check your best novels here

Monday 20 March 2017

SABON AL'AMAREE 55/56

[15/03 16:36] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》








NA BILKEESA IBRAHEEM 
    {♡Bilyn Abdul♡}





HIQAYA ONLINE WRITER'S
https://mrsbilkisa.blogspot.com





55

..........Babu daďewa saiga ya mahmud da Dr Asheer, da sauri ya Mahmud ya'karaso gaban gado dan ganin waleed na niyyar faďowa, ya tareshi yana faďin wanan wane irin gangacine zaku ajiye min yaro kan gado, idan yafaďo yaji ciwofa??, jin masifa sama2 ya sa Nurr fitowa daga bayi, dan aunty bily barci ya ďauketa.
    Nurr ta ce, "baccifa yakeyi saidai idan yanzu yafarka".
      daga yau idan kunsan ba'a cikin ďaki kukeba ku daina kwantar dasu su kaďai, tunda zasu iya tashi harma suyi kokarin sakkowa, yanzu daban zoba saiya faďo awajenan ya fasa kai.
    To kayi ha'kuri baza'a sakeba insha ALLAH, yanzu ina doctor ďin??, yana falo bari nace yashigo tunda barci takeyi, Shiru tayi masa, yana fita ta ce, "masifaffe tunda bamuda aikinyi saimu zauna gadin 'ya'yanka.........sallamarsu tasata yin shiru, waleed yana hannun Dr, Nurr ta gaisheshi, ya amasa da tambayar yamai jiki??, da sau'ki tafaďa tana saka hijjab ďin aunty bily dan kayan jikinta 'kananane.
    Ya Mahmud ya zauna yatada aunty bily, ya ďagota zuwa jikinsa sannu bily kinji, ya jikin??, tayi ďan murmushi da sauki yaya, to ga Dr nan zai dubaki dan yasan maganin dazai baki, ta jinjina kai tana gyara zama, Dr Asheer yami'kama ya Mahmud waleed datun ďazu yake zille2n son zuwa wajensa saboda 'kiywa, yana kar6arsa ya kankame aunty bily dake kusada ya Mahmud, ta shafa kansa, ya Mahmud yaďageshi sama yana faďin Waleeden abba yau mom babu lafiya barta ta huta.
     Gwajin farko ya nuna aunty bily tanada shigar ciki na wata biyu, wayyo murna, Nurr kamar itace akace tanada cikin, to balle uban gayya ya Mahmud, aunty bily kam zuciyarta cike da fargaba, tana tsoron abinda yafaru baya karya sake faruwa a yanzu, amma tana addu'ar kar hakan ta faru.
   Dr Ashir yasaka mata 'karin ruwa sanan yatafi.
     ganin tayi barci ya mahmud ya ce, "Nurrina bari naje office tunda tasamu barci, akwai ba'ki damuke jiran zuwansu.
    To ALLAH ya kiyaye hanya, cikin jin daďi ya ce, "amin haskena, yana mamakin canjawar wasu dayawan haleyen Nurr, shin dama idan mutum ya haihu saiya 'kara hankali??, to shidai koma ba haka bane yaga fa'idar haihuwar Nurr, dan haihuwa ta canjata 60% daga shirme koyace kuruciyarta.
     Ya sumbaci kumatunta dana waleed dake wasa a 'kasa, yana kaiwa kofa waleed yasaka kuka, ya Mahmud yadawo yana dariya tokai Alhajina office fa zan koma yaza'ayi kenan??.
    Kayi tafiyarka kawai idan yagaji aii zaiyi shiru, yaďan harareta kina nufin natafi nabar yarona yana kuka, har kukan yaja masa zazza6i, ganin kallon dayake mata ta ce, "ALLAH yabaka ha'kuri, shiru yay mata yamaida kallonsa ga waleed daya wani kankamesa sosai dan kar atafi abarsa, yayma yaron kiss a kai, su waleedi manya, wato kai nan duk wayone karna tafi nabarka ko??, shine kayi mini wanan ri'kon haka??, kamar waleed yasan abinda Abban nasa yake faďa saiya ďago yana 'yar dariya, shima ya Mahmud dariyar yayi.
   Komawa yayi kusada Nurr ya zauna, ko kallonsu batayi ba, ya ďora mata waleed akan cinyarta, Haskena dan ALLAH kimasa wayo nagudu mana, itama ďaukar waleed ďin tayi tamaida masa akan cinya, toni miye nawa, can ta matse muku, ka ďaukeshi kutafi kawai, dan karkabarsa yay kuka har ciwon kai ya kamashi.
   Ya Mahmud yay murmushi to yi hakuri ALLAH inada ba'ki a office kar Fahad yayta jirana, Nurr tayi murmushi a'a kutafi tare mana, ya rungumota ajikinsa itada waleed cikin kunnanta yagaya mata wata magana, da sauri ta ce, "banyarda ba, sai anjima katafi kawai na yarda, Mi'kewa ya mahmud yayi yatashi tsaye yana shafa kan waleed, ya'karasa inda aunty bily da waleeda suke barci ya sumbaci kumatunsu sanan yafaki idon waleedi yafita da gudu, tuni Nurr ta tuntsire da dariya, waleed kuma yafara kuka daya waiga yaga abbansa bayanan.
    Wasa tafara masa saikuma yafara dariya, dahakadai ta hanasa kukan.
      Alhmdllh aunty bily tasamu sau'ki dama ita cikinta bai cika bata wahala ba sosai, saidai kasala da abunda ba'a rasaba, tom yanzu dai dukkan aikin gidan yadawo kan Nurr, komai itace dan ta saukema aunty bily komai, mijinma kusan yanzu ahannunta yake, shiyyasa yake shanawa yanda yakeso, to itama dai takan bada haďin kai dan gwaskan nata gwanine a6angaren sosayyay, ana cikin haka yakawo mata albishir ďin samun makaranta itada deena, sun samu Admission a (B.U.K).
   Wow!!! Zokaga murna wajen Nurr, dan danan takira deena ta guntsa mata suka kaure da murna acikin waya, ya mahmud yana zaune yana kallon ikon ALLAH, ya rikota zuwa jikinsa to Nurrina miye tukuycina??.
    Tasakar masa murmushin da har kumatunta ya lotsa, yaya mikakeso amtsayin tukyci??, ya tsirama kwayar idanunta ido, sunkai minti kamar biyar ahaka suna kallon juna ido cikin ido, yauce rana ta farko da Nurr ta ta6a tsayawa suka kalli juna ido cikin ido itada ya mahmud, wasu abubuwa taga suna fitowa daga idanunsa zuwa nata, yakama hannunta ya rumtse anasa, tasaki wata sassanyar ajiyar zuciya, ahankali ya Mahmud ya ce, "i luv u so very much my Nurri, ina sonki dayawa harma nakan kasa control ďin kaina asonki, Haskena yaushene zaki soni??, yaushene zaki kar6eni amatsayin mijinki???.......cikin raunin murya yake maganar.
     Yabama Nurr tausayi kwarai da gsk, dazata iya yimasa 'karya to da saitace tana sonsa, amma bazata iyaba dan bata iya karyaba bare yaudara, dan haka taja numfashi, azatonsa itama zatace tana sonsane, amma saiyaji ta ce, "yaya mubar zancenan kawai plzzz.
   Idanu ya kafeta dasu cikin damuwa, ahankali ya zare hannunsa daga nata, yazame yakwanta sosai asaman gadon, waleeda yajawo yarungume ajikinsa yana shafa kanta ahankali, yarinyar gaba ďaya takoma kamanin Nurr, yaďan tsura mata idanu dan yana 'kyaunar yaransa sosai, harma baisan adadain yawan kaunar dayake musuba, ya lumshe idanunsa sosai.
    Nurr ma idanu ta tsura musu dagashi har ďiyar tasa, tabass abubuwa dayawa suna tsunkulinta azuciya gameda ya Mahmud amma itafa har yanzu basanshi takeyiba, takuma rasa hanyar dazatabi domin su rabu, tashi tayi tashiga bayi tayo wanka domin yin shirin barci, hartagama shirinta ya Mahmud yana nan kwance a inda ta barsa.
    Ta hawo gadon ta kwanta itama, yana jinta amma ya shareta, jitayi kuma babu daďi, domin yasabar mata duk dare ajikinsa take barci, amma yau yayi canjinta da Waleeda, kuma waleeda wajen aunty bily suke kwana, yanzuma daga can ya ďakkota dan tuni waleed yayi barci acan.
    Haka tayita juye2 dan barci ya'ki ďaukarta kwata2, shima yakasa barcin saboda damuwa, yayi shirune kawai dan bayaso tagane idonsa biyu, duk juye2n datakeyi akan kunnrnsa takeyinsu yana jinta sarai yakuma san abinda ya hanata barcin, shima kuma shine ya hanashi barcin amma zai daure kodan yafara maganin Nurr ďin.
   Yaudai haka akayi wannan kwanciyar kowa zuciyarsa babu daďi, itama aunty bily tayi mamakin rashin dawo da wakeeda ďakinta, amma bata kawo komai a rantaba ta rungume waleed sukayi barcinsu mai daďi.
      Da safe Nurr ta tashi dawani ciwonkai saboda rashin isashshen barci, gakuma tun shekaranjiya batajin daďin jikinta dama.
   Da yake yau weekend babu inda ya mahmud yake zuwa, haka ta daure tashiga kichin shikuma yakoma barci, dan yana bu'katar barcin shima tunda baiyi isashsheba adaren jiya.
      Tagama haďa break da taimakon 'yan aiki, suka gyara gidan tsaf, tacika ko ina da kamshi, suna cikin gyaran waleed yafito dan yanzu sun fara tafiya, ta ďaukeshi tana murmushi damasa kiss akumatu, yaron mom tashi kayi kabar mom ďin??, bari to namaka wanka kafin waleeda ta tashi, tasan yanzu idan taje ďakinta dashi saiya tada su yaya da waleeda, dan haka sai kawai tanufi saman ya mahmud, acan tayi masa wankan ta gyara shi tsaf, saita dawo ďakin aunty bily danta saka masa kaya, dan kayansu suna ďakin aunty bily, sun tararma aunty bilyn ta tashi, Nurr ta ce, "aunty kintashi??.
   Wlhy yanzu na tashi nafara jajen waleed ma kuka shigo, Nurr ta mi'ka mata waleed tana faďin fita yayi bayan yatashi, gashinanma namasa wanka, to mungode Ummi.
     Nurr tafito tana dariya, zuwa tayi ta iske ya mahmud yayima waleeda wanka itama, yanata 'ko'karin saka mata fanfas ta'ki tsayawa, sun bata dariya dan haka taďan murmusa, ta karasa inda suke yaya Ina kwana??, lafiya yafaďa ata'kaice, ta daure ta ce, "kakawota nasaka mata to, ďaukar waleeda yayi yana faďin barshi bari na kaiwa My bily ta saka mata.
     Jiki a sanyaye tabishi da kallo, bataso taga ana fushi da ita ko yaya ne wlhy, jiki babu kwari tagyara ďakinta tayi wanka itama, a dinning ta iskesu har sun fara break basu jirataba, ta zauna tana satar kallon fuskar ya mahmud.
     Fuskarshi aďan hađe take, kuma babu walwala atare dashi, to amma sanda take tahowa aitaji suna dariya shida aunty bily  saida tazo ya canja fuska, abincinta tahaďa tanaci badan daďiba, sukuma sunaci suna bama yaran, aunty bily taďan so fahimtar wani abu atsakaninsu to amma tunda basu gaya mataba itama bazata tambayaba.
    Gaba ďaya yau haka ya mahmud ya wuni yana fushi da Nurr, to itamabata cika walwalaba saboda ciwon kan dake damunta tun dare.

Rayuwa tana tafiya yanda yakamata, Nurr sun fara zuwa makaranta itada deena, aunty bily tana rainon cikinta cikin addu'a da fatan ALLAH yasa ta sauka lafiya, yanzu haka cikinta yakai wata na biyar zuwa shidda, Nurr ta yaye su Waleed jiya dan haka mama tazo ta ďaukesu yau da safe ta tafi dasu wajenta itace zata yayesu, sai sukaji gidan shiru babu daďi saboda babu iyayen 'kiriniya, zuwa yanzu ya mahmud yadaina fushi da Nurr amma ba sosai yake shiga harkartaba, kwata2 batajin daďin hakan dayake mata, tarasa yanda zatayi tashawo kansa sukoma kamar da.
   Ita kuma batason gayama aunty bily matsalarta domin wannan sirrintane tsakaninta da mijinta.
    Deenama tana yawan tambayarta saboda rashin walwala datake gani atare da ita, amma Nurr ďin tadage akan babu komai, 'kila wannan yayen ne datayi.
    Deena ta ce, "babu wani yaye, abinda yaran ma bawata shakuwa kukayiba, yanda suka shaku da aunty bily ma aibasu shaku dakeba, kina ganin jiya damukaje gidan kodamuwa basuyiba dazamu taho, amma mama ta ce, "da aunty billy tazo saida wayo tabar gidan, hakama ya mahmud idan yazo gaidasu da dabara yake fita.
    Nurr tayi murmushi to aii sune iyayensu ni miye nawa aciki,, deena ta ce, "aii shiyyasa nace miki bahakan bane yake damunki akwaidai abinda ke damunki bakison faďane kawai.
    Nurr ta ce, "kinga uwar biyu abar maganar wataran zan faďa miki amma bawata damuwa bace, yanzudai mutafi gida tunda bamuda wasu lectures a gaba,  wlhy nagaji.....
   To shikenan, amma kema kina hanyar zama wata uwar biyun kwanan nan, Nurr ta ce, "tab rufani ki sayani, nikam yanzu aii bana fatan ciki, kudai kuyita ja, nasan kila kusan tare zaki haihu da aunty bily.
    Gsky kam inaga kusan tare zamu haihu, mota suka shiga direba yajasu sai gida..............








Luv u oll my fan's
©2017
[15/03 18:49] bilyn Abdul: 《《SABON AL'AMAREE》》









NA BILKEESA IBRAHEEM 
     {♡Bilyn Abdul♡}







HIQAYA ONLINE WRITER'S
https://mrsbilkisa.blogspot.com 



56

..........'Yan kwana kinnan Nurr batajin daďin jikinta, tana daurewane kawai saboda bazai yuwu ita kwance aunty bily kwanceba, damma su waleed suna wajen mama ayuka sun mata sau'ki, tana yawan yin ciwon kai, ga aikin gida ga makaranta, lamarin sai addu'a.
    Haka tadawo daga school yau agajiye, tazube saman kujera tana fidda numfashi, aunty bily tayi dariya 'yan makaranta sannunku.
   Yauwa auntyna ykk?, yazama da tashi?, tasake yin murmushi, gamunan munayi, kasa tashi tayi sai marka ta kwalama kira takawo mata ruwa, harda abinci, Nurr ta kalleta cikin mamaki marka waya girka abinci kuma??.
   Hajiyace tayi".
  Cikin mamaki Nurr take kallon aunty bily, kai aunty dan ALLAH kibar wahalar da kanki da babynmu, ALLAH banason naga kina aikinnan, shiyyasa naketa hanzarin dawowa gida.
   To autar mama aii yakamata naďan ringa motsa jikina ko??, zaman isata yakeyi, gashi mama taki dawo mana dasu waleedi gidan shiru babu daďi, sai idan su Abdul sun dawo makaranta sun shigo.
     Ayya my aunty wlhy nima idan natafi makaranta kina raina nasan kaďaici yana miki yawa, idan yaya ya dawo kice yadawo miki dasu mana,, aikuwa za'akai ga hakan Nurr baridai yadawo.
   Nurr tanacin abinci suna 'yar hirarsu, har tagama tashiga ďaki ta watsa ruwa, sanan tadawo.
   Aunty bily anya kuwa yau yaya zai dawo daga abujar nan??, naga har biyar ta gotafa??, wlhy nima abinda nake tunani kenan Nurr, nakira wayarsa kuma yaki ya ďaga, inaga suna mitinne.
   Nurr ta ce, "to ALLAH yasa lafiya dai, amin ya rabbi........maganar Nurr ta kakare saboda turo kofar ya mahmud, gaba ďaya suka maida kansu inda yake yatsaya bakin kofa yana kallonsu ďaya bayan ďaya fuskarsa cike da murmushi, aunty bily tace oyoyo Abban 2, yay sama da kai, babu wani oyoyo, dan ba'a tareniba hakan ya nuna ba'a murna da dawowata kenan??.
    Dariya aunty bily tayi, nidai amin afuwa tashi wahala yakemin, to 'yar uwar ďayarfa??, Nurr kenan yake nufi, Nurr tai kasa da kai tana murmushi, aunty bily ta ce, "auta atashi to.
     Kai aunty dan ALLAH kibarsa nifa bazan iyaba, ya ce, "lallai ashe yau zan kwana nan kenan, Nurr taďan zaro ido kai haba??, oh kin ďauka wasanake yi kenan??, to zauna kigani, Nurr tami'ke tsaye A'a aiba ayi hakaba dadai badaga tafiya kakeba dasai abarka ka kwana, takarasa tana kar6ar jakar hannunsa, haďata yayi itada jakar yarungume tareda bata sumba akumatu, itadai kunyar aunty bily takeji shiyyasa taketa zille2.
    Yasaketa ya'karaso ga aunty b, itama zama yay ya rungume ta yana shafa cikinta, my baby kana lafiya??, ta sumbaci kumatunsa yana lafiya my handsome saidai yana kewar yayyensa da Abbansa.
    to gani nadawo, suma yayunsa yau zasu dawo gareshi, lah yaya da gsk??, insha ALLAHU yafaďa yana shafa kumatunta, amma yaya shine ba'a faďa manaba mushirya tarbarsu, yami'ke yana dariya oh kumfi ďokin dawowar yaranku akan Abbansu ko??, haba mu mun isa, munyi missing nasune dai.
   Samansa ya haye yana faďin nima nayi missing nasu, acan yatarar da Nurr tagama haďa masa ruwan wanka, yariko hannunta suka koma ciki dan tana niyyar fitane, 'yammata aibakida damar fita.
    Yaya zan kawo maka ruwan shanefa, no karki damu yanzu nasha ruwa amota, wanka nake bu'kata amin dai dan nagaji wlhy.
      Tab yaya kaima kasan babu 'yar haka tsakanina dakai, ALLAH bazan iyaba, ya rungumeta sosai ajikinsa, yakamata mubar wannan 'yar kunyar, dan yanzu babu maganar kunya a tsakaninmu, karki manta harfa kin haifa mini yara, ta rintse idonta dan ita bawai wankanne bazata iya yimasaba, kawaidai bata sonsane, ya sumbaci ďan bakinta, ki za6a wanka ko wani abu daban, dolene amin ďaya aciki, da sauri tabuďe ido tana kallonsa, miye ďayan??, da hannu ya nuna mata gado, ta waro idanu, shima saiya waro nasa, sai suka tuntaure da dariya, da wayau yasata tamasa wankan, yana fitowa yashirya cikin doguwar riga yafice masallaci domin yin sallar magriba.
   Itama sakkowa tayi tashirya abinci a dinning sanan tatafi ďaki, tana zaune kwatsam wani tunani yazo zuciyarta, shine rashin ganin al'adarta, idan bata manta lissafinba yau wata kwanansa goma sha uku da tsayawa, kuma tanayin al'adarta a farkon watane, dan danan tsoro ya kamata hankalinta yatashi sosai, tafara safa da marwa aďakinta, bataso abinda take tunani yazama gsky wato ciki, ta maimaita sunan ciki!!!! Kuma??, kai dasake wai abama mai kaza kai.
    Ya mahmud yashigo ďakinta dan yunwa yakeji, ganinta a birkice yasakashi tsayawa kallonta, itama da sauri taďago tana kallonsa, Nurri lafiya kuwa??, ta ďan dafe kai inafa lafiya yaya, dan ALLAH idan bazaka damuba inason magana da doctor Asheer.
    Ya sauke numfashi tareda 'karasawa inda take, miyasa kikeson yin magana dashi??, taďan tsaya daga yawon datakeyi, ta cije ďan yatsanta, ina cikin damuwane yaya bana fatan abinda nake zargi yakasance akan yawan ciwon danakeyi 'yan kwanakinnan.
     Ta 'kara sakashi aduhu, dan haka ya ce, "kinga nutsu kimin bayani yanda zan fahimta, yaru'ko hannunta suka zauna.
    Ina saurarenki,,".
    wato dama ina tunanine akan al'adata sainaga har na shige lokacin danakeyi da kwana goma sha uku, shine hankalina yatashi.
   To kinga kwantar da hankalinki bari na kira doctor muji mizaice, waya ya ďauka yakira Dr Asheer, bayan sun gaisa ya ce, "doctor dan ALLAH inason na tambayekane??, okey Sardauna ina saurarenka.
   Wato matanane lokacin al'adanta yashige saita tada hankalinta da tunanin kowani ciwone??, kuma a 'yan kwanakinnan takanji canji ajikinta, komiye dalilin hakan??.
   'Yar dariya Dr Yayi, Sardauna to anawa tunani matarka tanada ciki kenan inhar hasashena yayi dai2, da sauri ya ce, wow!! Dr da gsk??, insha ALLAHU hakane Sardauna, babu wani ciwo dake damunta saina laulayi, amma kaima yakamata ka shaida hakan, dan zakaji ta canja maka, lallaikam doctor ammafa ngd da wanan albishir saika jini da safe dan kawo maka goro.
    Nurr tanajinsu dan haka tuni tayi mutuwar zaune, sai hawaye daketa zirara a idanunta.
   Ya Mahmud yayma Doctor sallama ya kashe wayar,, cikin farin ciki yajuyo ga Nurr, amma saiyayi turus dan ganin tana kuka, Nurr kibar kuka babu cutar datake damunki, sai abin farinciki daya samemu.
   Da sauri ta ce, "kokuma bin ba'kin ciki ko??, yaya dankaga nasaki jiki na haifi su waleeda shiyyasa kake tunanin zan cigaba da haihuwa dakai??, kayi kuskure daka cigaba da wannan tunanin,, ka ďauka baka samu wanan cikinba dan zubar dashi zanyi.
    Tami'ke da sauri domin barin wajen, damke hannunta yayi da 'karfi, yay matu'kar canja fuska cikin matu'kar 6acin rai ya nunata da ďayan hannunsa "k walhy kishiga hankalinki, koda wasa kikayi kuskuren zubar min da ciki saikin fiskanci fushina, ''k wai wacce irin mutumce ne!!!??, wlhy Nurr wanan shine zai zama mafi girman kuskure dazakiyi arayuwarki, bazan hanakiba ga fili gamai doki, kije kizuba mara mutunci kawai!!!!, afusace ya mi'ke yabar ďakin.
    Zubewa Nurr tayi akasa tana kuku kamar ranta zai fita, ya Mahmud kuwa koda yafita saiya nufi gidan daddy, baishiga ďakin kowaba yawuce saman dady, dady suna tareda mama danyau aikintane, yashigo falon kamar mai shirin yaki sai huci yake da hura hanci, mama da dady suka bishi da kallo, da sauri waleeda dake zaune kan cinyar dady tazo ta tareshi, yarike hannunta kawai yau babu zancen ďagasu sama kamar yanda ya saba, dady ya ce, "mahmud lafiya kuwa??.
   Dady da sau'ki dai kawai, yafaďa yana zama..   .
     to mikuma yafaru??, kaidawa??,.
    Nida Nurr ne.
Nurr kuma??, miya haďaku, zayyanema su daddy komai yayi batareda yarage komaiba har kiran doctor, da i'kirarin Nurr na zubar da ciki, suma hankalinsu yatashi kwarai da gsk, dady ya ďauki waya yakira Nurr.
   Tana zaune inda ya Mahmud yabarta tana rabzar kuka, sai wayarta tafara wringing da kamar bazata ďagaba saikuma taga sunan daddy, tabbas tasan ya Mahmud yaje gida, tabďi tafaďa tana gyara zama, to aii ita a wanan karon tayi shirin komima zai faru ya faru, dan haka zata gayama su dady gskyar abinda ke ranta gameda zama da Ya Mahmud, wayar ta katse aka sake kira, ta ďaga batareda wani shayiba.
     Nurr kizo gida yanzu inason ganinki, bai jira amsartaba ya kashe, itama mi'kewa tayi ta zira hijjab tafice, ko aunty b batayima sallamaba.
    Afalon dady ta iskesu dan haka tarissina ta gaishesu, waleeda tana jikin ya Mahmud amma koda taga mamanta bata tasoba.
    Dady ya ce, "yanzu yayanku yazo mini da wata magana shin gsky ne??, babu ko tsoro atare da ita ta ce, "eh gsky ne, ta ďora da faďin dady kuyi ha'kuri idan ranku ya 6aci.
    Dady ya girgiza kai a'a mu ranmu bai 6aciba, yanzuma banida ikon hanaki abinda kikayi ra'ayi, saidai kafin ki zubar da cikin inason nabaki wani abu ki karanta, daga nan saiki yanke hukuncin dakiga ya dace dake.
   Idan zaki iya cigaba da zama da mahmud bazan hanakiba, hakanma mu zaiyi mana daďi.
   Idan bakida ra'ayin cigaba da zama dashi bazamu tauyekiba, zamubi hanyar daya dace ya sakeki ki auri wanda kikeso,ALLAH yaraya abinda kuka haifa.
   dady yami'ke yashiga ďakinsa.
      Nurr kanta na 'kasa ta kasa kallon mama, shikam ya mahmud aii yashiga ruďani da bayanin dady, har ga ALLAH baiga guguwar dazata taso akan rabashi da Nurr ba komai ruguntsumin dake cikinta kuwa......dawowar dady ta katse masa tunaninsa, ya mi'kawa Nurr book gashi kuje gida ki karanta, ina jiranku gobe idan ALKAH ya kaimu da safe.
      Kutashi ku tafi, mi'kewa sukayi ya mahmud yami'kama mama waleeda datayi barci suka fice sai gida..................

tofa masu karatu, kunji kuma wani SABON AL'AMAREE.
    Koya zata kasance???, kubiyo mata agidan Abdul kawai










Luv u oll my fan's.
©2017
Share:

0 comments:

Post a Comment

Recent

Contact Form

Name

Email *

Message *