check your best novels here

Saturday 11 March 2017

SABON AL'AMAREE 34/36

[02/03 13:29] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》








®BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡bilyn Abdul♡}



34

......Mutuwar tsaye ya Mahmud yayi dan Nurr ta tafi da imaninsa, Abdul ya kwace hannunsa yatafi da gudu yafaďa kan Nurr, a tsorace ta buďe ido saitaga Abdul, tashi tayi zaune tana dariya tareda cire iya fis daga kunnenta, ta ďauki Abdul tana faďin dadyna yaushe kukazo?? Ya ce, "yanju munzo da daddy yafaďa tareda nuna ya mahmud dake tsaye da rauda a kafaďarsa tamkar gunki.
    Yay sourin dai2ta nutsuwarsa, palon ya 'karaso, Nurr ta ce, "Rauda zonan.
   Harara ya Mahmud yasakar mata "k sai yaushe zaki iya sannu da zuwa??, Nurr ta kwa6e fuska tana kauda kai ta ce, "to dannu da zuwa, banaso yafaďa yana zama, ahankali ta ce, "karkaso ďin mana masifaffafe, itafa tun randa yay mata abunnan haushinsa takeji.
    Aunty bily tafito tana masa sannu da zuwa, ya amsa yana murmushi, ruwa taje takawo masa yasha ta ce, "wankafa??, yaďan marairaice fuska tareda maida zancensa zuwa turanci dankarsu Abdul suji, ya ce, saidai aminwankannan dan nagaji my bily, kuma da matsala na dawo.
     Tasan inda yadosa danhaka tayi murmushi, yayinda Nurr tai saurin cewa ""innalillahi wa'inna'ilaihirraji'un"", gaba ďaya suka juyo suna kallonta azatonsu wani abune yasameta, sai sukaji ta ce, "ALLAH ya shirya 'kato dakai za'a maka wanka, ido aunty bily tazaro danjin furucin Nurr, shikam gogan naku yadasa mata idanu cike da haushi, tunaninma abinda zaimata yakeyi, mi'kewa yati azatonsu wajenta zaizo saisukaga ya haye samansa.
    Anty bily ta ce, "ALLAH yashiryeki Nurr, itama ta takema ya Mahmud baya taje ta lallashi abinta.
            Nurr ta ta6e baki ALLAH ya shiryeku dai, dan kune kuke bu'katar addu'ar shiriya baniba, ta kama hannun su Abdul suka tafi ďakinta.
   Aunty bily ta 'karasa ga ya Mahmud dake zaune abakin gado yacika yay fam da haushin Nurr, tazauna tana gaya masa maganganu masu daďi da kwantar da hankali, haba my handsome bai kamata maganganun Nurr suringa 6ata maka raiba, karka manta Nurr yarinya ce, har yanzu tana bu'katar uzuri daga gareka, yaďan lumshe ido ya buďe ya ce, "haba bily har sai yaushe Nurr zata fita daga 'kuruciyar nan ne??, kina ganin duk maganar data fito daga bakin yarinyarnan kwa6amini takeyi saikace sa'anta, inda aure nayi dawuri da na haifi kamarta wlhy, amma kibari kwanan zanyi maganinta, zanyi mata abinda zata shiga hankalinta, ahankali take shafa bayansa tareda yimasa salo maicike da ďaukar hankali, to dama yana bu'kata sai kawai yabada kai sukakashe juna da soyayya mai nagarta, (nace soyayya ruwan zuma, gwauraye yakamata ayi aure, irinsu....... baridai na rufa miki Asiri amma wataran saina faďa)

   Itako Nurr tana đaki suna shan wasa dasu Abdul, koda aunty bily tazo kiranta suci abinci saitace ta 'koshi, babu lallashi dabatayi mataba amma ta ce, "itafa ta 'koshi, dole ta 'kyaleta takamo hannun su Abdul suka fito.
    Aunty bily ta ce, "yaya koda kanka zakaje nayi2 Nurr tazo taci abinci amma ta'ki waita 'koshi, yaďan ta6e baki wlhy babu inda zanje danba cikina zata kaiba, ki barta kawai dolene kwanannan nakoyama yarinyar nan hankali, a'a yaya kayi ha'kuri a hankali yakamata mubita, to kawai yace mata yacigaba dacin abincinsa.
    Bayan sun gama cin abincin suka dawo falo suna hira, su Abdul kuma suna wasansu, saida zashi sallar la'asar sanan yamaidasu Abdul gida, harsanan Nurr bata fitoba tana ďaki abinta tana karatun Novel.

Sanda yadawo aunty bily tana ďaki, yaďan le'ka yana tambayarta har yanzu bata fito taci abincinba??, anty bily taďaga masa kai batareda tayi maganaba, shima baice komaiba yafito, ďakin Nurr yanufa kai tsaye.
       Ya tura 'kofar yashiga, hakan yayi dai2 da fitowarta daga wanka, tafito tana 'yar wa'karta, yasakama 'kofar key ahankaili yazare key ďin dan bata kula dashiba, ta 'karaso tsakkiyar ďakin takama tawulďin jikinta zata yaye saitayi arba dashi atsaye, 'kara ta kwallah, da sauri ya'karasa inda take yasa lallausan hannunsa ya toshe mata baki tareda daka mata tsawa, da 'karfi ta kwace dagudu tanufi dirowa danufin tashige ciki, taku ďaya yayi ya dam'kota, yajuyo da ita suna fuskantar juna, jikinta sairawa yakeyi  yay mugun haďe fuska, cikin muryarsa mai tsoratar da marajin magana.
   ya ce, "wai yaushe muka fara 'yar wasa dakene??.
     ni abokin wasankine??.
 yaushe raini yashi tsakaninmu??.
     tuni fuskarta tayi kaca2 da hawaye ta ce, "dan ALLAH kayi ha'kuri yaya wlhy na rantse maka bazan sakeba.
      Tsawa yadaka mata kimin shiru nace, wanan bakin yaymin tsitt!!!, gum ta kulle bakinta tamkar ruwa yacinyeta saidai rawar jikinta yana 'karuwa, yabi guntun tawul ďin jikinta da kallo har zuwa santala2n cin yoyinta, sakin hannunta yayi dake dam'ke anasa, ya dafe hannayensa biyu ajikin dirowar, ya matsa daf da ita har sunajin fitar numfashin juna, cikin tsoro Nurr take kallonsa tana 'kara manne jikinta ajikin dirowar, ya 'kara haďe fuska tamkar bai ta6a dariyaba, idanunsa ya zazzare mata ya ce, "rufe idonki, yanda yafaďa cikin tsawa sai jikinta ya'kara tsananta rawa, ta runtse idanunta gam tana hawaye.
      Bin fuskarta yayi da wani shi'umin kallo yana murmushi, ahankali yakai bakinsa kan nata ya manne, zabura Nurr tayi saboda tsorata bata ta6a zaton abinda zaiyimata kenanba, hannu yasa ya tallafota sosai tareda zame tawul ďin jikinta, wata zazzafar sumba yake mata tamusamman tareda kai hannunsa ko ina a sassan jiknta, tuni Nurr tafara fitsari atsaye, sai mutsu2n kwacewa take amma ya'ki bata damar hakan, saima 'kara matseta dayayi ajikinsa [nace tabďijan akwai matsala ya Mahmud kashiga hankalinka fa, karkai mana aika akai].
     Tun tana iya kaimasa duka abaya da mintsini harta gaza, shiko ko gezau baiyiba hasalima 'kara yimata wasu abubuwan yakeyi waďanda sukafi 'karfin tunaninta, tuni kwakwalwarta ta fara gaza aiki, saida yayi mai isarsa kamar zai cinyeta ďanya sanan yacikata yana maida numfashi asar'ke (nace wanga mutum akwai........hum baridai nayi shiru).

Da gudu ta haye gado tana kuka ta janye zanin gadon duka ta 'kudundunr jikinta, shikam saman kujerar dake ďakin yazauna jagwaf kamar wanda ya kwaďi giya, ahankali yazame jikinsa ya kwanta tareda lumshe idanu, sunkai minti goma ahaka shiyana hutawa itakuma tana kuka, saida yaga zata cika masa kunne da kuka sanan yatashi zaune yadaka mata tsawa, wlhy idan bakimin shiruba zanmiki mai kankat 'yar rainin hankali kawai, ya 'karasa jikin gadon, kafarsa ďaya yaďora saman gado ďaya akasa ya ce, "buďe idonki ki kalleni da 'kyau, wlhy daga yau kika 'kara aikata wani abu agidannan saina bambance miki tsakanin aya da tsakkuwa mara kunya, gobe idan kin gadama kisake faďin abinda duk yazo a bakinki, zakiga yanda zanyi dake a gidannan, wananma kaďan nayi miki idan kika 'kara zakisha mamaki idan kunne yaji jiki yatsira ya sauke 'kafarsa tareda ficewa daga ďakin.
       Kara rushewa da sabon kuka tayi, ta sakko daga kangadon tanufi bayi, brosh da makilin taďauka tashiga goge bakinta, tawanke yafi sau goma sanan tabari tafito tana hawaye bayan tasake sabon wanka, shiryawa tayi ahankali tafice gidan saboda babu kowa afalon, tanaji mai gadi yana cemata alhaji ya ce, "kar abar kowa yafita inda magriba tayi amma saitayimasa tsaki tafice sai gidan dady.................




Luv u oll my fan's
©2017
[03/03 17:33] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》




NA BILKEESA IBRAHEEM 
       {♡Bilyn Abdul♡}


Kuyi ha'kuri da wannan, yau naje anguwane, bansamu damar yin typing ba, luv u oll


35

.......Shikam koda yafita ďakinsa yatafi, bayi yanufa kai tsaye dan dole shikam saiyayi wankan tsarki, sai wani murmushi yake kamar wanda yayi mai gaba ďaya ( nace uhmm su ya Mahmud manya) bayan yafito jallabiya kawai yazura yatafi masallaci.
   Itakam aunty bily batamasan hidimar dasukeyiba tana ďakinta.

Nurr kuwa gidan dady tanufa tana cigaba da kukanta (nace su Nurr an iya yaji)a falo taci karo dasu ya mustapha suna kallo, ya mubarak ya ce, "kekuma lafiya zaki shigo da kuka, ta 'kara fashewa dawani sabon kukan dagudu tashige ďakin mama, suka rakata da idanu sukam.
   Tana zuwa tafaďa kan mama tana kuka, mama tayi mata 'kya'ky'kyawan ruko tana tambayar lafiya?, kafin tabata amsa daddy yashigo, dama al'adarsa ce idanyadawo daga tafiya yazo ďakin matar da yabari a gida susha hira.....tsayawa yayi yana kallonsu, ya ce, "lafiya kuwa??.
    Mama taďago tana kallonsa wlhy alhaji nima bansaniba yanzu tashigo min tana kuka, baice komaiba ya zauna bakin gado, wayarsa yafiddo daga aljihu yafara kiran ya Mahmud, bugu ďaya biyu ya ďauka, dady ya ce, "Mahmud kana inane??,    dady yanzun nafito daga masallaci zan tafi gida.
    To kazo yanzu kasameni agida.
  To dady.
Mami ma tashigo dan tana sallah taji maganganun su mustapha.
  Ta ce, "lafiyadai ko??.
 Dady ya ce, "muma ita mukesonji, guri tanema ta zauna itama.
   Dayake masallacin kusada gidane a kankanin lokaci saiga ya Mahmud, afalo ya iske su ya mubarak suka gaisheshi, harya nufi saman dady sukace masa yana ďakin mama, ďakin maman yadawo yashiga, gabansa yafaďi dan ganin Nurr kwance ajikin mama tana kuka, yariyar nan fa batada hankali zata iya faďar abinda nayi mata.
   Tunda yashigo mama ke watsa masa harara, dady ya ce, "zoka zauna mana, 'karasowa yayi yazauna kusada 'kafafun dady jiki a sanyaye dan yakula da hararar da mama take masa, ya daure yagaida iyayen nasa, dady da mamine kawai suka amsa amma mama shiru tayi.
    Dady ya ce, "Nurr tashi zaune.
  Nurr ta tashi tana sharar hawaye, dady yakuma faďin share hawayenki kimana bayani dallah2 yanda zamu gane, ido ya Mahmud yawaro tareda buďe baki yasan halin yarinyarnan sairai zata iya faďar komai, dady yana kallonsa amma saiya sharesa ya ce, "ma Nurr ina saurarenki.
   Saida tajuyo takalli ya Mahmud ya gallah mata harara, tayi saurin kauda kai tareda faďin dama.......da sauri ya Mahmud ya katseta da faďin dady bafa wani abu nayi mataba, laifi tayi na tsawatar mata shine ta tahonan.......dady yaďaga masa hannu alamar yay shiru, yakuma cewa Nurr faďi.
  Tasake buďe baki zatayi magana.....ya Mahmud ya ce, "k wai bakida hankaline?"!!!!. Cikin tsawa yayi maganar.
   Itama mama tadaka masa tsawar to ubanmu saika haďa hardamu tunda mumukace tafaďi kajimin yaro, tunda kasan bakada gsky ai dole kayimata mazurai karta faďa, wlhy ka kiyayeni zan 6ata maka rai yanzunan.
    Mami ta ce, "a'a dukma haka bata tasoba tunda ai ba'asan ita mitayi masaba, abari sai anji sanan abashi laifi, amma ba haka kawai ayanke hukunciba.
   Dady dai baice musu komaiba, mama ta ce, "Nurr faďi karki sake kallonsa saikin gama faďa, Nurr ta share hawaye ta ce, "mama nidai bazan sake komawa gidansaba anan zan zauna danni ba 'yar iska baceba........da sauri mami ta katseta to ya isa haka.
   Ya mahmud yay saurin dafe kai.
   Suduka sun fahimci inda zancen nata ya dosa, dady ya girgiza kai yana bin ya Mahmud daketa sunkuyar dakai da kallo, yay gyaran murya tareda faďin to kukan ya isa haka share hawayenki, Nurr ta share hawaye harda 'kara narkewa ajikin mama.
   Dady ya maida kallonsa ga ya Mahmud ya ce, "kai babban yaya komai aii saida lallashi, hakuri akeyi kaga har yanzu akwai sauran kuruciya tareda Nurr, yanzu dai kaďauketa kutafi dasafe kazo ina nemanka.
   Kuka Nurr tafasa musu tareda faďin itafa bazata komaba.
   Mama da tunďazu bata sake cewa komaiba ta ce, "Alhaji inaga yabarta saida safe idan ta huce ta koma,.
   Dady yay ďan jimm tareda kallon ya Mahmud tokai kaji kabarta ďin takwana???.
   Babu damuwa dady takwanaďin.
   To shikenan ALLAH yay muku albarka.
   Amin ya amsa, daga nan  yami'ke yana faďin saida safenku.
   To ALLAH yatashemu lafiya, ka gaida bilkeesun, to dady zataji insha ALLAHU, mami ma tace ya gaida aunty bily, amma mama batace 'kalaba, bayan fitarsa dady yashiga yima Nurr nasiya mai ratsa jiki, tareda lallashi, yadaďe yana kwantar mata da hankali daga baya yatashi yatafi ďakinsa.
  Mami ma tafice.
  Mama tace Nurr tashi kici abinci kinji, ta ce, "to, abinci mama takawo mata taci ta 'koshi dama yunwa takeji, tayi wanka ta haye gadon mama, jitake tamkar tafito daga gidan bursin yau zatayi barci harda sale6a, sai wajen 'karfe ďaya mama tadawo ďakin inaga daga ďakin dady take, zuwa sanan Nurr tayi barci, tahawo gadon ta zauna, ido ta 'kurama Nurr cike da so da 'kauna, ta shafa kanta tanamai addu'ar ALLAH yasa ta kwantar da hankalinta ta zauna a gidan mijinta lafiya, fatanta baiwuce taga 'ya'yan ya Mahmud da abar sonta Nurr ba, duk cikin 'ya'yanta tafison ya Mahmud kawai tana kawaicine saboda kasancewarsa ďan fari, Nurr ta motsa ahankali, saikuma tabuďe ido ta tashi zumbur tana kallon mama.
   Mama ta ce, "auta kin tashine??.
   Nurr ta ce, "mama lafiya naganki a zaune bakiyi barciba??, mama tajawota jikinta ta kwantar da kanta saman cinyarta, ta ce, "lafiya law Nurr ďina kawaidai ina zaunane.
   Nurr tayi ajiyar zuciya, wlhy harnaji sanyi mama, banaso naga bakida lafiya sainaji nima banida lafiyar.
  Mama tashafa kanta tana murmushi, cikin sigar lallashi ta ce, "Nurr ďina kinason yayaku kuwa??, Nurr tayi shiru dan tambayar tazo mata abazata, taďan ďago ido tana kallon mama, saitaga ita take kallo, tayi 'kasa da idanunta tanaďan murmushi, mama nibana sonsa, amma zan iya zama dashi.
    Mama tayi ďanyi murmushi, saboda mi ba'kya sonsa??, Nurr ta gyara kwanciyarta tareda kama hannun mama tana wasa dashi, mama babu komai nidai banajin ina sonsa, saikuma banason yanayimin faďa, shikuma ya mahmud yacika yima mutane faďa, amma idan yayi wani abun yana burgeni.
   Nanma mama murmushi tayi domin ta hango wani abu a 'karkashin zuciyar Nurr, takula 'kuruciyace kawai ke danne matashi, taja numfashi tareda shafa kan Nurr, to shikenan autana tunda zaki iya zama dashi inaso ki kwantar da hankalinki kinji, daga yanzu idan yace miki kiyi abu kiringa yi tunda ba'kyason faďa, kidaina yimasa abinda baya so kinji??, Nurr taďaga kai ahankali.
   Mama tacigaba da faďin sanan kuma idan yay miki abu kiringa kirana kina sanar min basai kinzo gidaba, ni zan masa faďa dakaina kinji??, nanma kai ta jinjina, cikin hikima mama ta rin'ka yimata nasiha da nuna mata abinda yadace tayima mininta, sundaďe kafin daga baya suyi barci.

A6angaten ya Mahmud kuwa yana zuwa gida saiya haye samansa, abincima saican aunty bily takai masa, kuma tayi2 ya'ki faďa mata damuwarsa, ya ce, "dai kawai suna gidan dady tareda Nurr, dataga bayason faďa mata sai kawai ta 'kyalesa ta ďakko masa wata hirar daban, sama2 yake amsata daga bayama sai kawai yatashi yashige bedroom yakwanta.
  Kai kawai aunty bily ta jinjina tana binsa da kallo, mijinta kenan mai abubuwan mamaki..................




Luv u oll my fan's
©2017
[04/03 15:08] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》





NA BILKEESA IBRAHEEM 
      {♡Bilyn Abdul♡}



34

......Da safe da'kyar aunty bily ta lalla6ashi yayi break, tarasa irin wanan shiga damuwa haka, koda yake da alama talura Nurr ba'a gidan ta kwanaba, toko miya haďasu oho, tunda bai gaya mataba itama bazata tanbayeshiba insha ALLAHU.
     kaďan yaci abincin yami'ke, aunty bily tabishi da kallo, my handsome badai harka 'koshiba??.
   Yaďan kalleta fuskarsa babu walwala, kai kawai ya jinjina mata batareda yayi maganaba.
  Itama batace komaiba saima ďaukar jakkar aikinsa datayi, juyawa yayi yanufi 'kofa itama saita take masa baya, har mota tarakashi, taďan du'ko ta 6angarensa tareda faďin ALLAH ya tsare, ala66ansa ya amsa da ameen, ta ce, "yaya dan ALLAH zanje gidan dady nataho da Nurr, saida yay mata kallon tsaf sanan ya ce, "A'a kibarta zata dawo anjima aii.
   To nidai dan ALLAH kabarni naje.
   Afusace ya ce, "kinsan dai banason gardama ko??.
    kayi ha'kuri tafaďa asanyaye, ALLAH ya huci zuciyarka, bai tankataba yadatada motar yafice, bin motar tayi da kallo harta fice daga harabar gidan, mai gadi yamaida gate ya kulle, juyawa tayi cikin gida zuciyarta cike da tunani kala2, saidai dayake tasan halin kayanta abin bai cika 6ata mata raiba sosai, (kunsan abinda kakeso bako yaushe yake laifi agarekaba).

Gidan dady yanufa kamar yanda ya umarceshi, afalo ya iske su mustapha suna break suka gaidashi ya amsa fuskarsa babu walwala,  saman dady ya haye suka bishi da kallo, mubarak ya ce, "bro's wai mike faruwa agidannan ne?? Naga jiya anan Nurr takwana kuma naga yau ya Mahmud kamar yana cikin damuwa.
   Mustapha yaďan ta6e baki wlhy bansan musuba, 'kila ta haďosune, shiyyasa ni bana sha'awar auren 'karamar yarinya, nifa daza'abi ta shawarata toda bazan auri 'yar family ďinnan ba amma yazamuyi tunda maigayya mai aiki yabar wasiyya akan hakan.
    Dariya sosai ya mubarak yakeyi, ya ce, "malam aini tunima nayi maka mata a family ďinan, garama ka shirya.
   Ya mustapha ya harareshi, tareda mi'kewa yabar falon.

Afalon dady kuwa ya Mahmud nacan zaune gefen dady bayan ya gaisheshi suka ďan tattauna akan kasuwanci sanan dady ya ce, "kasan abinda yasa nace kazo yau?, ya Mahmud ya girgiza kai.
   To dama akan matarkane Nurr, mahmud dolene saika 'kara ha'kuri sosai akan Nurr, yarinyace sosai, saninkan kane abakwani aka haifeta, saida tayi wata uku akwalba sanan akabama mahaifiyarta, sanan tazo kuma ta kubce mata alokacin datake bu'katar jin ďumin jikinta, mahaifiyarka tana son Nurr so bana wasaba, karka bari sa6ani yashiga tsakaninka da ita adaliln Nurr.
   Inason ka canja salon takun zamanka da Nurr, kasandai abinda nike nufi domin kai mai ilimine, ina alfahari dakai fiye da kowane ďana acikin gidanan, nandai daddy yayta yimasa nasiha da koya masa dabarun zama da mace.
   Yaji daďin shawarwarin dady sosai dan haka yay masa sallama ya sakko.
   Ďakin mama yafara shiga, tsayawa yayi cak dan ganin Nurr daga ita sai zani iya 'kugu da vest, suna zaune itada Saiff akan gadon mama suna lido, yacika fam da kishi, sukam bama susan da zuwansaba.
   Ya daka musu tsawa gabaďaya suka juyo suna kallonsa afirgice, ya gallama Saiff harara, dallah tashi kafice min anan kawani tsareni da idanuwa kamar ba'konka.
   Saiff yami'ke yana kunkunai yafice, itako Nurr saita haďe fuska tamau tacigaba da lido ďinta, ya 'karasa jikin gadon fuska ahaďe, "k yafaďa murya aďage.
   Taďago tana kallonsa amma fuskarta babu alamar wasa, ya ce, "wanan wane irin salon iskancine??, cikin rashin fahimtar zancen nasa ta ce, "iskanci kuma kamar ya??, ransa ya 'kara 6aci dan ganin tana neman raina masa hankali, yaďan cije ke6ensa na'kasa, duba kiga shigar dake jikinki amma saboda wula'kanci har kika iya zama kuna lido da Saiff ko?, ta turo baki gaba, to dan ALLAH miye aibun wanan kayan?, kuma Saiff ba ďan uwana bane??.
    Jiyake tamkar ya falla mata mari, amma bazaiyi hakaba kodan saboda mama, yariga yatanadi hanyar maganin Nurr dan haka ya juya yafice abinsa batarda ya tanka mataba, itako tarakashi da harara kai kaikam ajarabar masifa zaka 'kare fiti nanne kawai.
    Bayan yashiga ya gaida mami yafice zuwa office.

6:3pm 
      Dady yashigo ďakin mama, Nurr tana zaune bayan ta idar da sallah, ta gaisheshi ya ce, "Nurr!!".
    "Na'am dady".
        "Kishirya yanzu mijinki zaizo ku koma gida".
   Fuska ta kwa6e tamkar zata fasa kuka, dady dan ALLAH a barni sai gobe.
  Harara ya sakar mata, banason shashanci kitashi kishirya nace.
   Ta share hawayen dasuka fara zarya a fuskarta ta ce, "to dady zanyi yanda kace, murmushi dady yayi tareda shafa kanta, yauwa 'yar albarka ALLAH yay miki albarka kinji, amin dady Nurr tafaďa tana shashsheka, ya zauna yana lallashinta, saida yaga ta bar kukan sanan yatashi yafice domin isha'i ta gabato.
      Bayan Fitarsama mama ta 'kara lallashinta damata alkawarin indai yasake 6ata mata rai saita 6ata masa itama, kuma daga yanzu duk abinda yay mata takirata tafaďa mata (araina nace lallai mama wanan ďiyar taki tacika wauta fa).
     8:5pm 
  Ya Mahmud yashigo gidan, saida yafara zuwa wajen dady sanan yashigo ďakin mama zuwa sanan Nurr tagama shiryawa, bayan mama tayi musu Nasiha suka fice, sunyima mami sallama itana, tunda suka fita daga gidan babu wanda yayima wani magana, tana gaba yana biye, sai shatatar da hawaye take har suka shiga cikin gidan.
    Dakinta tawuce dan babu kowa afalon, shima yanufi nasa ďakin, tana zuwa ta haye gado tana kuka kamar wadda akaima dukan tsiya, tana nan kwance aunty bily tashigo, ta 'karasa jikin gadon ta zauna, ďago kan Nurr tayi tana lallashi, da'kyar tasamu tayi shiru, tana cikin lallashinta wayarta tafara wringing, taduba taga my handsome, mi'kewa tayi domin amsa kiran saraki, Nurr kuma tashiga bayi danta watsa ruwa.
    Afalo ta iskeshi sanye da gajeren wando da vest, yajingina kansa da kujera idanunsa na kallon silin, ta 'karaso ta zauna, ta ce, "gani.
   Shiru yayi tamkar bai jitaba, saida yaja tsawon minti biyar sanan yasauke kansa yana kallonta, shayi nakeson sha, to, amma abincifa??, ya ďan girgiza kai tareda lumshe idanu.
  Mi'kewa tayi tanufi kicin ta haďo masa shayi mai kauri ta kawo masa.
   Yatashi zaune sosai, shayin ya kar6a yana juya cokalin aciki, idonsa nakan tv ya ce, "bilkeesu!!.
   Na'am ta amsa cikin sar'kewar murya dan tadaďe bataji cikakken sunantaba a bakin ya Mahmud.
   Yaďan ja numfashi, inaso kishirya gobe idan ALLAH yakimu muje wajan doctor Ashir abuďe miki mahaifarki.
   Atsorace take kallonsa kuma cikin mamaki, yaya miya kawo wanan maganar kuma?, baice komaiba yaďauki shayin yana sha, saida ya haďiye wanda ya kur6a sanan ya ce, "daboda ina bu'katar haihuwa bily, inason 'ya'ya, shin haka kuke bu'kata namutu banga ďan kainaba?, kokuwa sai tsufa ya riskeni?, wasu 'yan kwalla suka taru masa agefen ido.
   Cikin matu'kar tausayi take kallonsa, tabbas ko ita datake mace mai rauni tafi ya Mahmud dauriya akan rashin 'ya'ya, tasan yana matu'kar son yara, tuni tana kula dashi akan yawan damuwa dayake shiga musamman idan ya ďakkosu Abdul idan zai  maidasu, taďan share hawayen dasuka zubo mata, yaya ba wananan bace mafita, kasan dai abin da doctor ya ce, "akaina, nasan kuma baka mantaba, yaya kadai canja shawara nake gani.
   Shiru yayi yana mai tsura mata idanu ko 'kyaftawa bayayai, ahankali ya ce, "bily to kinema mana mafita.
   Eh... yaya a kwai mafita nake gani aii, yaďan lumshe ido ya buďe alamar tafaďa, takama hannunsa tana murzawa, saidaifa kayi ha'kuri dan bansan yanda zaka fahimci zancen nawabane, amma kila shawarata tayi maka kokuma akasasin haka, .......tacigaba dafaďin yaya karka manta Nurr matarkace, itama zata iya haihuwa miyasa bazaka canja akalar zamanka da itaba??, miyasa bazaka janye 'kudirinka na bayaba??, nidakai duk muna bu'katar yara, amma ni bazan iya haifa makasuba saboda matsalar dake taredani, amma kanada wata matar, zakuma ta iya haihuwa yaya kaima kasani....ta'kare maganar da hawaye.
   Hannu yasa yana share mata hawayen, yajawota jikinsa ya rungume yanaďan buga bayanta ahankali alamar lallashi, to kukan ya isa haka, share hawayenki.
   Lallashinta yay tayi har saida ta daina kukan.
   Nurr dake tsaye tanajin duk abinda suke faďa tasheka da gudu ďaki...............







Luv u oll my fun's 
©2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *