsha tsokanar juna konace gardama akan soyayya shirmece kawai,, yakan cemini baka gamu da wadda tayi maka bane, nikuma na ce, "ai kona gamu bazanyiba, haka kullum muke akan gardama ďaya, tokuma kwatsam ranar saigaki.
   Nasan idan har mukabar wajen bammiki maganaba ba lallai bazamusake haďuwa ba, tunda garin kano ba 'karamin gari bane, ina cikin sa'ka da kwancewa saidabara ta faďo mini, wani abokina yata6a faďamin daga faďa suka fara da matarsa (prince salman mijin salma kenan, a novel ďin ayusher muh'd NIDA PRINCE), to dana tuna haka sainace nima bari nagwada sa'ata, kawai sai kwakwalwata ta kawo mini wuta akan na jefeki da kwalin yogot ďin nasan dole ki tanka,, bayan na jefeki sai abin yay matu'kar bani dariya yanda kika tsorata, to Kekuma saikikaji haushi harkika cemini w..............dasauri yasmeen ta rufe bakinsa dan ALLAH karka maimaita my man plzzzzzzzzzz!!.
    Yay murmushi to shikenan nabari, to bayan munyi faďa agurin mas'ud yarabamu kowa yatafi, damukazo gida saina matsawa mas'ud akan yatayani nemanki amma saiya'ki, nashiga ruďani alokacin dan banaso na rasaki gsky, ana cikin haka sai muka haďu abinkin safwan ranar naji daďi mara musali, amma bai hanani takalarki faďaba, harma na ce, "marin dakikaimin zai zama fansar budurcinki,, hummm nafaďane kawai danki tsorata, dan duk kamilar mace bata burin arabata da budurcinta bata hanyar aureba.
   To tundaga ranar ban sake jin labarinkiba, sabodake washe gari naje wajen walimar amma ke bakijeba,, yasmeen ta ce, "tsorone ya hanani, Nawaf yay dariya tareda jan hancinta ya ce, "matsoraciya kenan.
    To daga nanfa narasa hanyar dazan ganki,, sai ina gab da komawa Spain naganki keda ameena awani wajen hutawa, na ma'kale inda bazaku ganniba nashiga bin bayanku ayayin dazaku tafi gida, harsaida naga inda balarabe ya tsaya da mota, abin yabani mamaki danaga gidanku dakuma motar da aka ajiyeki, sai kawai najuya nakoma.
   Kwana biyu da faruwar haka nasa aka yimini bincike akanki, amma mas'ud bai saniba, babu abinda aka 6oyemin har tsakaninku dasu faisal, akwai abokina yana karatu a school ďin su faisal a america, shinasa yaymin bincike akan faisal.
    Anan nagane cewa ďan iskane manemin mata, harma ya lalata 'kanwar wani abokinsa dasuke zaune acan tare hisham kenan, amma baisaniba.
   Nine nasaka abokina ya gayama hisham, muka kuma kulla yazo Najeria domin yaga yarinyar da faisal zai aura yagano mana idan  tana sonsa, dama suna gab da kammala karatunsu dan haka suna gamawa sukazo, idan baki mantaba aranda sukazo saida suka kalli wani wasanmu agidan, sunkuma rin'ka miki surutu marassa ma'an, hhhh duk sunayine dasu harbo jirginki.
   To bayan sunzo sun faďa mana sai muka shirya yanda zamu rabaku, abinda muka turama faisal awaya baikai yazargekiba amma dayake jakine kuma badan ALLAH yake sonkiba saiya hau yazauna, har an ďaura aurenku yaje yasakeki.
    Saidai kinsan wani abin mamaki??.
   Yasmeen ta girgiza kai.
   Nawaf yay dariya, wlhy bansan papa yaje ďaurin aurenkiba bammasan angayyaceshiba, papa mutumne mai tausayi da kishin ďan uwansa muslmi, hankalinsane yatashi yayinda faisal ya ce, "yasakeki abba ya yanke jiki yafaďi, shine kawai ya ce aďaura auren da ďansa.
    Bayan yadawo gida yakirani ya zayyana mini, hankalina yatashi danni zuciyata ke takeso, nagama shan wahalar rabaki da faisal da nufin bayan kamar wata ďaya hankalinki ya kwanta sainaje na bayyana miki ina sonki, amma ga papa yayomini wata 6aran6arama, hankalina yatashi sosai nakuma shiga ruďani, harna kasa ta6uka komai awasan danazo bugawa kasata.
    Kinsan abinda yasani farinciki?, yasmeen tagirgiza kai,, ya kaďakai, randa mas'ud yakawoni gidanku ya ce, "nanne gidansu matata, nashiga ruďani da farinciki da zumuďin san ganin matar tawa, dan atarihinki da aka bani yanuna ku biyu aka haifa agidan,, hummm wayyo daďi abin farinciki wanda bazan ta6a mantawa dashiba shine lokacin danayi tozali dake naji kamar natashi nayita rawa amma saina dake dan banason kugane keda mas'ud.
   Yasmeen ta ri'ke baki "o, kai habibina amma shine harda mini mugunta aranar,, dama duk kaine kashirya waďannan abubuwan, amma danazo gidanka kake nuna kai bama kasona, tafaďa tana turo baki gaba.
   Yatashi zaune yana 'yar dariya, sorry xarah na, kemace dai kika kasa fahimtata, yakamata ki gane wani lokacin nakan kasa control ďin kaina, harnakan fito da sirrin zuyata fili.
   Yasmeen tayi dariya aini ina ďaukar hakan kawai amatsayi wani abu daban.
    Nawaf yay murmushi wlhy sonkine kawai yake ďawainiya dani, aduk lokacin danayimiki abu nakan dawo inajin tausayinki, to amma babu yanda zanyi, gashi kekuma bakinki baya mutuwa, kin iya tsiwa, yafaďa yana ďan buga bakin da yatsunsa biyu.
    Yasmeen ta rungumeshi tana faďin ammafa ka iya basaja bata wasaba, shima rungumeta yayi tsam yana sassanyar dariya a kunnenta to a yafemin bazan sakeba.
   Taďago tana kallonsa tana murmushi ta ce, "i luv u habibina, yasake rungumeta shima ya ce, "luv u too my xarah.


Haka suka cinye kwana biyunnan cikin soyayya da faranta ran juna, sun manta da kowa da komai, idonsu yarufe sunata zuba soyayya, dabama juna kulawa, Nawaf baya zuwa ko'ina, sallah ce kawai take fiddashi, abin sai wanda yagani, a yau kuma su momcy suka dawo..........







©2017








bilyn Abdul
    Mrs Abdus'salam
        luv u oll my fan's
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *