check your best novels here

Tuesday 14 March 2017

SABON AL'AMAREE 50/53

[12/03 16:29] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE 》》







NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡bilyn Abdul♡}











50

...........Murmushi ya Mahmud yasaki wanda har ya bayyana matsakaiciyar wushiryarsa dake tsakanin fararen ha'koransa, Nurrina kenan ke kina tunanin wani abune yake damunki??.
   ALLAH yaya serious nake maka maganar nan, karka ďauka wasa nakeyi, ta ďaga rigarta kallifa kagani dan ALLAH.
   Takardar hannunsa ya ajiye ya fuskanceta sosai, yana cigaba dayin murmushinsa, ya ďora hannunsa kan cikin nata kai Nurrina kumafa da gsk kikeyi cikinki ya'kara girma wlhy, ta langa6e kai gefe to kagani shiyyasa nace bari nasanar maka kakaini asibiti adubani, wlhy inajin tsoro.
    Jawota yayi jikinsa yana shafa cikin kinga ki kwantar da hankalinki inagafa yawan kwaďayin dakikeyine yasa kika fara tunbi, kai yaya tunbi kuma?, nikam wlhy banason tunbi, dan haka zan fara training kwannan kuwa, A'a basaikinyi training ba kibari zan sanar da Dr Asheer saiya baki magani, amma koba nanan karkiyi wani training shima matsalane ga mace, ta ce, "to shikenan kafa amsomin dan ALLAH, Karki damu zan kar6o miki.
   Ya faďa mata hakane dan kar wataran tadage da yin training wajen tsalle2 taimasa aika2.
   Ta yunkura zata tashi daga jikinsa, A'a ina kuma zuwa??, zan kwantane yaya kacigaba da aikinka kaima, wlhy nagaji sosai gashi gobe idan ALLAH yakaimu aunty bily ta ce, "zamuyi tashin wuri.
   Gsky ne, dan zanzo da abokaina suci abincin sallah, ta kwanta tana dariya ainima gidan dady zanje ko gidan deena na wuni, ya ce, "kilaba.
   Yaya kamar ya 'kila? bazaka barni najebane??, zan barki amma sai jibi idan ALLAH ya kaimu, kinga nace abokaina zasuzo gobe baikamata ba kuma ace wata acikinku ba tanan, to shikenan yaya ALLAH yakaimu jibin.
    Amin Nurrina yafaďa cikin matu'kar jin daďi, lallai Nurrinsa tafara hankali, da dane aikoda bala'i saitaje, babu daďewa barci ya kwasheta, shikuma yaciga dayin aikinsa.

YAU TAKE SALLAH
          YAU take sallah dukkan al'umar musulmai sun tashi cikin matu'kar farinciki, kowane 'kofar gida ka gifta 'kamshin suya kakeji da jar miya, maza da 'yammata da yara sunata shirin zuwa idi, kai harma dawasu matan auren, abin gwanin sha'awa da birgewa.
    Tunda asuba aunty bily ta tashi take aiki itada ya Mahmud dake tayata wasu abubuwan saikuma masu aiki, Nurr dai bayan tayi sallah barci ya Mahmud yasata takoma dan tana bu'katar abarta taringa isashshen barci.
    Wajen karfe bakwai itama ta tashi saitaje ta canji ya Mahmud akichin ďin shikuma yadawo falo yazauna.
   Zuwa 'karfe tara sun kammala komai daya dace, suka shiga kujiba2r gyara gidan, alokacin kuma ya mahmud yanacan yana ďaukar gayu aďakinsa, suna gama gyaran falo suka koma ďakunansu nanma suka gyara tsaf.
      Ya mahmud yasakko cikin wata ďanyar Sky blue ďin shadda, yau harda malun2, wow!!!! Nafaďa a zuciyata guy ďinfa yagama hađuwa tamkar angon dazaiyi auren fari, sai baza kamshin turarensa yake, kafarsa sanye da dark blue ďin takalmi sau ciki sai 'kyalli yake da ďaukar idanu, asama ma ya murza hula 'kube dark blue sai mai'ko takeyi, ďakin aunty bily yafara shiga yana ďaura ba'kin agogo a hannunsa.
    Tsayawa tayi cak tana kallon ikon ALLAH daya girma ya ďaukaka, ko 'kyafta idanu batayi, tunanima takeyi anya wannan mijintane kodai canjashi akayi, a slowly ya 'karaso inda take ya hure mata idanu takawo numfashi da 'karfi.
    Cikin kunnenta ya ce, "yammatana mikike kallo haka, tayi murmushinta mai 'kayatarwa, mijinane yatafi da dukkani hankalina, my handsome irin wanana ďaukar wanka haka saikace mai shirin sabon aure??, yayi 'yar dariya to kika sani ko yau nasamo ta uku??, humm aiko ina addu'a ALLAH ya makantar da kowace mace daga kallonka.
    Yaďan zaro idanu my bily wanan wace irin addu'ace kuma??, yazakimin bu'kulun samun sabuwar amarya??.
   Ta ta6e baki, ai inda akan amaryarnane zan 'karama wata addu'ar yanzu,, a'a yi ha'kuri karki zamin narasa amarya aranar sallah, ai kama ďauka karasa, kai namune mukaďai dagani sai Nurr ďin mama.
   Murmuahi yasakeyi tareda manna mata kiss akumatu, ALLAH yabarmin ke my bily, kemafa kin iya kishi?, amma miyasa bakiyi da Nurr??,  aini ban ďauki Nurr kishiyaba she is my blood sister!!.
    Ya kuma manna mata kisses a kumatu ina al'fahari dake my bily, ke macece tamkar da dubu ALLAH yay miki albarka.
   Ameen yayana ngd tafaďa tana manna masa kiss itama, ta ce, "sai masallaci??, ya ďaga mata kai yana murmushi.
   To adawo lafiya ALLAH yatsare mana kai, yadawo mana dakai lafiya.
  Ameen bilyna ngd da addu'arki, bari nawuce karna makara ko, ya kalli agogonsa, to bey bey.
      Shima hannu ya ďaga mata yafito, ďakin  Nurr ya shiga. 
   Gaban madubi ya isketa zaune tana tsara kwalliya, lallai yau ranar farincikice irin wanan kwalli haka, Nurr tajuyo tana kallonsa, itamadai yayi mata 'kyau lallai kwalliyar tasa tabada ma'ana, jitayi kamar tace karya fita wasu matan su gansa (na ce, tofa Nurr kina kishi kar irinsu Deexerh gwauraye su 'kyasa miki shine??).
    Cikin takun gayu ya 'karaso inda take, tabayan kujerar yaran'kwafo ya ďora kansa a gefen kafaďarta suna kallon juna ta madubi, Nurr ta lumshe idanu tana murmushi, shima murmusawar yayi, Nurrina miyasaki murmushi haka??, takuma murmusawa har kumatunta suka lotsa, babu komai yaya happy sallah!!.
     D/same 2u my luv!!, yafaďa yana sumbatar kumatunta, kinyi kyau Nurrina, kaima kayi 'kyau aii yaya.
   Wani daďi yaji ya tsargashi azuciya, da gsk??, ta jinjina kai ALLAH kuwa yaya, ya lumshe idanunsa l luv u Nurrina naji daďin yabawarki, kema inason kafin nadawo na tarar kinďau wanka na fitar hankali, dan dana dawo zan bada barka da sallah.
    To ALLAH ya kiyaye hanya, ameen Nurrina, amma baza abani wata tsaraba ta barka da sallah??.
    Taďan kalleshi cikin rashin fahimta, to ni yaya minike dashi dazan baka??, keko kikeda abin bani Nana maryam, ya mi'ko mata kumatunsa a bani sumba ďaya mai 'kyau.
    Hannu tasa ta rufe fuska ALLAH kuwa yaya inajin kunya, babu wata kunya nidai sai anmini, yafaďa maganar cikin shagwa6a.
   Ta ce, "kai yaya saikace yaro??.
   Ni yarone mana idan ina gaban Nurrina dan haka idan bakiminba bazanje masallacinba.......A'a ba ayi hakaba to rufe idonka, gam ya rufe idonsa kuwa ta manna masa kiss a kumatu.
    Wow!!!! Yafaďa tareda sauke wani nannauyan Numfashi, l luv u my Nurri!!!!.
   Hannu tasa tarufe fuska, ya ce, "natafi idan nadawo ma gauraya.
    Yana fita wani haushi ya turni'ke Nurr, komiyasama tayi masa kiss ďinnan??, tasa tawul tana faman goge bakinta(na ce, "humm wai daga baya kenan inji 'keya).
      Da har ta fasa kwalliyar saikuma ta ce, "aibama danshi zanyiba, zanyine dan ina murna yau sallah, saita cigaba da tsara kwalliyarta, ta shirya cikin wata haďaďďiyar atamfa orange color ta naďa ďaurin ďankwali na ďaukar hankali, kai masu karatu Nuriin ya mahmud tafitofa, dama 'kyawun karamin ciki yana ďawainiya da ita, ďan cikinta yaďan fito kađan saiyayi mata 'kyau kuwa, ta saka sarka da zobuna abin hannu dadai duk abinda yadace, ďakin aunty bily tashiga, wow!!! Nurr kinyi 'kyau wlhy, kai auntyna kema kin haďu kinma fini yin kyau.
    Aunty bily tayi dariya kin rama kenan, itama dariyar tayi, ta ce, "aunty bily ALLAH turaren ya Mahmud nakeson satowa, ina kuma tsoron karna shiga ďakinsa yadawo ya ritsani.
   Dariya aunty bily tayi, ai bazaice komaiba kije kawai ki sawo, kina ganin babu matsala aunty ???, insha ALLAH aunty bily tafaďa.
   Nurr ta ce, "to ina zuwa, samansa ta haye ta feso turare bana wasaba, ashe wajen kala huďu yake haďawa shiyyasa takan kasa banbance turaren nasa, akan madubinsa ta tarar dasu reras dan haka taďauki kowanne tafesa, dama ta feso wasu ađakinta, tuni jikinta ya kwaure da 'kamshi harma yana hawa kai, amma ita ko ajikinta haka takeso.
    Tana sakkowa su ya Mahmud suna shigowa falon shida gayyar abokansa harsu wajen bakwai, idanu yakafama Nurr tamkar yau yafara ganinta gashi duk tacika falon da fitinannan 'kamshi, sumadai abokan nasa idonsu na kan Nurr, ahankali ya 'karasa tareda kama hannunta ya kareta sosai dankar abokan nasa suganta, ( nace ya mahmud kishi kenan?? ) saida yakaita ďaki sanan ya rungumeta Nurrina irin wanan 'kyau haka kamar zaki za6en sarauniyar 'kyau??, batace komaiba saima ta6e baki datayi, yay kissing ďin fuskarta, kinga ďauki gyale kisaka sanan kifito ku gaisa, bai jira amsartaba yafice abinsa.
     Jitayi kamar karda tafita,, amma abokansa sun riga sun ganta kuma harda yayyenta aciki bai dace ace taki fitaba, gyale taďauka kalar kayan tafito, itama sanan aunty bily tafito suna gaisawa, Nurr ma takarasa tana gaishesu, ya mahmud yakasa ďauke ido daga kan matan nasa, kowacce tabada ma'ana acikin kwalliyar sallar.
   Aunty bily takama hannun Nurr suka tafi kichin, abinci suka fara shiryawa a dinning ya mahmud yataso yana faďin aikamata yayi ashiryashi afalo ko? inaga zaifi musake sosai.
   Okey babu damuwa, afalon sukacigaba da shirya komai ya Mahmud yana tayasu dawasu abubuwan, abincine kala2 na gargajiya dana zamani, ga soye2 na nama da abinda yadanganci filawa, sai lemuka kala2 suma duk namu nagida, falon ya kaure da wani shahararren kamshi na musamman.
    Sukansu abokan na ya Mahmud sun 'kagara sufara ďibar gara dan duk kamshi yacika musu hanci tuni.
   Har sun tsugunna zasu fara Sarving nasu ya Mahmud ya ce, "ku kyalesu su zuba dakansu, karku wahalar da kanku.
    Hafiz ya ce, "kai Sardauna mufa bakinkane??, aina sani idan kunji haushi kuyi aure mana, dariya sosai sukeyi tareda faďin abinma 'yar gorice Alhaji??, to gara aimuku gorin ko kwayi zuciya kuyi kuma, kudaina bin gidan mutane cin tuwon sallah.
    A'a kaima yaushe kafita acikinmu?, kwanannane fa, amma karka damu zamu rama muma muna hanya insha ALLAHU.
   to ALLAH ya yarda ya mahmud yafaďa yana cire babbar rigarsa.
    Sosai sukaci abincin sunata zuba santi, komai saida sukaci tareda yabawa matan na ya mahmud masu kwazo da iya girki.
    Sun dađe agidan daga baya sukai musu alkairi suka fita harda ya Mahmud ďin, amma ya canja kayansa zuwa wata ďanyar farar shaddar itama mai mai'ko.......................










Luv u oll my fun's 
©2017
[14/03 11:14] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》








NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡Bilyn Abdul♡}




HIQAYA ONLINE WRITER's
         




51

........Haka bikin sallah yacigaba da gudana, su Nurr buri yacika ansha yawo gidan dangi harda inda ba'a aiketaba duk saida taje, gidan dadyne karshe sukaje suka wuni itada aunty bily, har dare, saida magriba suka dawo gida.
    Rayuwa tanata tafiya yanda ALLAH ya tsara, yau akayi sunan ďangidan deena wato Ibrahim khalil, to ALLAH yaraya babana daduk kan sauran 'ya'yan musulmai, taron suna ya 'kayatar yanda yakamata su Nurr sune amarori kirjin biki, komai saidasu, taron sunan ya 'kyatar yanda yakamata, dangi sun nuna bajinta, dahaka taro yatashi lafiya kowa ya kama gabansa.

Yau Nurr agajiye take saboda shagali dasukasha, akan gado tazube tana maida numfashi na gajiya, ahankali ya mahmud yaturo 'kofar yashigo da sallama, tana daga kwance ta amsa masa, akusada ita yazauna yana faďin 'yan suna kamarku daban.
    Nurr tayi 'yar dariya tana tashi zaune, lallaikam munsha  shagalin suna  yau, wlhy bakaji 'kafafunaba yaya kamar su cire, tofa miye dalili??, wlhy zirga2 ce kawai yaya, kafafuwan yakamo ya ďora saman cinyarsa yanaďan matsa mata ahankali, Nurrina harmafa sun ďanyi fushi.
   To yazanyi babynane yajamin haka, daga yaukuma sai wani, wannan kam ya wuce, hakane daga nan kuma saike, humm kaji yaya dawata magana nikuma miya haďani da suna??, murmushi yayi yana kallon fuskarta kika sani kokema kin samu cikin??.
     idanu tazaro waje a'a yaya daina yimini wannan fatan inani ina ciki yanzu, nifa burina nakoma makaranta kawai.
   Ya tuntsire da dariya, nikuma kinga burina naga 'ya'yana aduniya, kuma kece zaki haifamin da bily.
   Toni yaya ainayi 'karama dayawa garama aunty bily ita babbace, sai dai nace ALLAH yasa ta haifa maka to, ya langa6e kai gefe "k baki fatan ki haifamin sai bily kawai??, taďan kwa6e fuska dan bata fata ta haihu dashi itakam, so take idan yasaketa taje ta auri wanda take so ta haifi yaranta acan (na ce, "huumm hajiya Nurr kenan, ashe bazaki farka a wanan mafarkinba kenan??).
    Yaďan matsa kafar takawo numfashi, tunanin mikike kuma Nurrina??, ta ta6e baki babu komai.
    Shiru yayi yayi niyyar gaya matane tanada ciki, to amma yaga yakamata ya ďan tsahirta sai nan gaba, ya ce, "kinga mubar wanan show ďin, yanzu dai tashi muje na gasa miki jiki da ruwan zafi saikiji daďin jikinki.
    Ta ce, "kai yaya kullum saikaita maidani 'karamar yarinya.
   Ooh namantafa ashe k babbace, to amma yanzu kika gaya min k yarinyace ba yanzu zaki haihuba.
    Shiru tayi dan ganin ya harbo jirginta, ta zame 'kafarta daga cinyarsa yaya bari nayi wankan dan nafara jin barci, to jekiyi yafaďa yana kwanciya akan gadon, harta shige bayi yana binta da kallo, komai na Nurrinsa mai 'kyaune, yana son yarinyarnan sosai amma yana damuwa sosai idan yatuna ita bata sonshi, ya lumshe idanu tareda fitar da huci mai zafi daga bakinsa, ALLAH yakaimu ranar da Nana maryam zata soni koda rabin son danake matane ( na ce, "ameen ya Mahmud).
      Babu daďewa tafito tayi shirin barci suka kwanta, dukda ita ba'a son ranta yake kwana aďakin nataba, amma babu yanda zatayi tunda yayantane har yanzu yanada daraja irinta babban wa agareta, kai tsaye bazata iya yimasa rashin kunya ba ko wani abu mara 'kyau, saboda tarin kwarjini da ALLAH yabashi.
   Sau'kin tama yanzu ba kullum yakan cika matsa mataba, wani lokacin ma acikin kwana biyu dayakeyi a ďakinta saiya bar ďakin nata bai mata komaiba, kokuma ya kusanceta sau ďaya acikin kwana biyun.
   A hakama abun na bata haushi amma yazatayi, tana gudun tsinuwar mala'ikune akanta, agefe kuma ya Mahmud yakan mantar da ita soyayya ko kiyayya ayayin dayake nuna mata zallar soyayyarsa mai aminci da nagarta, sai bayan wucewar komai sanan takan tuna da bata sonshi.
     Taďan tsurama fuskarsa idanu, babu laifi ya Mahmud 'kyakykyawane dukda kasancewarsa ba'ki sosai, gashi nutsatstsen mutum mai ilimi da iya zama da mutane, yanada faďa da saurin fushi, ga son addini da dangi, koya ďan uwansa yake zakaga yana kaffa2 dashi, ya iya soyaya mai tafiya da kwanyar mace, tuni zaitafi da imaninki ya mantar dake damuwar ki, abinda ke haďata dashi masifa ya Mahmud ďan hayaniyane dukda shi baya son haya niyar........ahankali ya buďe idanunsa shima yana kallonta, Don yanaji ajikinsa shi take kallo, tai saurin rufe nata idon, dan azatonta barci yake, yayi murmusgi mai sauti, ki buďe idonki Nurrina ki kalli mijinki babu mai hanaki, ni nakine babu shamaki Haskena!!, itadai takasa ko motsi saifaman rintse ido take tana murmushi, kunya takeji ya kamata tana kallonsa, ya sumbaci idanunta shima yana murmushi ya ce, "Nurri sarkin kunya, inason mace mai kunya, rungumeta yayi tsam ajikinsa yana gaya mata kalamai masu daďi da kwantar da zuciyar mai sauraro, (tabbas wataran ya Mahmud zai canja Nurr kodan iya salon soyayyarsa ga 'ya mace).

  Yauda gobe sai ALLAH, har gashi cikin Nurr yashiga wata biyar, ayanzune kuma yakamata tafara zuwa awo, amma ya Mahmud yana fargabar yanda zai kaita aii mata awo dan yasan tabbas zata gane, gashi ďazu Dr Asheer yakirashi yasanar masa ranar monday yakaita asibitin domin awo.....
      Aunty bily ta 'katse masa tunani da ta6ashi abaya, ya ďago idanunsa dasukayi ďanja yana kallonta, tazauna kusadashi sosai yayana miye damuwarka??, yaja numfashi wlhy bily Nurr ce damuwata, Nurr kuma yaya??, miya faru da ita??, a'a babu abinda yafaru da ita akan maganar awone danake gaya miki Dr ya ce, "a kaita ranar monday.
    Yaya ai inaga wanan ba wani abun damuwa bane, bata ba6ace maka tanason shan maganin rage tunbiba??, ya ce, "eh hakane, to kawai kace tashirya kuje za'a duba aga mike damunta inaga hakan zai fiddaka daga ruďani.
    Rungume ta yayi yana bata kisses ako ina najikinta, ina sonki dayawa bily, akwaiki da hikima da dogon tunani wlhy, kema ALLAH yakaimu randa zaki haifamin yara daga wanan cikin, to amin yayana, amma wanda za'a haifama yanzu nawane, dan duk nafiku sonshi, yakuma matseta ajikinsa hakane bilyna, kowama yasan nakine, ko an haifama mallakinkine, haka sukaitayima juna kalamai masu daďi da kwantar da hankali, (nace masoya juna kenan).
    Yau deena tana gidan tazo musu yini, suna ďaki itada Nurr, khalil kuma yanacan aunty bily ta goyashi, Nurr ta ce, "deena gsky inada damuwa.
    Cikin kulwa deena take kallonta 'yar uwa miye damuwarki??, ko yayane??.
   Nurr ta gyara zama, to kusan hakane, deena kalli cikina mana tafaďa tana ďaga riga, deena ta kalli cikin to miya samu cikin naki??, bakiga ya 'kara girmaba, deena tayi murmushi nagani to miye??.
    Yazaki cemin miye?, baki tunanin wata cutarce ta shigeni, yau tsawon wata biyar banida cikakkiyar lafiya, daga inji nan yana ciwo yau sai inji nan yakamu gobe, narasa wannan dalili, saikuma abin mamaki saina farga cikina yana 'kara girma, wanan yasa na sanar da ya mahmud dan ya kaini asibiti adubani amma saiyace tumbine, to alokacin bai kai haka girmaba shiyyasa na yarda dashi, to amma saiya cigaba da girma kuma kullum jikina sake salon ciwo da canji yakeyi, deena miye yake shirin faruwa dani hakane??, ta kare maganar da zubo da hawaye.
    Hannu deena tasa ta share mata hawayen, saida taga ta nutsu sanan ta ce, "Nurr in tambayeki mana?.
   Nurr ta ce, "to ina saurarenki.
  Watanki nawa bakiyi al'adaba??, gaban Nurr yafaďi, itafa bata ta6a yin wanan tunaninba, ta ce, "deena nakai wajen wata biyar fa, deena ta jinjina kai, to amma miyasa baki ta6a tunanin miya hana al'adarki zuwaba??, wlhy deena nima ban saniba, kinsanni da 'kyankyamin jini musamman ma na al'ada, shiyyasa alokacin danaga banayi sainayi matu'kar farinciki, dan ina ganin yanzu nahuta ne kawai.
    Murmushi deena tayi, to Nurr a ilimin da ALLAH yabaki miyake kawo ďaukewar al'ada ga mace matashiya mai kuruciya???.
   Cikin sanyin murya Nurr ta ce, "cikine ko rashin lafiya.
   Masha ALLAHU deena tafaďa, Nurr ina mamaki yanda ciki yana jikinki kika kasa fahimtar hakan, nasan har yanzu kina ďaukar kanki yarinya 'karama, amma atunanina ko yarinyar kauye 'yar shekara goma sha uku akaima aure idan tasamu ciki takan sani, bareke haihuwar birni, kinsamu ilimin boko dana addini iya bakin gwargwado, shekarunki akalla yanzu sunkai sha bakwai zuwa sha takwas, kinada wayewa iya gwargwado, amma har ki gagara gane cewa akwai ciki atareda ke??.
   Wai kekam wace irin kuruciya ce dakene??,.
   Nurr dai tuni ta daskare agurin kamar wadda kankara ta kafe, takasa ďaga koda yatsan hannunta saboda ta'ajibi, to wai ita miyasama bata ta6a irin wanan tunaninbane??, miyasa hankalinta bai ta6a kaiwa wajen bane, tashiga tuno kalaman ya mahmud na lokuta mabanbanta, lallai buri yayi kama da mutum, wanan shine 6oye2 da ake mata agaban Dr kenan??, wasu hawaye suka ziraro akumatunta.
    Deena ta girgiza kai, Nurr atunanina farinciki zakiyi ba kukaba domin abinda yasameki abin farincikine??.
    Bana farin ciki deena dan bana fatan haibuwa da yaya mahmud.
   Cikin mamaki deena take kallonta, kamarya bakison haihuwa dashi??.
   Saboda bana sonsa.
 Lallai Nurr aiiko idan da wanda ya cancanta kiso bai wuce ya mahmud ba, ya mahmud gwarzone acikin maza, babu abinda ALLAH bai bashiba, ilimi tarbiyya son ibada, gashi 'kyakykyawa son kowa kin wanda yarasa, to miye abin'ki gameda ya Mahmud??, aii duk macen data sameshi amatsayin miji tagama nasara, dan namijine tamkar da dubu, acikin maza dubu sai andage ake samun irin ya Mahmud goma, Nurr kidawo cikin hankalinki ki saita tunaninki sosai.
   Karki bari idanunki su rufe har shaiďan yasamu damar kissifa miki wani abu daban da tarbiyyarki, ya Mahmud fa ďan uwankine najini to miye aibunsa??.
     Itadai Nurr batace komaiba sai faman kuka datakeyi, tun deena tana lallashi har abin yafara bata matu'kar haushi, dan ita bataga dalilin yin kuka a wanan maganarba, kinga nikam zan kama gabana indai kukan zakiyi, dan bazan ta6a goya miki bayaba gsky dan haka kinga tafiyata, duk abinda kikaga yadace da rayuwarki kiyi.......shigowar ya Mahmud ce takatsema deena maganarta..................










Luv u oll mu fan's
©2017
[14/03 11:15] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》






NA BILKEESA IBRAHEEM 
   {♡Bilyn Abdul♡}


HIQAYA ONLINE WRITER's
       





52

........Gabaďaya suka ďago suna kallonsa, shima cikin mamaki yake kallon Nurr dake kuka, domin lafiya lau yafita yabarta har yana tsokanarta tana dariya, ya maida kallonsa ga deena dake tsaye fuskarta atamke.
    Deena lafiya dai kuwa??.
Lafiya lau yaya.
  To miyasa Nurr kuka??.
           Tambaya ta tayi nabata amasa, dan kawai nace tanada ciki shine ta zauna tana kuka, cikin 6acin rai deena take maganar.
    Gaban ya Mahmud yafaďi, azuciyarsa ya ce, "deena kin 6aromin aiki, kin ruguza komai, amma afili saiyaja ajiyar zuciya, ya jungina da bango tareda tura hannunsa cikin aljihu, kafafunsa aharďe, idanu kawai ya tsuma Nurr dan baisan mizai cemataba..  
    su duka sunyi shiru sai shashshekar kukan Nurr kawai, ahaka aunty bily tashigo ta samesu, takawo khalil daya farka yana kuka, ďaya bayan ďaya tabi fuskarsu dakallo, ganin kowa fuskarsa da damuwa gakuma Nurr tana kuka sai gabanta yafaďi, ta ce, "yaya lafiya kuwa??.
    Baice komaiba illa tsira mata idanu dayayi, tasan idan ransa ya6aci baya iya magana.
   Ta maida kallonta ga deena, deena mike faruwa??, deena ta gayawa aunty bily abinda yafaru amma banda Nurr batason ya Mahmud, ajiyar zuciya aunty bily ta sauke, ta mi'kama deena khalil kar6eshi kibashi yasha nono, deena ta kar6i khaleel ta zauna.
    Ita kuma aunty bily ta zauna kusada Nurr, fuskarta taďago ta share mata hawayen fuskarta, cikin sigar lallashi take magana, haba Nurr bai kamata dan ance kinda ciki kiyi kukaba, aii abin farincikine wanan bana kukaba, duk macen datayi aure burinta ta samu 'ya'ya domin wanan shine ribar auren.
   Nurr ki tuna akwai ďunbin mutane aduniya dasuke fafutuka da dukiyarsu da jikinsu domin neman haihuwa, wasu a kullum sai sun zubar da hawaye akan damuwar rashin 'ya'ya, miyasa keda ALLAH yabamawa bazaki gode masaba harki nuna ďunbin farin cikinki, azatona kece wadda zata fara taya yaya murnar samun wanan cikin dake jikinki, Nurr kituna sau takwas muna asarar baby nida ya Mahmud, tare akayi bikinmu da ya Fahad amma yazu yaransa biyu tare zaku haifi na uku da ikileema, amma yaya baida ko ďaya, sai yanzu za'a haifa masa ďan fari, kalli kiga deena harta haihu itama, inaga ko waďannan kananun misalan sun isa a tausayama ya Mahmud.
    Cikin jikinki farincikine ga mutane masu yawa, amma dammi zakiyi ba'kin ciki ke kaďai??, plzzz Nurr kibar kuka ki rungumi alkairi da 'kyautar da ALLAH yabaki, ki gode masa kiyi farinciki kuma domin shima babbar godiyane, idan kikayi hakan muma zamuyi farinciki sosai.
     Nurr taja ajiyar zuciya, ALLAH aunty inajin tsoro haihuwa akwai wahala naji anacewa.
    humm Nurr kenan babu wata wahala acikin haihuwa, kuma da ana gudun haihuwa da iyayenmu sunji tsoron haihuwarmu, na haihu naji kuma ni nafaďa miki haihuwa babu wahala, deenace mai wanan maganar.
   Ya Mahmud yana tsaye yana jinsu amma baice musu kalaba.
   Shikenan na ha'kura kuma na kar6i kyautar ALLAH da hannu biyu, nakuma gode masa.
   Ajiyar zuciya ya Mahmud yasaki, zuciyarsa fal farin ciki, baita6a zaton abin zaizo da sauki hakaba, bayi tunani zatayi saurin kar6ar cikin hakaba, Alhmdllh yafaďa ahankali, aunty bilyma cikin farin ciki ta rungumeta, itama deena sai murmushi take danjin daďin 'yar uwarta ta fahimcesu.
   Ahankali ya Mahmud ya'karaso ya tsugunna agabanta yana mai kallon 'kyakykyawar fuskarta, hannunsa ya ďora saman cikinta yana sakin murmushi, babyna ALLAH yakawominkai duniya lafiya, ALLAH yasa kazama mabuďin 'ya'ya masu tarin yawa danake mafarki da fatar samu arayuwata, Nana maryam ngd miki sosai ALLAH yayi miki albarka kinji.
    su aunty bily sukace amin. tashi yayi yazauna kusada ita suka sakata tsakkiya shida aunty bily, sai kalamai masu daďi suke mata da kwantar da hankali.
   Anan deena tawuni sukasha shafta da kara kwantarma da Nurr hankali.

Da daddare tana zaune saman kujerar dake ďakinta ta rabga tagumi saiga ya Mahmud, kwata2 batasan yashigo ďakinba, ya 'karasa kusada ita yazauna, tagumin yacire shima fuskarsa na nuna alamun damuwa, haba Nurrina ki daure ki cirema kanki tunaninnan kinsan ba'a son mai ciki da yawan tunani yana bata matsala sosai plzz ki rage.
    Jikinsa tafaďa ta fashe da kuka, ya rungumeta tsam yana lallashi da bata ha'kurin 6oye matan dasukayi, sunyi hakane badan komaiba saidan ta kwantar da hankalinta, amma tayi musu afuwa.
   Cigaba yayi da lallashinta, ta ce, "amma yaya nidai wlhy inason karatuna, kenan bazan cigaba da karatuba??, haba Nurrina ki ďauka kun koma makaranta keda Deena, haihuwa bata hana karatu saidai maiyi bai shiryaba, namiki al'kawarin kina haihuwa insha ALLAH zaku koma makaranta keda deena.
    Cikin farin ciki ta ce, "da gsk yaya??, murmushi yay mata ya ce, "da gsk Haskena, ta 'kara kankameshi tana murna, yaji daďi sosai shima saiyayi mata 'kya'kykyawar runguma yana tayata murnar, ya ce, "kinga karki matsemin yaro wajen murna, ta ďago tana murmushi yaya ina farin cikine shiyyasa, fuskarta yakama ya haďe bakinta da nasa yana bata sumba mai 'kyau, (tofa abin mamaki) saiga Nurr tana maida murtani, shi kansa ya Mahmud yarikice da faren ciki, wannan yasa ta 'kara masa 'kaimi akan abinda yake har suka kaiga Nasara ( na ce, "humm 'yammata kodai kodai????).
    Yaudai cikin farin ciki sukayi barci, washe gari ya ajiye aikinsa yakaita awo, saida aka gama komai ya maidota gida sanan yatafi office.

Alhmdullah bikin su ya mustapha yatashi, ALLAH kuma yacikama khairat burinta zata auri ya Mustapha, ya mubarak kuma zai auri Rabi'a itama 'yar family ďince, dama sun daďe suna soyayya, to saimuce ALLAH yasanya alkairi.

Zuwa yansu cikin Nurr yashiga wata na takwas, gakuma binkin su ya Mubarak yazo, dan har anfara shagali, Nurr tana samun kulawa wajen ya mahmud da aunty bily, dai dai da wanka oga ya Mahmud ne keyi mata, aunty bilyma bata barinta aikin komai, daga barci sai kallo, saikuma ya mahmud idan yadawo yakama hannunta suyta zagaya gida saboda likita ya ce, "taďan ringa motsa jikinta.
   Babu laifi yanzu ta kwantar da hankalinta, amma har yanzu tana 'ikirarin bata son ya Mahmud, dukda dai bata faďa agabansa saboda tsoron abinda yay mata akwanakin baya saka makon furta bata sonsa datayi.
   Yanzudai cikinne yake bata haushi musamman yanda duk 'kananun kayanta sukaiyi mata kaďan, batada damar saka 'kananun kaya, Saima dogayen riguna nashan iska da ya mahmud yasayo mata, saikuma waďanda aka ďan ďinko mata, lamarin nabata haushi musamman idan zasu anguwa, saidai tasa doguwar riga.
   To yanzu ga biki yazo ankontama sai dogayen riguna akayi mata, dakuma zani da fly.
    Dahakadai aka shiga hidimar biki, yau lunching amma ya Mahmud ya hanata zuwa, tana zaune abakin gadon mama duk haushi ya isheta, mama tashigo, a'a autata lafiya naga ranki a6ace??.
    Ta turo baki gaba, ba yaya bane ya hanani zuwa lunching, ALLAH mama inason zuwa kuma,, mama tazauna kusada ita tana lallashinta, kinga kiyi zamanki ki huta, aii sauki ya nema miki, yanzu kinyi nauyi bako ina yadace kijeba kiyi zamanki kinji, kingama abinda nayi miki yanzu dan nasan kinaso, ta mika mata filet ďin alalan daketa kamshin kifi.
   Cikin farin ciki ta amsa tana murna, tafara ci kenan saiga aunty khadija da ya mahmud.
   Aunty khadija ta ce, "da 'kyau autar mama kina nan ansaki ďaki kinacin abin daďi, babu ruwanki da wata hayaniya, ya mahmud kana ganifa??.
    Ya mahmud ya ce, "aii kedai khadija bari kawai, mu munacan muna shan rana ita tana nan aďaki da kayan daďi mama najidakefa auta, mama dake zaune tayi murmushi to 'yan sa ido ku saurara mata, auta aii yanzu abin tausayice ga kowa, burina kawai naga ta sauka lafiya, Nurr ta ce, "mama sunafa yin kishine aii tuni na ganosu, ya Fahad ne kawai da ďan uwa Saiff basa kishi dani aďakinnan.
   Dariya su ya mahmud suka saka, harda mama datayi murmushi, ya mahmud ya ce, "wato kishi muke dake??.
   , tace emana.
tafaďa tana saka laumar alalarta.
     Aunty khadija ta ce, "tofa kai yaya an harbo jirginmufa, yayi murmushi ya ce, "saimuyi taka tsantsan, suna haďa ido da Nurr ya kanne mata ido ďaya tareda ďaga mata gira.
    Murmushi kawai tayi ta maida kanta 'kasa dan ganin mama tana kallonsu.
                        Da hakadai aka cigaba da hidimar biki, da 'kyar yabarta taje dinar  danma yaga darene kuma tare sukaje, washe gari aka ďaura aure, da daddare aka kai amare ďakunansu.
    To su khairat ALLAH ya sanya alkairi da zaman lafiya, tareda zuri'a ďayyiba.
    Muma ranar bikin Reefat yahya zamu cashe, dan saimun kwashi shoki nida Manshat lol.
    Ameen ya rabbi.....................







Luv u oll my fun's 
©2017
[14/03 13:08] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》










NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡Bilyn Abdul♡}






HIQAYA ONLINE WRITER'S




53

...........Haka Nurr tacigaba da rainon ciki, yayinda ya Mahmud da aunty bily suke bata gudummawa agefe.
     Alhmdllh ciki yashiga watan haihuwa, yanzu Nurr ďin tasake zama 'yar shagwa6a sosai, ga saurin fushi, to dama idan ciki ya tsufa sai ahankali, kusan kullum sai mama ko mami sunzo dubata, idan mama tazo taringa shagwa6a kenan, tace wanan tace wancan, (to kowa yasamu dama ya dama).
   Ya mahmud ko ďakin aunty bily yake to idan dare yay nisa saiya dawo ďakin Nurr ya ida kwana daboda gudun kar haihuwa tazo kwatsan babu kowa akusa, to yanzuma da ake saran yau gobe ko jibi sai kawai aunty bily ta ce, "ta yafe yaringa kwana ďakin Nurr ďin har ALLAH ya sauke ta lafiya, yaji daďi sosai har yasaka mata albarka.
   Nurr dake zaune tana jinsu saitaji ta 'kara kaunar aunty bily, tana addu'ar ALLAH yabata ikon 'kyautata mata kamar yanda itama take mata batareda 'kyashiba, har zuciyarta tana 'kyaunar aunty bily da halayenta, har wataran tana sha'awar koyan halin hakuri da kawaici irin na aunty bily, taja ajiyar zuciya danjin anta6ata.
   Aunty bily tayimata murmushi Nurr ďin mama arage dogon tunani kinji??, murmushi Nurr tayi tareda jin jina kai, ya mahmud yabi matan nasa da kallo cikin sha'awa da kara kaunarsu.
   wasu na gudun haďa mata biyu amma shi yaga fa'idar haďa mata biyu, har yakanji yafi kowa sa'a arayuwa, yana fatan ALLAH yabashi ikon cigaba dayin adalci arayuwarsu baki ďaya, ALLAH yacigaba da haďe masa kansu har 'karshen numfashinsu.


                   .☆♡☆.
Yaudai kam tun rana Nurr batajin daďin jikinta, dauriya kawai take, aunty bily taso taďan fahimci hakan, amma da Nurr tafarga aunty bily tana kallonta saitayi murmushi ta basar kawai.
    Aunty bily ta ce, "Nurr kamar bakida lafiya??, Nurr tayi murmushin ya'ke aunty mikika ganine??, lafiyata kalau kawaidai kinsan yauda gobe, gakuma cikinnan ya isheni.
   'Yar dariya aunty bily tayi karki damu muma mun 'kagara ki juyo mana babyn mu, murmushi kawai Nurr tayi dan tanama aunty bily kawaici, suna nan suna 'yar hira lokaci2 Nurr takan ďan cije le6enta, amma bata bari aunty bily tagani.
   Ya mahmud yaturo 'kofar yashigo da sallama, suka amsa su duka, cikin fara'a aunty bily ta tarbeshi, ya mi'ka mata jakkar aikinsa, tareda sumbatar kumatunta, ya ce, "ya gidan?.
   Ga shinan lfy my handsome, masha ALLAH yafaďa yana lumshe idanu, aunty bily tawuce ďakinsa domin kai masa jakkar, yatako ahankali inda Nurr ke zaune, tunda tai masa kallo ďaya bayan shigowarsa ta ďauke kai, tanadai jin maganarsu da aunty bily, durkusawa yayi akasa tareda sumbatar cikinta, ta rintse idanunta saboda haushi, my baby ina fata kana cikin 'koshin lafiya??, Nurr dai tana jinsa amma bata tanka masaba, ya ďago yana kallonta Nurrina ko sannu da zuwa babu??, taďan ta6e baki toni sannun mi zan maka bayan ďankane agabanka.
    Da sauri ya 'mi'ke yakoma kan hannun kujera yana murmushi, ni na isa my Nurri, ya sumbaci kumatunta ina fata kina lafiya??, 'yar harara tayi masa, sai yanzu kayi tunanin ina lafiya??, o, sorry gimbiya amin afuwa, batace komaiba.
    Aunty bily ta sakko ta kawo masa ruwa yasha sanan yay hamdala, yamike daga kusada Nurr kunga bari naje na watsa ruwa ko?, to yaya! aunty bily tafaďa, samansa ya nufa, yay taku ďaya zuwa biyu saiya juyo, Nurr yakama tana kallonsa, da sauri ta kauda kai daga kallonsa, yay ďan murmushi sanan yacigaba da tafiya.
    Har zuwa dare Nurr tana jinta ba daidaiba, ga wani abu yana ta zuba daga jikinta, tsoro yafara kamata, kodai tafaďawa aunty bily ne??, kai bari dai ta'kara daurewa kilama irin ciwon datakejine kullum, tana zaune tanata sake2 saitaji cikinta yajuya kamar an birkita abunda ke cikinta, ya salam tafaďa murya aďashe, tareda kan kame filon kujera, zuwa wani ďan lokaci saiya lafa.
   Ya mahmud yashigo sanye da kayan barci, yaďan bita da kallo dan ganin kamar tana cikin wani hali, Nurri na lafiya kuwa??, ta huro hanci dan har yanzu yana ďan murďa mata kaďan2, kafin tabashi amsa an sake wuntsilawa, ta ce, "inna lillah wa inna ilairraji'u"". 
    Da sauri ya Mahmud yari'keta dan tana shirin faďowa 'kasane, tofa daga nan tafara murkusu2 ajikinsa da kiran yaya ka taimakeni zan mutu, tuni ya ruďe ya sa6eta gaba ďaya yafice, afalo yashiga kwalama aunty bily kira, atsorace tafito itama tana tambayar lafiya kuwa??, ďakko makullin mota bilkeesu Nurr babu lafiya.......ai kafin ya 'karasa faďa takai karshen benen sa, babu daďewa tafito ta shiga ďakinta zumbulelen hijjab tasako akan kayan barcin jikinta, a harabar gidan ta iske su ya mahmud yana ri'ke da Nurr daketa kiran sunan ALLAH, babu 6ata lokaci ya mahmud yashiga baya aunty bily taja motar suka fice daga gidan aguje.
    Asibitin Dr Asheer suka nufa, aiko cikin gaggawa aka amshesu, aka kai Nurr ďakin haihuwa, ya mahmud ma ya danna kai, Dr Asheer ya ce, "Sardauna kayi ha'kuri kajiramu a waje.
   Sorry Dr bazan iyaba wlhy, ka barni kawai, babu yanda Dr ya iya dole yabar ya mahmud, yaje ya rungume Nurr daketa faman kuka da ambatar duk addu'ar datazo bakinta, shima cigaba da taimaka mata da add'ar yayi idanunsa sunyi jajur saboda tashin hankali, gani yake kamar Nurrinsa zata mutune.
    Haka Nurr taci gaba da Na'kuda abin tausayi, cikin amincin "UBANGIJI" ta sallu6o 'katuwar 'yarta mace, mai kama da ita sak, abin sai wanda yagani masha ALLAH, tuni murna ta lilli6e ya Mahmud, acikin jinin yasunkuci 'yarsa yarungume, Dr Asheer ya ce, "wow!! Sardauna, ka 6ata jikinka aii, karka damu doctor ina cikin farin ciki yau, da'kyar ya lalla6ashi ya kar6i baby ana gyarata, dama tuni an ďauke Nurr, fitowa yayi danya kawoma aunty bily albishir sai yatarar dasu mama ma sunzo, cikin zumuďi suke tambayarsa lafiya?? dan ganin jini ajikinsa.
    Ya washe baki yana faďin Alhmdllh ta haihu, gaba ďaya suka kaure da faďin alhmdllh!!!, saikuma ga dector yafito dawani sabon albishir Nurr tasake haihuwar Namiji, wayyo daďi aii sai Murna ta 'kara karfi, cikin minti talatin aka gama gyara mai jego da jarirai, Allurar barci akayima Nurr danta samu hutu, aka kaita ďakin hutu.
   Yaran kuma akace su shigo su gansu, masha ALLAH kowa ke faďa dan yaran masha ALLAHU sunyi ruwa biyune, sun ďebo mamarsu da babansu.
   Cikin kankanin lokaci labari yacika family ďin cewa Nurr ta haihu, ALLAH sarki kowa murna yake dafaďin ALLAH yajikan mahaifiyarta inama tanan, wanan abin farinciki ya faru??.
      Humm ya Mahmud kam ai yafi kowa murna da farinciki awanan rana, jiyake kamar yafi kowa sa'a awajen ALLAH, Nurr dai tanata barci batasan halin da'ake cikiba, sai washe gari tafarka da safe.
     aunty bilky tana zaune itada mama, yaran suna hannunsu, annaďesu cikin pink ďin kayan sanyi sai tashin 'kamshi suke, ya mahmud ya'karasa kusada ita da sauri yana faďin Nurri kin tashi, kai kawai ta ďaga masa batareda tayi maganaba.
   Masha ALLAH yafaďa yana murmushi, zaki iya tashine ???, nanma kai ta jinjina masa, su mama suka shiga yimata sannu bayan ta tashi zaune, bari nakira Dr ya mahmud yafaďa yana fita, babu daďewa suka dawo shida likita, cikin farin ciki likita ya ce, "kai masha ALLAH ai komai Normal inagama zaku iya tafiya da ita gida acigaba dabata kulawa, Amma gobe idan ALLAH ya kaimu akawo yaran dansu amshi allura.
   Babu damuwa Dr mungode sosai, sukayi musbaha da ya Mahmud, Sardauna ina maka murna sosai ALLAH yaraya mana manyan gobe.
   Amin doctor nima ngd sosai ALLAH yabar zuminci, amin doctor Ashir yafaďa shida su mama.
   Nanfa suka shiga shirin tafiya gida, kai tsaye gidan ya Mahmud aka wuce da ita, saidai tuni fuskar Nurr ta canja launi dan ita a tunaninta gidan dady za'a tafi da ita, amma saitaga sa6anin haka, mama tana lura da ita dan haka tayi murmushi kawai, dan tasan halin autar tata da son gida.
    Suna zuwa ruwan wanka aka ďora mama dakanta tayima Nurr wanka, tanata zille2 da faďin zafi, mama ta ce, "haka zaki daure dan idan ba ayimiki wanan wankanba aisai asamu matsala, ana gamawa mama tabarota danta karasa kimtsa jikinta, jariraima an sallesu tareda saka musu kayan sanyi farare masu taushi da laushi, Nurr ma tafito ta shirya cikin sabuwar atamfa siket da riga.
   Aunty bily takawo mata shayi mai kauri da dađi, saikuma farfesun namankai, da gasassar kaza datasha kayan haďi, dakuma dankali soyayye.
    Humm saidaifa nakula mutuniyarku har yanzu banga ta kula jariranba, kokuwa har yanzu tana cikin magagin haihuwar ne??, to baradai muga ikon ALLAH.
    saida mama ta tsareta sanan taci abincin sosai amma da sai wani tsantseni takeyi, bayan tacika tunbinta mama ta ce, "suma yara sai abasu nasu abincin, Nurr tarage fara'a wayyo mama nikam gsky.........mama ta katseta dafaďin ban gane ke gsky ba??, maza ďaukarsu kibasu abincinsu banason shashancin, mama ta ďora mata baby'girl ďin akan cinya, oya fiddo kibasu.
    Babu yanda Nurr zatayi dole tayi yanda mama takeso, saidai tana kamawa tai saurin cirewa wai zafi, mama ta ce, "eh ahakan zaki basu, zafi kam aii dolene tunda yaune na farko.
    Ta 'kara daurewa tasaka mata, data kama saita janye tana faďin wash ALLAH mama zafi wlhy......ahaka ya mahmud yashigo ya samesu, zama yayi yana kallonsu kawai cike da sha'awa, mama dataga Nurr tana 6ata mata lokaci dan sai wani no'ke2 take.
   Sai kaiwai ta dam'ki nonon tasakama yarinyar, caraf kuwa takama tafara sha, Nurr tashiga yarfa hannu da faďin wayyo mama dan ALLAH abarshi haka plzzz. 
    Ina mama ta'ki saurarenta, itako baby babu ruwanta tunbinta take cikawa, tuni dariya ta zoma ya Mahmud dan ganin yanda Nurr take yarfe hannu, yasa hannu yatoshe bakin dan kar dariyar tafito, amma ina tuni Nurr ta gansa, ta fashe da kuka bayan mama tacire yarinyar ta ďakko baby'boy ďin, mama kinga yaya ko yana min dariya, cikin hawaye tafaďa.
    Mama ta harari Ya Mahmud kaikuma sannunka, to miye na dariyar anan, yacire hannun yanaďan haďe fuska shi adole zai kame kansa, mama nifa ba dariya nake mataba kawaidai ta tsargune, mama ta girgiza kai tareda sakama yaron nono abaki, ya mahmud yafaki idon mama yay mata Nurr gwalo......mama wlhy yanamin gwalo.
    Kai tashi kafita daga ďakinnan, mama yafaďa cikin faďa.
   Ya mahmud yami'ke yana kunshe dariya, saida yazo bakin kofar fita sanan yay mata gwalo yafice.
     (kai ALLAH ya shirya masu karatu)..................






Luv u oll my fun's 
©2017
[14/03 15:38] bilyn Abdul:
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *